Sure: Suratul Qalam

Vers : 1

نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ

NUN[1]. (Allah ya ce): Na rantse da alqalami da abin da (mala’iku) suke rubutawa


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Sure: Suratul Qalam

Vers : 2

مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ

Kai ba mahaukaci ba ne saboda ni’imar Ubangijinka



Sure: Suratul Qalam

Vers : 3

وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ

Kuma lalle tabbas kana da lada marar yankewa



Sure: Suratul Qalam

Vers : 4

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ

Lalle kuma kai kana kan halaye masu girma



Sure: Suratul Qalam

Vers : 5

فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ

To ba da daxewa ba za ka gani, su ma kuma su gani



Sure: Suratul Qalam

Vers : 6

بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ

Wane ne daga cikinku mahaukaci?



Sure: Suratul Qalam

Vers : 7

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle Ubangijinka Shi Ya fi sanin wanda ya kauce wa hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin shiryayyu



Sure: Suratul Qalam

Vers : 8

فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Saboda haka kada ka bi masu qaryatawa



Sure: Suratul Qalam

Vers : 9

وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ

Sun yi burin da za ka sassauto, sai su ma su sassauto[1]


1- Watau ya daina aibata gumakansu da bautarsu, sai su ma su daina sukan sa da addininsa.


Sure: Suratul Qalam

Vers : 10

وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ

Kada kuma ka bi duk wani mai yawan rantsuwa, wulaqantacce



Sure: Suratul Qalam

Vers : 11

هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ

Mai yawan yin zunxe, mai yawan yawo da annamimanci



Sure: Suratul Qalam

Vers : 12

مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ

Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai yawan savo



Sure: Suratul Qalam

Vers : 13

عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

Mai busasshiyar zuciya, bayan wannan kuma marar asali ne



Sure: Suratul Qalam

Vers : 14

أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ

Don ya kasance mai dukiya da ‘ya’ya



Sure: Suratul Qalam

Vers : 15

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne.”



Sure: Suratul Qalam

Vers : 16

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ

Ba da daxewa ba za Mu yi masa alama a kan hancinsa



Sure: Suratul Qalam

Vers : 17

إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ

Lalle Mu Mun jarrabe su (wato mutanen Makka) kamar yadda Muka jarrabi ma’abota gona, lokacin da suka rantse cewa, lalle tabbas za su girbe ta da asussuba



Sure: Suratul Qalam

Vers : 18

وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ

Ba sa kuma togaciya (da faxar insha Allah)



Sure: Suratul Qalam

Vers : 19

فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ

Sai wani bala’i daga Ubangijinka ya kewaye ta alhali su suna bacci



Sure: Suratul Qalam

Vers : 20

فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ

Sai ta wayi gari (baqi qirin) kamar duhun dare



Sure: Suratul Qalam

Vers : 21

فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ

Sai suka kirawo junansu da asussuba



Sure: Suratul Qalam

Vers : 22

أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ

Cewa: “Ku yi sammako ga amfanin gonarku idan kun kasance masu yin girbi.”



Sure: Suratul Qalam

Vers : 23

فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ

Sai suka tafi alhali suna yi wa junansu raxa



Sure: Suratul Qalam

Vers : 24

أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ

Cewa: “Lalle a yau kada wani miskini ya shigar muku cikinta.”



Sure: Suratul Qalam

Vers : 25

وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ

Suka kuwa yi sammako suna masu zaton su masu iko ne a kan hana (mabuqata)



Sure: Suratul Qalam

Vers : 26

فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ

To lokacin da suka gan ta sai suka ce: “Lalle mu tabbas mun yi vatan kai



Sure: Suratul Qalam

Vers : 27

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne kawai.”



Sure: Suratul Qalam

Vers : 28

قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ

Sai wanda ya fi su kirki ya ce: “Ban gaya muku ya kamata ku tsarkake Allah ba?”



Sure: Suratul Qalam

Vers : 29

قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Suka ce, “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu, lalle mu mun kasance azzalumai.”



Sure: Suratul Qalam

Vers : 30

فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ

Sai sashinsu ya fuskanci sashi suna zargin juna