السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 17

وَمَا تِلۡكَ بِيَمِينِكَ يَٰمُوسَىٰ

“Mene ne kuma wancan yake a hannun damanka ya Musa?”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 18

قَالَ هِيَ عَصَايَ أَتَوَكَّؤُاْ عَلَيۡهَا وَأَهُشُّ بِهَا عَلَىٰ غَنَمِي وَلِيَ فِيهَا مَـَٔارِبُ أُخۡرَىٰ

(Musa) ya ce: “Ai sandata ce da nake jingina a kanta, ina kuma kaxo wa dabbobina ganye da ita, ina kuma da sauran wasu buqatu game da ita.”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 19

قَالَ أَلۡقِهَا يَٰمُوسَىٰ

(Allah) Ya ce: “Jefar da ita ya Musa.”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 20

فَأَلۡقَىٰهَا فَإِذَا هِيَ حَيَّةٞ تَسۡعَىٰ

Sai ya jefar da ita, sai ga ta ta zama macijiya tana ta sauri



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 21

قَالَ خُذۡهَا وَلَا تَخَفۡۖ سَنُعِيدُهَا سِيرَتَهَا ٱلۡأُولَىٰ

Ya ce: “Kama ta, kuma kada ka ji tsoro; za Mu mai da ita kamar yadda take a da



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 22

وَٱضۡمُمۡ يَدَكَ إِلَىٰ جَنَاحِكَ تَخۡرُجۡ بَيۡضَآءَ مِنۡ غَيۡرِ سُوٓءٍ ءَايَةً أُخۡرَىٰ

“Kuma ka haxa hannunka da kwivinka zai fito fari sal ba tare da wata cuta ba; (wannan) wata ayar ce daban



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 23

لِنُرِيَكَ مِنۡ ءَايَٰتِنَا ٱلۡكُبۡرَى

“Domin Mu nuna maka irin manya-manyan ayoyinmu



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 24

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

“Ka tafi wurin Fir’auna don kuwa lalle ya qetare iyaka.”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 25

قَالَ رَبِّ ٱشۡرَحۡ لِي صَدۡرِي

(Musa) ya ce: “Ubangijina Ka buxe mini qirjina[1]


1- Watau ya cire masa in’ina da take damun sa.


السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 26

وَيَسِّرۡ لِيٓ أَمۡرِي

“Kuma Ka sauqaqa mini lamarina



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 27

وَٱحۡلُلۡ عُقۡدَةٗ مِّن لِّسَانِي

“Ka kuma warware qullin da yake a harshena



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 28

يَفۡقَهُواْ قَوۡلِي

“(Don) su fahimci maganata



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 29

وَٱجۡعَل لِّي وَزِيرٗا مِّنۡ أَهۡلِي

“Kuma Ka sanya mini waziri daga dangina



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 30

هَٰرُونَ أَخِي

“(Watau) xau’uwana Haruna



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 31

ٱشۡدُدۡ بِهِۦٓ أَزۡرِي

“Ka qarfafa gwiwata da shi



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 32

وَأَشۡرِكۡهُ فِيٓ أَمۡرِي

“Kuma Ka shigar da shi cikin lamarina[1]


1- Watau shi ma ya ba shi annabta ya aiko su tare.


السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 33

كَيۡ نُسَبِّحَكَ كَثِيرٗا

“Domin mu tsarkake Ka da yawa



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 34

وَنَذۡكُرَكَ كَثِيرًا

“Mu kuma ambace Ka da yawa



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 35

إِنَّكَ كُنتَ بِنَا بَصِيرٗا

“Lalle Kai Ka kasance Kana ganin mu.”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 36

قَالَ قَدۡ أُوتِيتَ سُؤۡلَكَ يَٰمُوسَىٰ

(Allah) Ya ce: “Haqiqa an ba ka abin da ka tambaya, ya Musa



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 37

وَلَقَدۡ مَنَنَّا عَلَيۡكَ مَرَّةً أُخۡرَىٰٓ

“Haqiqa kuma Mun yi ni’ima a gare ka a wani lokaci



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 38

إِذۡ أَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ أُمِّكَ مَا يُوحَىٰٓ

