السورة: Suratul Kahf 

الآية : 40

فَعَسَىٰ رَبِّيٓ أَن يُؤۡتِيَنِ خَيۡرٗا مِّن جَنَّتِكَ وَيُرۡسِلَ عَلَيۡهَا حُسۡبَانٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ فَتُصۡبِحَ صَعِيدٗا زَلَقًا

“To ina fatan Ubangijina Ya ba ni fiye da gonarka, Ya kuma aiko mata (gonarka) da wani bala’i daga sama, sannan ta wayi gari ta zama qeqasasshiyar qasa mai santsi



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 41

أَوۡ يُصۡبِحَ مَآؤُهَا غَوۡرٗا فَلَن تَسۡتَطِيعَ لَهُۥ طَلَبٗا

“Ko kuma ruwanta ya zama ya qafe qarqaf, ba ko za ka sami hanyar samo shi ba.”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 42

وَأُحِيطَ بِثَمَرِهِۦ فَأَصۡبَحَ يُقَلِّبُ كَفَّيۡهِ عَلَىٰ مَآ أَنفَقَ فِيهَا وَهِيَ خَاوِيَةٌ عَلَىٰ عُرُوشِهَا وَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُشۡرِكۡ بِرَبِّيٓ أَحَدٗا

Aka kuwa hallaka ‘ya’yan itacen nasa, sannan ya wayi gari yana tafa hannayensa kan irin abin da ya vatar a kanta, ita kuwa ga ta ta zubo a kan dirkokinta, yana kuma cewa: “Kaicona, ina ma ban haxa wani da Ubangijina ba!”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 43

وَلَمۡ تَكُن لَّهُۥ فِئَةٞ يَنصُرُونَهُۥ مِن دُونِ ٱللَّهِ وَمَا كَانَ مُنتَصِرًا

Ba shi kuwa da wata qungiya da za ta taimake shi ban da Allah, kuma bai zamo mai taimaka wa (kansa) ba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 44

هُنَالِكَ ٱلۡوَلَٰيَةُ لِلَّهِ ٱلۡحَقِّۚ هُوَ خَيۡرٞ ثَوَابٗا وَخَيۡرٌ عُقۡبٗا

A wannan lokacin ne (ya bayyana) cewa taimako na Allah ne Tabbataccen (Sarki). Shi ne Fiyayyen Mai ba da lada kuma Fiyayyen Mai kyautata qarshe



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 45

وَٱضۡرِبۡ لَهُم مَّثَلَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَآءٍ أَنزَلۡنَٰهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ فَٱخۡتَلَطَ بِهِۦ نَبَاتُ ٱلۡأَرۡضِ فَأَصۡبَحَ هَشِيمٗا تَذۡرُوهُ ٱلرِّيَٰحُۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ مُّقۡتَدِرًا

Kuma ka ba su misalin rayuwar duniya (wadda take) kamar ruwa ne da Muka saukar da shi daga sama, sai tsirran qasa suka cakuxa da shi, sannan ya zama busasshe, iska tana xaixaita shi. Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan komai



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 46

ٱلۡمَالُ وَٱلۡبَنُونَ زِينَةُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَٱلۡبَٰقِيَٰتُ ٱلصَّـٰلِحَٰتُ خَيۡرٌ عِندَ رَبِّكَ ثَوَابٗا وَخَيۡرٌ أَمَلٗا

Dukiya da ‘ya’ya adon rayuwar duniya ne; wanzazzun ayyuka nagari kuwa su suka fi lada a wurin Ubangijinka kuma su ne buri mafi alheri



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 47

وَيَوۡمَ نُسَيِّرُ ٱلۡجِبَالَ وَتَرَى ٱلۡأَرۡضَ بَارِزَةٗ وَحَشَرۡنَٰهُمۡ فَلَمۡ نُغَادِرۡ مِنۡهُمۡ أَحَدٗا

Kuma ka tuna ranar da za Mu tafiyar da duwatsu kuma ka ga qasa a baje (ba tudu ba rafi), Mu kuma tattara su (gaba xaya), ba Mu bar xaya daga cikinsu ba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 48

