السورة: Suratul Anbiya

الآية : 91

وَٱلَّتِيٓ أَحۡصَنَتۡ فَرۡجَهَا فَنَفَخۡنَا فِيهَا مِن رُّوحِنَا وَجَعَلۡنَٰهَا وَٱبۡنَهَآ ءَايَةٗ لِّلۡعَٰلَمِينَ

(Ka tuna) kuma wadda ta tsare matancinta, sai Muka yi busa a cikinta daga Ruhinmu, Muka kuma sanya ta ita da xanta aya ga talikai



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 92

إِنَّ هَٰذِهِۦٓ أُمَّتُكُمۡ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ وَأَنَا۠ رَبُّكُمۡ فَٱعۡبُدُونِ

Lallai wannan addini naku guda xaya ne (wato Musulunci), kuma Ni ne Ubangijinku, to ku bauta min



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 93

وَتَقَطَّعُوٓاْ أَمۡرَهُم بَيۡنَهُمۡۖ كُلٌّ إِلَيۡنَا رَٰجِعُونَ

Sannan sai suka rarraba al’amarinsu (na addini) a tsakaninsu; dukkaninsu dai masu komowa ne zuwa gare Mu



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 94

فَمَن يَعۡمَلۡ مِنَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَلَا كُفۡرَانَ لِسَعۡيِهِۦ وَإِنَّا لَهُۥ كَٰتِبُونَ

To duk wanda ya aikata kyawawan ayyuka alhali kuwa shi mumini ne, to babu musantawa ga aikinsa[1], lallai kuma Mu Masu rubuta masa shi ne


1- Watau ba za a yi masa runton aikinsa mai kyau ba, za a yi masa kyakkyawar sakayya ne a kai.


السورة: Suratul Anbiya

الآية : 95

وَحَرَٰمٌ عَلَىٰ قَرۡيَةٍ أَهۡلَكۡنَٰهَآ أَنَّهُمۡ لَا يَرۡجِعُونَ

Kuma haramun ne ga (duk) wata al’umma da Muka hallaka cewa za su komo (duniya)



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 96

حَتَّىٰٓ إِذَا فُتِحَتۡ يَأۡجُوجُ وَمَأۡجُوجُ وَهُم مِّن كُلِّ حَدَبٖ يَنسِلُونَ

Har sai lokacin da aka buxe Yajuju da Majuju, su kuwa za su gangaro ne ta kowanne tudu



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 97

وَٱقۡتَرَبَ ٱلۡوَعۡدُ ٱلۡحَقُّ فَإِذَا هِيَ شَٰخِصَةٌ أَبۡصَٰرُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يَٰوَيۡلَنَا قَدۡ كُنَّا فِي غَفۡلَةٖ مِّنۡ هَٰذَا بَلۡ كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Kuma alqawarin gaskiya ya gabato, sai ga shi idanuwan waxanda suka kafirta sun yi zuru-zuru (suna cewa): “Kaiconmu! Haqiqa mun kasance cikin gafala game da wannan (ranar); a’a, kai mu dai mun kasance azzalumai ne!”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 98

إِنَّكُمۡ وَمَا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ حَصَبُ جَهَنَّمَ أَنتُمۡ لَهَا وَٰرِدُونَ

(Sai a ce da su): “Lallai ku da abin da kuke bauta wa ba Allah ba, (duka) makamashin Jahannama ne, kuma ku masu shigar ta ne.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 99

لَوۡ كَانَ هَـٰٓؤُلَآءِ ءَالِهَةٗ مَّا وَرَدُوهَاۖ وَكُلّٞ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Da waxancan (gumakan) sun kasance alloli (na gaske) da ba su shiga cikinta ba, dukkaninsu kuwa madawwama ne a cikinta



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 100

لَهُمۡ فِيهَا زَفِيرٞ وَهُمۡ فِيهَا لَا يَسۡمَعُونَ

Suna ta qaraji a cikinta, alhali kuwa su a cikinta ba sa jin (sautin komai)



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 101

إِنَّ ٱلَّذِينَ سَبَقَتۡ لَهُم مِّنَّا ٱلۡحُسۡنَىٰٓ أُوْلَـٰٓئِكَ عَنۡهَا مُبۡعَدُونَ

