Sure: Suratul Furqan

Vers : 31

وَكَذَٰلِكَ جَعَلۡنَا لِكُلِّ نَبِيٍّ عَدُوّٗا مِّنَ ٱلۡمُجۡرِمِينَۗ وَكَفَىٰ بِرَبِّكَ هَادِيٗا وَنَصِيرٗا

Kamar haka Muka sanya wa kowanne annabi abokan gaba daga masu laifi, kuma Ubangijinka Ya ishe ka Mai shiryarwa Mai taimako



Sure: Suratul Furqan

Vers : 32

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَوۡلَا نُزِّلَ عَلَيۡهِ ٱلۡقُرۡءَانُ جُمۡلَةٗ وَٰحِدَةٗۚ كَذَٰلِكَ لِنُثَبِّتَ بِهِۦ فُؤَادَكَۖ وَرَتَّلۡنَٰهُ تَرۡتِيلٗا

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Me ya hana a saukar masa da Alqur’ani gaba xaya, a lokaci guda[1]?” Kamar haka ne (Muke saukar da shi kaxan-kaxan) don Mu tabbatar da zuciyarka da shi, Muka kuma karantar (da kai) shi daki-daki


1- Watau kamar yadda aka saukar da littafin Attaura ko Linjila.


Sure: Suratul Furqan

Vers : 33

وَلَا يَأۡتُونَكَ بِمَثَلٍ إِلَّا جِئۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ وَأَحۡسَنَ تَفۡسِيرًا

Kuma ba za su zo maka da wani misali ba (na qalu-bale) sai Mun zo maka da gaskiya, kuma da mafi kyan bayani



Sure: Suratul Furqan

Vers : 34

ٱلَّذِينَ يُحۡشَرُونَ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ إِلَىٰ جَهَنَّمَ أُوْلَـٰٓئِكَ شَرّٞ مَّكَانٗا وَأَضَلُّ سَبِيلٗا

Waxanda za a tashe su zuwa wutar Jahannama a kan fuskokinsu, waxannan su suka fi mummunan matsayi kuma mafiya vatacciyar hanya



Sure: Suratul Furqan

Vers : 35

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَجَعَلۡنَا مَعَهُۥٓ أَخَاهُ هَٰرُونَ وَزِيرٗا

Haqiqa kuma Mun bai wa Musa Littafi muka kuma sanya xan’uwansa Haruna tare da shi a matsayin Waziri



Sure: Suratul Furqan

Vers : 36

فَقُلۡنَا ٱذۡهَبَآ إِلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا فَدَمَّرۡنَٰهُمۡ تَدۡمِيرٗا

Sai Muka ce: “Ku tafi zuwa ga mutanen da suka qaryata ayoyinmu, sai Muka hallaka su hallakarwa mai tsanani!”



Sure: Suratul Furqan

Vers : 37

وَقَوۡمَ نُوحٖ لَّمَّا كَذَّبُواْ ٱلرُّسُلَ أَغۡرَقۡنَٰهُمۡ وَجَعَلۡنَٰهُمۡ لِلنَّاسِ ءَايَةٗۖ وَأَعۡتَدۡنَا لِلظَّـٰلِمِينَ عَذَابًا أَلِيمٗا

Mutanen Nuhu kuma lokacin da suka qaryata manzanni[1] sai Muka nutsar da su, Muka kuma sanya su wa’azi ga mutane, kuma Muka tanadi azaba mai raxaxi ga azzalumai


1- Watau ta hanyar qaryata Annabi Nuhu(), domin saqon duk manzanni guda xaya ne, shi ne kaxaita Allah da bauta.


Sure: Suratul Furqan

Vers : 38

وَعَادٗا وَثَمُودَاْ وَأَصۡحَٰبَ ٱلرَّسِّ وَقُرُونَۢا بَيۡنَ ذَٰلِكَ كَثِيرٗا

Kuma (Muka hallakar da) Adawa da Samudawa da kuma mutanen (rijiyar) Rassu, da kuma wasu al’ummu masu yawa tsakanin hakan



Sure: Suratul Furqan

Vers : 39

وَكُلّٗا ضَرَبۡنَا لَهُ ٱلۡأَمۡثَٰلَۖ وَكُلّٗا تَبَّرۡنَا تَتۡبِيرٗا

Kowannensu kuwa Mun ba shi misalai; kuma kowannensu Mun hallaka shi mummunar hallakawa



Sure: Suratul Furqan

Vers : 40

وَلَقَدۡ أَتَوۡاْ عَلَى ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلَّتِيٓ أُمۡطِرَتۡ مَطَرَ ٱلسَّوۡءِۚ أَفَلَمۡ يَكُونُواْ يَرَوۡنَهَاۚ بَلۡ كَانُواْ لَا يَرۡجُونَ نُشُورٗا

Haqiqa kuma (su mutanen Makka) sun bi ta alqaryar nan wadda aka yi wa ruwan azaba. Shin ba su kasance suna ganin ta ba ne? Ba haka ba ne, sun dai kasance ne ba sa tsammanin tashin alqiyama



Sure: Suratul Furqan

Vers : 41

وَإِذَا رَأَوۡكَ إِن يَتَّخِذُونَكَ إِلَّا هُزُوًا أَهَٰذَا ٱلَّذِي بَعَثَ ٱللَّهُ رَسُولًا

Idan kuma suka gan ka ba sa riqon ka sai abin yi wa izgili, (suna cewa): “Yanzu wannan ne wanda Allah ya aiko Manzo?



