Sure: Suratu Sad

Vers : 1

صٓۚ وَٱلۡقُرۡءَانِ ذِي ٱلذِّكۡرِ

SAD[1]. “Na rantse da Alqur’ani ma’abocin xaukaka


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


Sure: Suratu Sad

Vers : 2

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي عِزَّةٖ وَشِقَاقٖ

Sai dai waxanda suka kafirta suna cikin girman kai ne da jayayya



Sure: Suratu Sad

Vers : 3

كَمۡ أَهۡلَكۡنَا مِن قَبۡلِهِم مِّن قَرۡنٖ فَنَادَواْ وَّلَاتَ حِينَ مَنَاصٖ

Al’ummu nawa Muka hallaka gabaninsu, sai suka yi ta kururuwar neman agaji, alhali kuwa lokacin ba na neman tsira ba ne



Sure: Suratu Sad

Vers : 4

وَعَجِبُوٓاْ أَن جَآءَهُم مُّنذِرٞ مِّنۡهُمۡۖ وَقَالَ ٱلۡكَٰفِرُونَ هَٰذَا سَٰحِرٞ كَذَّابٌ

Suka kuma yi mamaki don mai gargaxi ya zo musu daga cikinsu; kuma kafirai suka ce: “Wannan mai sihiri ne babban maqaryaci



Sure: Suratu Sad

Vers : 5

أَجَعَلَ ٱلۡأٓلِهَةَ إِلَٰهٗا وَٰحِدًاۖ إِنَّ هَٰذَا لَشَيۡءٌ عُجَابٞ

“Yanzu yaya zai mayar da alloli Allah guda xaya? Lalle wannan abu ne mai ban mamaki.”



Sure: Suratu Sad

Vers : 6

وَٱنطَلَقَ ٱلۡمَلَأُ مِنۡهُمۡ أَنِ ٱمۡشُواْ وَٱصۡبِرُواْ عَلَىٰٓ ءَالِهَتِكُمۡۖ إِنَّ هَٰذَا لَشَيۡءٞ يُرَادُ

Manyansu kuma suka tafi (suna cewa): “Ku yi tafiyarku, kuma ku yi haquri a kan (bautar) allolinku; lalle wannan wani shiryayyen abu ne ake nufi



Sure: Suratu Sad

Vers : 7

مَا سَمِعۡنَا بِهَٰذَا فِي ٱلۡمِلَّةِ ٱلۡأٓخِرَةِ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا ٱخۡتِلَٰقٌ

“Ba mu tava jin irin wannan ba a addinin da ya wuce[1], wannan ba komai ba ne sai qage


1- Watau addinin Annabi Isa ().


Sure: Suratu Sad

Vers : 8

أَءُنزِلَ عَلَيۡهِ ٱلذِّكۡرُ مِنۢ بَيۡنِنَاۚ بَلۡ هُمۡ فِي شَكّٖ مِّن ذِكۡرِيۚ بَل لَّمَّا يَذُوقُواْ عَذَابِ

“Yanzu a saukar masa da Alqur’ani a tsakaninmu?” Ba haka ba ne, su dai suna kokwanto ne game da tunatarwata; bar su, ai har yanzu ba su xanxani azabata ba ne



Sure: Suratu Sad

Vers : 9

أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَحۡمَةِ رَبِّكَ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡوَهَّابِ

Ko kuwa a wurinsu ne taskokin rahamar Ubangijinka Mabuwayi Mai baiwa suke?



Sure: Suratu Sad

Vers : 10

أَمۡ لَهُم مُّلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَاۖ فَلۡيَرۡتَقُواْ فِي ٱلۡأَسۡبَٰبِ

Ko kuma mulkin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu nasu ne? To sai su kama hanyoyin zuwa sama (domin su aikata abin da suke so)



Sure: Suratu Sad

Vers : 11

جُندٞ مَّا هُنَالِكَ مَهۡزُومٞ مِّنَ ٱلۡأَحۡزَابِ

(Waxannan) wata runduna ce da za a murqushe ta, kamar sauran al’ummun da suka gabata (waxanda suka qaryata manzanninsu)



Sure: Suratu Sad

Vers : 12

كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ وَعَادٞ وَفِرۡعَوۡنُ ذُو ٱلۡأَوۡتَادِ

Mutanen Nuhu sun qaryata kafin su (mutan Makka) da Adawa da Fir’auna mai turaku



Sure: Suratu Sad

Vers : 13

وَثَمُودُ وَقَوۡمُ لُوطٖ وَأَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡأَحۡزَابُ

Da kuma Samudawa da mutanen Luxu da mutanen Sarqaqiya[1]. Waxannan su ne al’ummun


1- Su ne mutanen Annabi Shu’aibu ().