وَعُرِضُواْ عَلَىٰ رَبِّكَ صَفّٗا لَّقَدۡ جِئۡتُمُونَا كَمَا خَلَقۡنَٰكُمۡ أَوَّلَ مَرَّةِۭۚ بَلۡ زَعَمۡتُمۡ أَلَّن نَّجۡعَلَ لَكُم مَّوۡعِدٗا

Aka kuma kawo su a gaban Ubangijinka sahu-sahu (a ce da su): “Haqiqa kun zo mana kamar yadda tun farko Muka halicce ku. Ba ma haka ba, kun riya cewa ba za Mu sanya muku wani wa’adi ba.”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 49

وَوُضِعَ ٱلۡكِتَٰبُ فَتَرَى ٱلۡمُجۡرِمِينَ مُشۡفِقِينَ مِمَّا فِيهِ وَيَقُولُونَ يَٰوَيۡلَتَنَا مَالِ هَٰذَا ٱلۡكِتَٰبِ لَا يُغَادِرُ صَغِيرَةٗ وَلَا كَبِيرَةً إِلَّآ أَحۡصَىٰهَاۚ وَوَجَدُواْ مَا عَمِلُواْ حَاضِرٗاۗ وَلَا يَظۡلِمُ رَبُّكَ أَحَدٗا

Aka kuma ajiye littafin (ayyukansu), sannan sai ka ga masu laifi suna cike da tsoron abin da yake cikinsa, suna kuma cewa: “Kaiconmu, me ya sami wannan littafin, ba ya barin (aiki) qarami balle babba sai ya qididdige su. Suka kuma sami (duk) abubuwan da suka aikata an zo da su. Ubangijinka kuwa ba zai zalunci kowa ba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 50

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ كَانَ مِنَ ٱلۡجِنِّ فَفَسَقَ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِۦٓۗ أَفَتَتَّخِذُونَهُۥ وَذُرِّيَّتَهُۥٓ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِي وَهُمۡ لَكُمۡ عَدُوُّۢۚ بِئۡسَ لِلظَّـٰلِمِينَ بَدَلٗا

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce da mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu”, sai suka yi sujjadar in ban da Iblis, ya kasance kuwa daga cikin aljannu, sai ya sava wa umarnin Ubangijinsa. Yanzu kwa riqe shi shi da zurriyarsa masoya ba Ni ba, alhali kuwa su maqiyanku ne? Wannan canji na azzalumai ya munana



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 51

۞مَّآ أَشۡهَدتُّهُمۡ خَلۡقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلَا خَلۡقَ أَنفُسِهِمۡ وَمَا كُنتُ مُتَّخِذَ ٱلۡمُضِلِّينَ عَضُدٗا

Ban halarto da su ba lokacin halittar sammai da qasa, ko ma halittar kawunansu, ban kuma kasance Mai riqon masu vatarwa mataimaka ba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 52

وَيَوۡمَ يَقُولُ نَادُواْ شُرَكَآءِيَ ٱلَّذِينَ زَعَمۡتُمۡ فَدَعَوۡهُمۡ فَلَمۡ يَسۡتَجِيبُواْ لَهُمۡ وَجَعَلۡنَا بَيۡنَهُم مَّوۡبِقٗا

Kuma (ka tuna) ranar da (Allah) zai ce (da kafirai): “Ku kirawo abokan tarayyar nawa waxanda kuka riya (cewa su ne iyayen gijinku)”, to sai suka kirawo su, sai ba su amsa musu ba, Muka kuma sanya mahallaka a tsakaninsu



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 53

وَرَءَا ٱلۡمُجۡرِمُونَ ٱلنَّارَ فَظَنُّوٓاْ أَنَّهُم مُّوَاقِعُوهَا وَلَمۡ يَجِدُواْ عَنۡهَا مَصۡرِفٗا

Masu laifi kuma suka ga wuta sai suka tabbatar da cewa lalle za su shige ta ba kuwa za su sami wata makauta ba daga gare ta



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 54

وَلَقَدۡ صَرَّفۡنَا فِي هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ لِلنَّاسِ مِن كُلِّ مَثَلٖۚ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ أَكۡثَرَ شَيۡءٖ جَدَلٗا