Sure: Suratul Furqan

Vers : 42

إِن كَادَ لَيُضِلُّنَا عَنۡ ءَالِهَتِنَا لَوۡلَآ أَن صَبَرۡنَا عَلَيۡهَاۚ وَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ حِينَ يَرَوۡنَ ٱلۡعَذَابَ مَنۡ أَضَلُّ سَبِيلًا

“Lalle saura qiris ya vatar da mu daga ababen bautarmu, ba don mun yi haquri a kansu ba.” Ba da daxewa ba kuwa za su san wanda ya fi vatan hanya yayin da za su ga azaba



Sure: Suratul Furqan

Vers : 43

أَرَءَيۡتَ مَنِ ٱتَّخَذَ إِلَٰهَهُۥ هَوَىٰهُ أَفَأَنتَ تَكُونُ عَلَيۡهِ وَكِيلًا

Shin ka ga wanda ya mayar da son zuciyarsa (shi ne) abin bautarsa, to yanzu kai za ka zama mai kiyaye shi (daga bin son zuciyarsa)?



Sure: Suratul Furqan

Vers : 44

أَمۡ تَحۡسَبُ أَنَّ أَكۡثَرَهُمۡ يَسۡمَعُونَ أَوۡ يَعۡقِلُونَۚ إِنۡ هُمۡ إِلَّا كَٱلۡأَنۡعَٰمِ بَلۡ هُمۡ أَضَلُّ سَبِيلًا

Ko kuwa kana tsammanin cewa yawancinsu suna ji ne (na fahimta) ko suna hankalta? Ai su ba wasu ba ne illa kamar dabbobi; a’a su ne ma suka fi (dabbobi) vace hanya



Sure: Suratul Furqan

Vers : 45

أَلَمۡ تَرَ إِلَىٰ رَبِّكَ كَيۡفَ مَدَّ ٱلظِّلَّ وَلَوۡ شَآءَ لَجَعَلَهُۥ سَاكِنٗا ثُمَّ جَعَلۡنَا ٱلشَّمۡسَ عَلَيۡهِ دَلِيلٗا

Shin ba ka ganin (irin aikin) Ubangijinka yadda ya shimfixa inuwa, da kuwa ya ga dama da sai ya sanya ta a tsaye cak, sannan Muka sanya rana dalilin samuwarta (inuwar)



Sure: Suratul Furqan

Vers : 46

ثُمَّ قَبَضۡنَٰهُ إِلَيۡنَا قَبۡضٗا يَسِيرٗا

Sannan Muka riqa janye ta da kaxan-kaxan[1]


1- Watau tana raguwa gwargwadon xagawar rana, har ya zamanto ta gushe gaba xaya.


Sure: Suratul Furqan

Vers : 47

وَهُوَ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلَّيۡلَ لِبَاسٗا وَٱلنَّوۡمَ سُبَاتٗا وَجَعَلَ ٱلنَّهَارَ نُشُورٗا

Kuma shi ne wanda ya sanya muku dare ya zama sutura, bacci kuma don hutawa kuma ya sanya rana don watsuwa (wajen neman abinci)



Sure: Suratul Furqan

Vers : 48

وَهُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ ٱلرِّيَٰحَ بُشۡرَۢا بَيۡنَ يَدَيۡ رَحۡمَتِهِۦۚ وَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ طَهُورٗا

Kuma shi ne wanda ya aiko iska don albishir a gabanin (saukar) rahamarsa. Muka kuma saukar da ruwa mai tsarkakewa daga sama



Sure: Suratul Furqan

Vers : 49

لِّنُحۡـِۧيَ بِهِۦ بَلۡدَةٗ مَّيۡتٗا وَنُسۡقِيَهُۥ مِمَّا خَلَقۡنَآ أَنۡعَٰمٗا وَأَنَاسِيَّ كَثِيرٗا

Don Mu raya busasshiyar qasa da shi, kuma Mu shayar da dabbobi da mutane masu yawa daga abubuwan da Muka halitta



Sure: Suratul Furqan

Vers : 50

وَلَقَدۡ صَرَّفۡنَٰهُ بَيۡنَهُمۡ لِيَذَّكَّرُواْ فَأَبَىٰٓ أَكۡثَرُ ٱلنَّاسِ إِلَّا كُفُورٗا

Haqiqa kuma Mun sarrafa shi a tsakaninsu don su wa’azantu[1], sai mafi yawan mutane suka qi (wa’azantuwa) sai kafirci


1- Watau Allah () ya sarrafa hujjoji da dalilai daban-daban a cikin Alqur’ani domin mutane su wa’azantu.


