-
Sure :
Suratus Shu’ara
-
Teil:
19
-
Verszahl :
227
-
Versnummer :
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 1
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 2
تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
Waxannan ayoyi ne na Littafi mabayyani
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 3
لَعَلَّكَ بَٰخِعٞ نَّفۡسَكَ أَلَّا يَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
Ko za ka kashe kanka ne don ba su zama muminai ba?
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 4
إِن نَّشَأۡ نُنَزِّلۡ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةٗ فَظَلَّتۡ أَعۡنَٰقُهُمۡ لَهَا خَٰضِعِينَ
Da Mun ga dama da sai Mu saukar musu da aya daga sama sai wuyoyinsu su zamo masu qanqan da kai gare ta[1]
1- Watau mu’ujizar da za ta tilasta musu su miqa wuya ko ba sa so.
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 5
وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن ذِكۡرٖ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ مُحۡدَثٍ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهُ مُعۡرِضِينَ
Kuma ba wani wa’azi sabo da zai zo musu daga (Allah) Mai rahama sai sun kasance masu bijire masa
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 6
فَقَدۡ كَذَّبُواْ فَسَيَأۡتِيهِمۡ أَنۢبَـٰٓؤُاْ مَا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ
To haqiqa sun qaryata, ba da daxewa ba labaran aqibar abin da suke yi wa izgili za su zo musu
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 7
أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَمۡ أَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ
Shin ba su yi duba zuwa ga qasa ba, (su ga) dangogin tsirrai masu kyau nawa ne Muka tsirar daga cikinta?
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 8
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle a game da wannan tabbas akwai aya (mai nuna cikar ikon Allah); kuma yawancinsu ba su zamanto masu imani ba
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 9
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi Mabuwayi ne, Mai rahama
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 10
وَإِذۡ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئۡتِ ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Kuma (ka tuna) lokacin da Ubangijinka Ya kira Musa cewa: “Ka tafi wajen mutanen nan azzalumai
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 11
قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَۚ أَلَا يَتَّقُونَ
“(Watau) mutanen Fir’auna. Yanzu ba za su kiyaye dokokin Allah ba?”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 12
قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
(Musa) ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni ina tsoron su qaryata ni
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 13
وَيَضِيقُ صَدۡرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرۡسِلۡ إِلَىٰ هَٰرُونَ
“Kuma qirjina yana quntata, kuma harshena ba ya sakuwa, sai Ka aika zuwa ga (xan’uwana) Haruna
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 14
وَلَهُمۡ عَلَيَّ ذَنۢبٞ فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ
“Ni kuma akwai wani laifi da na yi musu, sai nake tsoron su kashe ni.”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 15
قَالَ كَلَّاۖ فَٱذۡهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسۡتَمِعُونَ
(Allah) Ya ce: “A’a; (ba abin da zai same ka), sai ku tafi (kai da xan’uwanka) da ayoyinmu; lalle Mu masu jin (komai da zai faru) ne tare da ku
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 16
فَأۡتِيَا فِرۡعَوۡنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
“Ku je wajen Fir’auna sai ku faxa masa cewa: ‘Lalle mu manzannin Ubangijin talikai ne
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 17
أَنۡ أَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
“‘Cewa, ka sako mana da Banu-Isra’ila’.”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 18
قَالَ أَلَمۡ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدٗا وَلَبِثۡتَ فِينَا مِنۡ عُمُرِكَ سِنِينَ
(Fir’auna) ya ce: “Yanzu ba mu muka raine ka a cikinmu tun kana jariri ba, kuma ka zauna ka yi wasu shekaru na rayuwarka a cikinmu?
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 19
وَفَعَلۡتَ فَعۡلَتَكَ ٱلَّتِي فَعَلۡتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
“Ka kuma aikata aika-aikarka da ka aikata[1] alhali kuwa kana daga masu butulce wa (ni’imata)?”
1- Yana nufin kashe Baqibxe da ya yi lokacin da ya same shi yana faxa da Ba’isra’ile. Duba Suratul Qasas, ayat ta 15.
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 20
قَالَ فَعَلۡتُهَآ إِذٗا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
(Musa) ya ce: “Na aikata haka ne a lokacin ina cikin marasa shiriya (ta rashin wahayi)
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 21
فَفَرَرۡتُ مِنكُمۡ لَمَّا خِفۡتُكُمۡ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكۡمٗا وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
“Sannan na guje muku lokacin da na tsorata da ku, sai Ubangijina Ya ba ni kyautar ilimi Ya kuma sanya ni daga manzanni
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 22
وَتِلۡكَ نِعۡمَةٞ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنۡ عَبَّدتَّ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ
“Waccen ni’imar kuwa da kake goranta min ita saboda ka bautar da Bani-Isra’ila ne.”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 23
قَالَ فِرۡعَوۡنُ وَمَا رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Fir’auna ya ce: “To wane ne Ubangijin talikai?”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 24
قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
(Musa) ya ce: “(Shi ne) Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu, idan har kun kasance masu sakankancewa (da hakan)”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 25
قَالَ لِمَنۡ حَوۡلَهُۥٓ أَلَا تَسۡتَمِعُونَ
(Fir’auna) ya ce da waxanda suke kewaye da shi: “Shin ba kwa jin (abin da yake faxa)?”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 26
قَالَ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
(Musa) ya ce: “Shi ne Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko!”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 27
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِيٓ أُرۡسِلَ إِلَيۡكُمۡ لَمَجۡنُونٞ
(Fir’auna) ya ce: “Lalle Manzon da aka aiko muku tabbas mai tavin hankali ne!”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 28
قَالَ رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ
(Musa) ya ce: “(Shi ne) Ubangijin mahudar rana da mafaxarta da kuma abin da yake tsakaninsu; in kun zamanto masu hankalta.”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 29
قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذۡتَ إِلَٰهًا غَيۡرِي لَأَجۡعَلَنَّكَ مِنَ ٱلۡمَسۡجُونِينَ
(Fir’auna) ya ce: “Na rantse in har ka riqi wani abin bauta ba ni ba, tabbas zan jefa ka cikin ‘yan kurkuku!”
-
-
Fertig
Fehler
-
Sure:
Suratus Shu’ara
Vers : 30
قَالَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكَ بِشَيۡءٖ مُّبِينٖ
(Musa) ya ce: “Ko da na zo maka da wani abu bayyananne?”
-
-
Fertig
Fehler
-