Kuma haqiqa Mun sassarafa kowane irin misali ga mutane a cikin wannan Alqur’anin. Mutum kuwa ya kasance wanda ya fi komai yawan musu



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 55

وَمَا مَنَعَ ٱلنَّاسَ أَن يُؤۡمِنُوٓاْ إِذۡ جَآءَهُمُ ٱلۡهُدَىٰ وَيَسۡتَغۡفِرُواْ رَبَّهُمۡ إِلَّآ أَن تَأۡتِيَهُمۡ سُنَّةُ ٱلۡأَوَّلِينَ أَوۡ يَأۡتِيَهُمُ ٱلۡعَذَابُ قُبُلٗا

Ba kuwa abin da ya hana mutane su yi imani lokacin da shiriya ta zo musu, su kuma nemi gafarar Ubangijinsu har sai irin abin da ya zo wa mutanen farko ya zo musu, ko kuwa azaba ta zo musu gaba-da-gaba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 56

وَمَا نُرۡسِلُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ إِلَّا مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَۚ وَيُجَٰدِلُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِٱلۡبَٰطِلِ لِيُدۡحِضُواْ بِهِ ٱلۡحَقَّۖ وَٱتَّخَذُوٓاْ ءَايَٰتِي وَمَآ أُنذِرُواْ هُزُوٗا

Ba Mu kuma aiko da manzanni ba sai don su zama masu albishir mai gargaxi. Su kuma waxanda suka kafirce sai su dinga jayayya da qarya don su kawar da gaskiya da ita; suka kuma riqi ayoyina da kuma abin da aka yi musu gargaxi da shi a matsayin abin izgili



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 57

وَمَنۡ أَظۡلَمُ مِمَّن ذُكِّرَ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِۦ فَأَعۡرَضَ عَنۡهَا وَنَسِيَ مَا قَدَّمَتۡ يَدَاهُۚ إِنَّا جَعَلۡنَا عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ أَكِنَّةً أَن يَفۡقَهُوهُ وَفِيٓ ءَاذَانِهِمۡ وَقۡرٗاۖ وَإِن تَدۡعُهُمۡ إِلَى ٱلۡهُدَىٰ فَلَن يَهۡتَدُوٓاْ إِذًا أَبَدٗا

Wane ne ya fi zalunci fiye da wanda aka yi masa gargaxi da ayoyin Ubangijinsa sannan ya bijire musu, ya kuma manta abin da hannayensa suka gabatar (na mugun aiki). Lalle Mun sanya rufi a zukatansu don kada su fahimce shi (Alqur’ani), a cikin kunnuwansu kuma (Muka sanya) wani nauyi. Idan kuwa ka kirawo su zuwa ga shiriya to ba za su yi imani ba har abada



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 58

وَرَبُّكَ ٱلۡغَفُورُ ذُو ٱلرَّحۡمَةِۖ لَوۡ يُؤَاخِذُهُم بِمَا كَسَبُواْ لَعَجَّلَ لَهُمُ ٱلۡعَذَابَۚ بَل لَّهُم مَّوۡعِدٞ لَّن يَجِدُواْ مِن دُونِهِۦ مَوۡئِلٗا

Ubangijinka kuwa Mai yawan gafara ne Ma’abocin rahama; da Yana kama su da abin da suka aikata, to da Ya gaggauta musu azaba. A’a, (ba Ya yin haka), sai dai suna da qayyadajjen lokaci wanda ba za su sami wata makauta ba daga gare shi



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 59

وَتِلۡكَ ٱلۡقُرَىٰٓ أَهۡلَكۡنَٰهُمۡ لَمَّا ظَلَمُواْ وَجَعَلۡنَا لِمَهۡلِكِهِم مَّوۡعِدٗا

Kuma waxancan alqaryu Mun hallakar da su yayin da suka yi zalunci, Muka kuma sanya qayyadajjen lokaci na hallakar da su



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 60

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِفَتَىٰهُ لَآ أَبۡرَحُ حَتَّىٰٓ أَبۡلُغَ مَجۡمَعَ ٱلۡبَحۡرَيۡنِ أَوۡ أَمۡضِيَ حُقُبٗا

Kuma (ka tuna) lokacin da Musa ya ce da yaronsa: “Ba zan dakata da (tafiyata) ba har sai na kai mahaxar kogunan nan biyu, ko kuwa in zarce har tsawon shekaru[1].”