“Sanda Muka yiwo wahayi ga mahaifiyarka da abin da ake yin wahayi da shi



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 39

أَنِ ٱقۡذِفِيهِ فِي ٱلتَّابُوتِ فَٱقۡذِفِيهِ فِي ٱلۡيَمِّ فَلۡيُلۡقِهِ ٱلۡيَمُّ بِٱلسَّاحِلِ يَأۡخُذۡهُ عَدُوّٞ لِّي وَعَدُوّٞ لَّهُۥۚ وَأَلۡقَيۡتُ عَلَيۡكَ مَحَبَّةٗ مِّنِّي وَلِتُصۡنَعَ عَلَىٰ عَيۡنِيٓ

“Cewa, ‘ki saka shi (jinjirin) a cikin akwatu, sannan ki jefa shi cikin kogi, to sai kogin ya jefa shi a gava, sai maqiyina kuma maqiyinsa ya xauke shi.’ Na kuma sanya maka farin jini daga gare Ni, don kuma a yi tarbiyar ka a gaban idona



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 40

إِذۡ تَمۡشِيٓ أُخۡتُكَ فَتَقُولُ هَلۡ أَدُلُّكُمۡ عَلَىٰ مَن يَكۡفُلُهُۥۖ فَرَجَعۡنَٰكَ إِلَىٰٓ أُمِّكَ كَيۡ تَقَرَّ عَيۡنُهَا وَلَا تَحۡزَنَۚ وَقَتَلۡتَ نَفۡسٗا فَنَجَّيۡنَٰكَ مِنَ ٱلۡغَمِّ وَفَتَنَّـٰكَ فُتُونٗاۚ فَلَبِثۡتَ سِنِينَ فِيٓ أَهۡلِ مَدۡيَنَ ثُمَّ جِئۡتَ عَلَىٰ قَدَرٖ يَٰمُوسَىٰ

“Lokacin da ‘yar’uwarka take tafiya tana cewa (da su): ‘Yanzu ba na haxa ku da wadda za ta raine shi ba?’ Sai Muka komo da kai zuwa ga mahaifiyarka don zuciyarta ta yi sanyi, kada kuma ta yi baqin ciki. Kuma ka kashe wani mutum[1] sannan Muka tserar da kai daga uquba, Muka kuma jarrabe ka da jarrabobi daban-daban. Sannan ka zauna shekaru a cikin mutanen Madyana, sannan ka zo (nan) daidai lokacin da Na qadarta (maka annabta) ya Musa


1- Shi ne Baqibxen da Annabi Musa ya naushe shi ya faxi nan take ya mutu.


السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 41

وَٱصۡطَنَعۡتُكَ لِنَفۡسِي

“Kuma Na zave ka don kaina[1]


1- Watau Allah () ya zave shi domin ya yi magana da shi, ya aika shi zuwa Fir’auna da mutanensa.


السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 42

ٱذۡهَبۡ أَنتَ وَأَخُوكَ بِـَٔايَٰتِي وَلَا تَنِيَا فِي ذِكۡرِي

“Ka tafi kai da xan’uwanka da ayoyina, kada kuwa ku sassauta game da ambatona



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 43

ٱذۡهَبَآ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

“Ku tafi wurin Fir’auna, don ko lalle ya wuce iyaka



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 44

فَقُولَا لَهُۥ قَوۡلٗا لَّيِّنٗا لَّعَلَّهُۥ يَتَذَكَّرُ أَوۡ يَخۡشَىٰ

“Sai ku gaya masa magana mai taushi, ko wataqila zai wa’azantu ko kuma ya ji tsoron (azabar Allah).”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 45

قَالَا رَبَّنَآ إِنَّنَا نَخَافُ أَن يَفۡرُطَ عَلَيۡنَآ أَوۡ أَن يَطۡغَىٰ

(Musa da Haruna) suka ce: “Ya Ubangijinmu, lalle mu muna tsoron ya far mana ko kuma ya wuce iyaka (wajen yi mana uquba).”



السورة: Suratu Xa Ha

الآية : 46

قَالَ لَا تَخَافَآۖ إِنَّنِي مَعَكُمَآ أَسۡمَعُ وَأَرَىٰ

Ya ce: “Kada ku ji tsoro; haqiqa Ni ina tare da ku, ina ji kuma ina ganin (komai)