السورة: Suratur Rahman

الآية : 15

وَخَلَقَ ٱلۡجَآنَّ مِن مَّارِجٖ مِّن نَّارٖ

Ya kuma halicci aljani daga harshen wuta



السورة: Suratur Rahman

الآية : 16

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 17

رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقَيۡنِ وَرَبُّ ٱلۡمَغۡرِبَيۡنِ

Ubangijin mahudar rana biyu da mafaxarta biyu[1]


1- Watau a lokacin sanyi da kuma lokacin zafi.


السورة: Suratur Rahman

الآية : 18

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 19

مَرَجَ ٱلۡبَحۡرَيۡنِ يَلۡتَقِيَانِ

Ya gudanar da koguna guda biyu suna haxuwa (da juna)



السورة: Suratur Rahman

الآية : 20

بَيۡنَهُمَا بَرۡزَخٞ لَّا يَبۡغِيَانِ

A tsakaninsu (kuma) akwai wani shamaki da ya hana su shiga juna



السورة: Suratur Rahman

الآية : 21

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 22

يَخۡرُجُ مِنۡهُمَا ٱللُّؤۡلُؤُ وَٱلۡمَرۡجَانُ

Lu’ulu’u da murjani suna fita daga cikinsu



السورة: Suratur Rahman

الآية : 23

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 24

وَلَهُ ٱلۡجَوَارِ ٱلۡمُنشَـَٔاتُ فِي ٱلۡبَحۡرِ كَٱلۡأَعۡلَٰمِ

Jiragen ruwa kuma da aka yi su suna gudu a cikin kogi kamar manya-manyan duwatsu nasa ne



السورة: Suratur Rahman

الآية : 25

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 26

كُلُّ مَنۡ عَلَيۡهَا فَانٖ

Dukkan wanda yake kanta (qasar) qararre ne



السورة: Suratur Rahman

الآية : 27

وَيَبۡقَىٰ وَجۡهُ رَبِّكَ ذُو ٱلۡجَلَٰلِ وَٱلۡإِكۡرَامِ

Fuskar Ubangijinka kuwa Ma’abocin girma da karamci ne kawai take wanzuwa



السورة: Suratur Rahman

الآية : 28

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 29

يَسۡـَٔلُهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ كُلَّ يَوۡمٍ هُوَ فِي شَأۡنٖ

Duk wanda yake cikin sammai da qasa yana roqon Sa. Kowane lokacin Shi a cikin wani sha’ani yake



السورة: Suratur Rahman

الآية : 30

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 31

سَنَفۡرُغُ لَكُمۡ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ

Ba da daxewa ba za Mu dawo kanku ya ku mutane da aljannu



السورة: Suratur Rahman

الآية : 32

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 33

يَٰمَعۡشَرَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِ إِنِ ٱسۡتَطَعۡتُمۡ أَن تَنفُذُواْ مِنۡ أَقۡطَارِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ فَٱنفُذُواْۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلۡطَٰنٖ

Ya ku jama’ar aljannu da mutane, idan kun sami ikon ficewa daga cikin sassan sammai da qasa to ku fice. Ba za ku fice ba sai da samun wani qarfi[1]


1- Watau ba za su kuvuce wa Allah ba sai idan suna da wata hujja ko wani qarfi, wanda kuma su ma sun tabbata ba su da shi.


السورة: Suratur Rahman

الآية : 34

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 35

يُرۡسَلُ عَلَيۡكُمَا شُوَاظٞ مِّن نَّارٖ وَنُحَاسٞ فَلَا تَنتَصِرَانِ

Za a aiko muku (ku mutane da aljannu) da balbalin wuta da kuma hayaqi, saboda haka ba za ku iya kare kanku (daga gare shi) ba



السورة: Suratur Rahman

الآية : 36

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 37

فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتۡ وَرۡدَةٗ كَٱلدِّهَانِ

Sannan idan sama ta kekkece ta zama jajir kamar jar fata[1]


1- Watau saboda an gusar da hasken taurarin cikinta gaba xaya.


السورة: Suratur Rahman

الآية : 38

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 39

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُسۡـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٞ وَلَا جَآنّٞ

Sannan a wannan rana ba a tambayar mutum ko aljan laifinsa



السورة: Suratur Rahman

الآية : 40

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 41

يُعۡرَفُ ٱلۡمُجۡرِمُونَ بِسِيمَٰهُمۡ فَيُؤۡخَذُ بِٱلنَّوَٰصِي وَٱلۡأَقۡدَامِ

Ana gane manyan masu laifi da alamominsu[1], sai a kama su ta makwarkwaxa da dugadugai


1- Saboda fuskokinsu za su yi baqi qirin, idanuwansu kuma za su yi jawur.


السورة: Suratur Rahman

الآية : 42

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 43

هَٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِي يُكَذِّبُ بِهَا ٱلۡمُجۡرِمُونَ

(Za a ce da su): Wannan ita ce Jahannamar da manyan masu laifi suke qaryatawa



السورة: Suratur Rahman

الآية : 44

يَطُوفُونَ بَيۡنَهَا وَبَيۡنَ حَمِيمٍ ءَانٖ

Za su riqa kai-kawo tsakaninta da tafasasshen ruwa mai tsananin zafi