Sure: Suratu Sad

Vers : 14

إِن كُلٌّ إِلَّا كَذَّبَ ٱلرُّسُلَ فَحَقَّ عِقَابِ

Babu xaya daga cikinsu wanda bai qaryata manzanni ba, sai uqubata ta wajaba (a kansu)



Sure: Suratu Sad

Vers : 15

وَمَا يَنظُرُ هَـٰٓؤُلَآءِ إِلَّا صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ مَّا لَهَا مِن فَوَاقٖ

Kuma ba abin da waxannan suke sauraro sai busa guda xaya wadda ba ta da makawa



Sure: Suratu Sad

Vers : 16

وَقَالُواْ رَبَّنَا عَجِّل لَّنَا قِطَّنَا قَبۡلَ يَوۡمِ ٱلۡحِسَابِ

Suka kuma ce: “Ya Ubangijinmu, Ka gaggauto mana rabonmu (na azaba) tun kafin ranar hisabi!”



Sure: Suratu Sad

Vers : 17

ٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَٱذۡكُرۡ عَبۡدَنَا دَاوُۥدَ ذَا ٱلۡأَيۡدِۖ إِنَّهُۥٓ أَوَّابٌ

(Sai Allah Ya ce): “Ka yi haquri a kan abin da suke faxa, ka kuma tuna bawanmu Dawuda ma’abocin qarfi; lalle shi ya kasance mai yawan komawa ne (ga Allah)



Sure: Suratu Sad

Vers : 18

إِنَّا سَخَّرۡنَا ٱلۡجِبَالَ مَعَهُۥ يُسَبِّحۡنَ بِٱلۡعَشِيِّ وَٱلۡإِشۡرَاقِ

Lalle Mu Mun hore masa duwatsu suna yin tasbihi tare da shi a yamma da hantsi



Sure: Suratu Sad

Vers : 19

وَٱلطَّيۡرَ مَحۡشُورَةٗۖ كُلّٞ لَّهُۥٓ أَوَّابٞ

Da kuma tsuntsaye a tattare; dukkaninsu suna biyayya a gare shi



Sure: Suratu Sad

Vers : 20

وَشَدَدۡنَا مُلۡكَهُۥ وَءَاتَيۡنَٰهُ ٱلۡحِكۡمَةَ وَفَصۡلَ ٱلۡخِطَابِ

Kuma Muka qarfafa mulkinsa, Muka kuma ba shi hikima da bayyana hukunce-hukunce (tsakanin masu husuma)



Sure: Suratu Sad

Vers : 21

۞وَهَلۡ أَتَىٰكَ نَبَؤُاْ ٱلۡخَصۡمِ إِذۡ تَسَوَّرُواْ ٱلۡمِحۡرَابَ

Shin labarin abokan husuma ya zo maka, yayin da suka haura wurin ibada?



Sure: Suratu Sad

Vers : 22

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَىٰ دَاوُۥدَ فَفَزِعَ مِنۡهُمۡۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ خَصۡمَانِ بَغَىٰ بَعۡضُنَا عَلَىٰ بَعۡضٖ فَٱحۡكُم بَيۡنَنَا بِٱلۡحَقِّ وَلَا تُشۡطِطۡ وَٱهۡدِنَآ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلصِّرَٰطِ

Yayin da suka shiga wurin Dawuda sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata, (mu biyun nan) masu husuma ne, xayanmu ya zalunci xaya, sai ka yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya, kada kuma ka yi zalunci, kuma ka shiryar da mu hanya madaidaiciya



Sure: Suratu Sad

Vers : 23

إِنَّ هَٰذَآ أَخِي لَهُۥ تِسۡعٞ وَتِسۡعُونَ نَعۡجَةٗ وَلِيَ نَعۡجَةٞ وَٰحِدَةٞ فَقَالَ أَكۡفِلۡنِيهَا وَعَزَّنِي فِي ٱلۡخِطَابِ

“Lalle wannan xan’uwana ne yana da awaki guda casa’in da tara, ni kuma ina da akuya guda xaya, sai ya ce: ‘Ka ba ni ita;’ ya kuma rinjaye ni game da maganar.”