Sure: Suratul Furqan

Vers : 51

وَلَوۡ شِئۡنَا لَبَعَثۡنَا فِي كُلِّ قَرۡيَةٖ نَّذِيرٗا

Da kuma Mun ga dama, lalle da mun aiko wani mai gargaxi cikin kowacce alqarya[1]


1- Amma bai yi haka ba, sai ya aiko Annabi Muhammadu () shi kaxai zuwa ga talikai baki xaya.


Sure: Suratul Furqan

Vers : 52

فَلَا تُطِعِ ٱلۡكَٰفِرِينَ وَجَٰهِدۡهُم بِهِۦ جِهَادٗا كَبِيرٗا

To kada ka bi son ran kafirai kuma ka yaqe su da shi (Alqur’ani) yaqi mai girma



Sure: Suratul Furqan

Vers : 53

۞وَهُوَ ٱلَّذِي مَرَجَ ٱلۡبَحۡرَيۡنِ هَٰذَا عَذۡبٞ فُرَاتٞ وَهَٰذَا مِلۡحٌ أُجَاجٞ وَجَعَلَ بَيۡنَهُمَا بَرۡزَخٗا وَحِجۡرٗا مَّحۡجُورٗا

Shi ne kuma wanda Ya haxa koguna biyu: wannan mai tsananin daxi wannan kuma mai tsananin zartsi, Ya kuma sanya shamaki a tsakaninsu da kuma kariya mai karewa



Sure: Suratul Furqan

Vers : 54

وَهُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ مِنَ ٱلۡمَآءِ بَشَرٗا فَجَعَلَهُۥ نَسَبٗا وَصِهۡرٗاۗ وَكَانَ رَبُّكَ قَدِيرٗا

Shi ne kuma wanda Ya halicci mutum daga ruwa sannan Ya mayar da shi dangantaka da surukuta. Ubangijinka Ya kasance Mai iko ne



Sure: Suratul Furqan

Vers : 55

وَيَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَا يَنفَعُهُمۡ وَلَا يَضُرُّهُمۡۗ وَكَانَ ٱلۡكَافِرُ عَلَىٰ رَبِّهِۦ ظَهِيرٗا

Kuma suna bauta wa wanin Allah abin da ba zai amfane su ba kuma ba zai cuce su ba. Kafiri kuwa ya kasance mai taimaka wa (Shaixan ne) a kan bijire wa Ubangijinsa



Sure: Suratul Furqan

Vers : 56

وَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ إِلَّا مُبَشِّرٗا وَنَذِيرٗا

Kuma ba Mu aiko ka ba sai kawai don ka zama mai albishir mai gargaxi



Sure: Suratul Furqan

Vers : 57

قُلۡ مَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍ إِلَّا مَن شَآءَ أَن يَتَّخِذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ سَبِيلٗا

Ka ce (da su): “Ba na tambayar ku wani lada a kansa (gargaxin), sai dai ya rage ga wanda ya ga dama ya riqi hanya (ta gari) zuwa ga Ubangijinsa.”



Sure: Suratul Furqan

Vers : 58

وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱلۡحَيِّ ٱلَّذِي لَا يَمُوتُ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِهِۦۚ وَكَفَىٰ بِهِۦ بِذُنُوبِ عِبَادِهِۦ خَبِيرًا

Kuma ka dogara ga (Allah) Rayayye Wanda ba zai mutu ba, kuma ka yi tasbihi da godiyar sa, kuma Ya isa Masani ga zunuban bayinsa



Sure: Suratul Furqan

Vers : 59

ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ ٱلرَّحۡمَٰنُ فَسۡـَٔلۡ بِهِۦ خَبِيرٗا

(Shi ne) wanda Ya halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, sannan Ya daidaita a kan Al’arshi. (Shi ne) Arrahmanu, sai ka tambayi Masani game da Shi



Sure: Suratul Furqan

Vers : 60

وَإِذَا قِيلَ لَهُمُ ٱسۡجُدُواْۤ لِلرَّحۡمَٰنِ قَالُواْ وَمَا ٱلرَّحۡمَٰنُ أَنَسۡجُدُ لِمَا تَأۡمُرُنَا وَزَادَهُمۡ نُفُورٗا۩

Idan kuwa aka ce da su: “Ku yi sujjada ga Arrahmanu” sai su ce: “Mene ne Arrahmanu[1]? Yanzu ma yi sujjada ga abin da kake umartar mu?” (Wannan umarnin) kuma ya qara musu fanxarewa


1- Watau kafirai ba su yarda da sunan Allah Arrahmanu ba, kamar yadda ya zo a cikin Suratur Ra’ad, aya ta 30.