1- Daga nan har zuwa qarshen aya ta 82 Allah () ya ba da labarin tafiyar Annabi Musa () neman ilimi wajen Annabi Khadir (). Yaronsa shi ne Annabi Yusha’u ().


السورة: Suratul Kahf 

الآية : 61

فَلَمَّا بَلَغَا مَجۡمَعَ بَيۡنِهِمَا نَسِيَا حُوتَهُمَا فَٱتَّخَذَ سَبِيلَهُۥ فِي ٱلۡبَحۡرِ سَرَبٗا

To lokacin da suka isa mahaxar tasu (watau kogunan) sai suka manta da kifinsu wanda ya kama hanyarsa a cikin kogi kamar xakin qarqashin qasa



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 62

فَلَمَّا جَاوَزَا قَالَ لِفَتَىٰهُ ءَاتِنَا غَدَآءَنَا لَقَدۡ لَقِينَا مِن سَفَرِنَا هَٰذَا نَصَبٗا

To lokacin da suka wuce (wannan wuri) sai (Musa) ya ce da yaronsa: “Kawo mana abincinmu, haqiqa mun haxu da wahala cikin wannan tafiya tamu.”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 63

قَالَ أَرَءَيۡتَ إِذۡ أَوَيۡنَآ إِلَى ٱلصَّخۡرَةِ فَإِنِّي نَسِيتُ ٱلۡحُوتَ وَمَآ أَنسَىٰنِيهُ إِلَّا ٱلشَّيۡطَٰنُ أَنۡ أَذۡكُرَهُۥۚ وَٱتَّخَذَ سَبِيلَهُۥ فِي ٱلۡبَحۡرِ عَجَبٗا

Sai (yaron) ya ce: “Ba ka gani ba lokacin da muka fake a daidai dutsen nan ai sai na manta da kifin, ba kuwa wani ne ya mantar da ni shi ba sai Shaixan, ya hana ni in tuna. Sai kuma ya kama hanyarsa cikin kogi, abin mamaki!”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 64

قَالَ ذَٰلِكَ مَا كُنَّا نَبۡغِۚ فَٱرۡتَدَّا عَلَىٰٓ ءَاثَارِهِمَا قَصَصٗا

(Musa) ya ce: “Wannan da ma shi ne abin da muke nema”, Sai suka koma da baya suna bin sawunsu (ta inda suka fito)



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 65

فَوَجَدَا عَبۡدٗا مِّنۡ عِبَادِنَآ ءَاتَيۡنَٰهُ رَحۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَا وَعَلَّمۡنَٰهُ مِن لَّدُنَّا عِلۡمٗا

To sai suka sami wani bawa daga bayinmu wanda Muka bai wa rahama daga gare Mu, kuma Muka koyar da shi wani ilimi daga wajenmu



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 66

قَالَ لَهُۥ مُوسَىٰ هَلۡ أَتَّبِعُكَ عَلَىٰٓ أَن تُعَلِّمَنِ مِمَّا عُلِّمۡتَ رُشۡدٗا

Musa ya ce da shi: “Shin na iya bin ka don ka koyar da ni (wani abu) daga abin da aka koyar da kai na shiriya?”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 67

قَالَ إِنَّكَ لَن تَسۡتَطِيعَ مَعِيَ صَبۡرٗا

Ya ce: “Lalle ba za ka iya haquri da ni ba



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 68

وَكَيۡفَ تَصۡبِرُ عَلَىٰ مَا لَمۡ تُحِطۡ بِهِۦ خُبۡرٗا

“Qaqa kuwa za ka yi haquri kan abin da ba ka kewaye da saninsa ba?”



السورة: Suratul Kahf 

الآية : 69

قَالَ سَتَجِدُنِيٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ صَابِرٗا وَلَآ أَعۡصِي لَكَ أَمۡرٗا

(Musa) ya ce: “Za ka same ni mai haquri in sha Allahu, ba kuma zan sava wa umarninka ba.”