Sure: Suratu Sad

Vers : 24

قَالَ لَقَدۡ ظَلَمَكَ بِسُؤَالِ نَعۡجَتِكَ إِلَىٰ نِعَاجِهِۦۖ وَإِنَّ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلۡخُلَطَآءِ لَيَبۡغِي بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٍ إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَقَلِيلٞ مَّا هُمۡۗ وَظَنَّ دَاوُۥدُ أَنَّمَا فَتَنَّـٰهُ فَٱسۡتَغۡفَرَ رَبَّهُۥ وَخَرَّۤ رَاكِعٗاۤ وَأَنَابَ۩

(Dawuda) Ya ce: “Haqiqa ya zalunce ka saboda neman haxe akuyarka cikin awakinsa; kuma lalle yawancin masu haxa dukiyarsu tabbas wasunsu suna zaluntar wasu, sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, su kuwa kaxan ne qwarai. Sai kuma Dawuda ya tabbata cewa Mun jarraba shi ne, sai ya nemi gafarar Ubangijinsa, ya kuma faxi yana sujjada kuma ya koma (ga Allah)



Sure: Suratu Sad

Vers : 25

فَغَفَرۡنَا لَهُۥ ذَٰلِكَۖ وَإِنَّ لَهُۥ عِندَنَا لَزُلۡفَىٰ وَحُسۡنَ مَـَٔابٖ

Sai Muka gafarta masa wannan; lalle kuma yana da kusanci da Mu da kuma kyakkyawar makoma



Sure: Suratu Sad

Vers : 26

يَٰدَاوُۥدُ إِنَّا جَعَلۡنَٰكَ خَلِيفَةٗ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَٱحۡكُم بَيۡنَ ٱلنَّاسِ بِٱلۡحَقِّ وَلَا تَتَّبِعِ ٱلۡهَوَىٰ فَيُضِلَّكَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ يَضِلُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ لَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدُۢ بِمَا نَسُواْ يَوۡمَ ٱلۡحِسَابِ

Ya Dawuda, lalle Mun sanya ka halifa a bayan qasa, sai ka yi hukunci a tsakanin mutane da gaskiya, kada ka bi son zuciya sai ya vatar da kai daga hanyar Allah. Lalle waxanda suke vacewa daga hanyar Allah suna da (sakamakon) azaba mai tsanani saboda mantawar da suka yi da ranar hisabi



Sure: Suratu Sad

Vers : 27

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَآءَ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا بَٰطِلٗاۚ ذَٰلِكَ ظَنُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۚ فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنَ ٱلنَّارِ

Kuma ba Mu halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu a banza ba. Wannan zato ne na waxanda suka kafirta. Saboda haka tsananin azabar wuta ya tabbata ga waxanda suka kafirce



Sure: Suratu Sad

Vers : 28

أَمۡ نَجۡعَلُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ كَٱلۡمُفۡسِدِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِ أَمۡ نَجۡعَلُ ٱلۡمُتَّقِينَ كَٱلۡفُجَّارِ

Shin za Mu mayar da waxanda suka yi imani suka yi ayyuka nagari kamar masu varna a bayan qasa, ko kuma za Mu mayar da masu taqawa kamar lalatattu?



Sure: Suratu Sad

Vers : 29

كِتَٰبٌ أَنزَلۡنَٰهُ إِلَيۡكَ مُبَٰرَكٞ لِّيَدَّبَّرُوٓاْ ءَايَٰتِهِۦ وَلِيَتَذَكَّرَ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Littafi ne mai albarka da Muka saukar maka da shi domin su yi tuntuntuni game da ayoyinsa, don kuma masu hankula su wa’azantu



Sure: Suratu Sad

Vers : 30

وَوَهَبۡنَا لِدَاوُۥدَ سُلَيۡمَٰنَۚ نِعۡمَ ٱلۡعَبۡدُ إِنَّهُۥٓ أَوَّابٌ

Muka kuma yi wa Dawuda baiwar (xa) Sulaimanu. Madalla da wannan bawan; lalle shi mai yawan komawa ne (ga Allah)