Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 31

وَمَآءٖ مَّسۡكُوبٖ

Da kuma ruwa mai kwarara



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 32

وَفَٰكِهَةٖ كَثِيرَةٖ

Da ababen marmari masu yawa



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 33

لَّا مَقۡطُوعَةٖ وَلَا مَمۡنُوعَةٖ

Ba masu yankewa ba kuma ba ababen hanawa ba



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 34

وَفُرُشٖ مَّرۡفُوعَةٍ

Da shimfixu masu daraja



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 35

إِنَّآ أَنشَأۡنَٰهُنَّ إِنشَآءٗ

Lalle Mu ne Muka qage su (‘yan matan Aljanna) sabuwar qagowa



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 36

فَجَعَلۡنَٰهُنَّ أَبۡكَارًا

Sannan Muka sanya su budurwai



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 37

عُرُبًا أَتۡرَابٗا

Masu begen mazajensu, tsarekun juna



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 38

لِّأَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

Don ma’abota hannun dama



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 39

ثُلَّةٞ مِّنَ ٱلۡأَوَّلِينَ

Su jama’a ne (masu yawa) daga (al’ummun) farko



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 40

وَثُلَّةٞ مِّنَ ٱلۡأٓخِرِينَ

Kuma jama’a ne (masu yawa) daga (al’ummar) qarshe



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 41

وَأَصۡحَٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلشِّمَالِ

Ma’abota hannun hagu kuma, mamakin qasqancin ma’abota hannun hagu!



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 42

فِي سَمُومٖ وَحَمِيمٖ

Suna cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 43

وَظِلّٖ مِّن يَحۡمُومٖ

Da kuma inuwa ta turnuqun hayaqi



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 44

لَّا بَارِدٖ وَلَا كَرِيمٍ

Ba mai sanyi ba, kuma ba mai daraja ba



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 45

إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُتۡرَفِينَ

Lalle su sun kasance masu holewa ne kafin wannan



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 46

وَكَانُواْ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلۡحِنثِ ٱلۡعَظِيمِ

Sun kuma kasance suna dogewa a kan zunubi mai girma.[1]


1- Watau babban laifi na kafirci da bautar wanin Allah.


Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 47

وَكَانُواْ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبۡعُوثُونَ

Sun kuma kasance suna cewa: “Yanzu idan mun mutu, mun zama qasa da qasusuwa, yanzu lalle za a tashe mu?



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 48

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلۡأَوَّلُونَ

“Hakanan ma iyayenmu na farko?”



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 49

قُلۡ إِنَّ ٱلۡأَوَّلِينَ وَٱلۡأٓخِرِينَ

Ka ce: “Lalle na farkon da na qarshen



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 50

لَمَجۡمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

“Tabbas za a tattara su zuwa wani lokaci na rana sananniya



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 51

ثُمَّ إِنَّكُمۡ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلۡمُكَذِّبُونَ

“Sannan lalle ku kuma waxannan vatattu masu qaryatawa



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 52

لَأٓكِلُونَ مِن شَجَرٖ مِّن زَقُّومٖ

“Tabbas za ku ci daga bishiyar Zaqqumu[1]


1- Watau wata bishiya ce mafi muni da sharri a wutar jahannama.


Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 53

فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

“Sannan za ku cika cikunanku da ita



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 54

فَشَٰرِبُونَ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡحَمِيمِ

“Sannan za ku sha tafasasshen ruwa a kanta



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 55

فَشَٰرِبُونَ شُرۡبَ ٱلۡهِيمِ

“Sannan za ku sha irin shan raquma masu jin qishirwa.”



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 56

هَٰذَا نُزُلُهُمۡ يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Wannan ita ce gararsu a ranar sakamako



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 57

نَحۡنُ خَلَقۡنَٰكُمۡ فَلَوۡلَا تُصَدِّقُونَ

Mu ne Muka halicce ku, me ya sa ba kwa gaskatawa?



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 58

أَفَرَءَيۡتُم مَّا تُمۡنُونَ

Ba kwa ganin maniyyi da kuke zubawa



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 59

ءَأَنتُمۡ تَخۡلُقُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡخَٰلِقُونَ

Shin ku ne kuke halittar sa, ko kuwa Mu ne Masu halittar?



Sure: Suratul Waqi’a

Vers : 60

نَحۡنُ قَدَّرۡنَا بَيۡنَكُمُ ٱلۡمَوۡتَ وَمَا نَحۡنُ بِمَسۡبُوقِينَ

Mu ne Muke qaddara mutuwa a tsakaninku, kuma Mu ba Masu gajiyawa ba ne