-
Surata :
Suratul Fajr
-
Parte:
30
-
Número de Versículos :
30
-
Número do versículo :
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 1
وَٱلۡفَجۡرِ
Na rantse da alfijir
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 2
وَلَيَالٍ عَشۡرٖ
Da kuma darare goma[1]
1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 3
وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ
Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]
1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.
2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 4
وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ
Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 5
هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ
Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?
1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 6
أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 7
إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ
(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 8
ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 9
وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ
Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 10
وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ
Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 11
ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 12
فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ
Suka kuma yawaita varna a cikinsu
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 13
فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ
Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 14
إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ
Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]
1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 15
فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ
Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 16
وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيۡهِ رِزۡقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَهَٰنَنِ
Amma kuma idan Ya jarrabe shi sai Ya quntata masa a arzikinsa, sai ya ce: “Ubangijina Ya wulaqanta ni.”
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 17
كَلَّاۖ بَل لَّا تُكۡرِمُونَ ٱلۡيَتِيمَ
Faufau, ba haka ba ne; ku ba kwa karrama maraya ne
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 18
وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ
Kuma ba kwa kwaxaitar da juna kan ciyar da miskinai
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 19
وَتَأۡكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكۡلٗا لَّمّٗا
Kuma kuna cinye dukiyar gadon marayu mummunan ci
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 20
وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا
Kuma kuna son dukiya so mai yawa
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 21
كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا
Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 22
وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا
Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu
1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 23
وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ
Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 24
يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي
Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 25
فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ
To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 26
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ
Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 27
يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ
(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 28
ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ
Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 29
فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي
Don haka ka shiga cikin bayina
-
-
Feito
Erro
-
Surata:
Suratul Fajr
O versículo : 30
وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي
Ka kuma shiga Aljannata
-
-
Feito
Erro
-