Lalle waxanda kalmarmu mafi kyau (ta cewa su ‘yan Aljanna ne) ta riga ta tabbata gare su, waxannan waxanda ake nesantawa ne daga gare ta (wutar)



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 102

لَا يَسۡمَعُونَ حَسِيسَهَاۖ وَهُمۡ فِي مَا ٱشۡتَهَتۡ أَنفُسُهُمۡ خَٰلِدُونَ

Ba za su ji hargowarta ba, kuma su masu dawwama ne cikin abin da ransu yake so



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 103

لَا يَحۡزُنُهُمُ ٱلۡفَزَعُ ٱلۡأَكۡبَرُ وَتَتَلَقَّىٰهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ هَٰذَا يَوۡمُكُمُ ٱلَّذِي كُنتُمۡ تُوعَدُونَ

Babbar firgitar (wannan ranar) ba ta samun su, kuma mala’iku za su tare su, (suna cewa): “Wannan ita ce ranar taku wadda kuka zamanto ana yi muku alqawarinta (a duniya).”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 104

يَوۡمَ نَطۡوِي ٱلسَّمَآءَ كَطَيِّ ٱلسِّجِلِّ لِلۡكُتُبِۚ كَمَا بَدَأۡنَآ أَوَّلَ خَلۡقٖ نُّعِيدُهُۥۚ وَعۡدًا عَلَيۡنَآۚ إِنَّا كُنَّا فَٰعِلِينَ

(Ita ce) ranar da za Mu naxe sama kamar naxin marubuci ga takardu. Kamar yadda Muka qagi halitta da farko (haka) za Mu mai da ita. Wannan alqawari ne da Muka xauka. Lallai Mun kasance Masu aikata (haka)



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 105

وَلَقَدۡ كَتَبۡنَا فِي ٱلزَّبُورِ مِنۢ بَعۡدِ ٱلذِّكۡرِ أَنَّ ٱلۡأَرۡضَ يَرِثُهَا عِبَادِيَ ٱلصَّـٰلِحُونَ

Kuma haqiqa Mun rubuta cikin saukakkun littattafai bayan (an rubuta a Lauhul-Mahfuzu) cewa, ita qasa bayina na gari ne za su gaje ta



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 106

إِنَّ فِي هَٰذَا لَبَلَٰغٗا لِّقَوۡمٍ عَٰبِدِينَ

Lallai a cikin wannan (Alqur’ani) akwai isar da saqo ga mutane masu bauta



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 107

وَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ إِلَّا رَحۡمَةٗ لِّلۡعَٰلَمِينَ

Ba Mu aiko ka ba sai don rahama ga talikai



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 108

قُلۡ إِنَّمَا يُوحَىٰٓ إِلَيَّ أَنَّمَآ إِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۖ فَهَلۡ أَنتُم مُّسۡلِمُونَ

Ka ce (da su): “Abin da kawai ake yiwo min wahayinsa (shi ne) lallai abin bautar ku Allah ne Guda Xaya; to shin ko za ku miqa wuya?”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 109

فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَقُلۡ ءَاذَنتُكُمۡ عَلَىٰ سَوَآءٖۖ وَإِنۡ أَدۡرِيٓ أَقَرِيبٌ أَم بَعِيدٞ مَّا تُوعَدُونَ

To idan sun ba da baya sai ka ce (da su): “Na sanar da ku cewa ni da ku muna kan abu xaya ne (wato ta-ware). Kuma ni ban sani ba, shin abin da ake yi muku alqawari da shi[1] kusa yake ko kuwa nesa?


1- Watau alqawarin zuwan azabar Allah a gare su.


السورة: Suratul Anbiya

الآية : 110

إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ مِنَ ٱلۡقَوۡلِ وَيَعۡلَمُ مَا تَكۡتُمُونَ

“Lalle Shi (Allah) Yana sane da (abin da kuke) bayyanawa na magana Yana kuma sane da abin da kuke voyewa



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 111

وَإِنۡ أَدۡرِي لَعَلَّهُۥ فِتۡنَةٞ لَّكُمۡ وَمَتَٰعٌ إِلَىٰ حِينٖ

“Kuma ban sani ba ko wataqila shi (jinkirta azabtar da ku) fitina ne a gare ku da kuma jin daxi zuwa wani xan lokaci



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 112

قَٰلَ رَبِّ ٱحۡكُم بِٱلۡحَقِّۗ وَرَبُّنَا ٱلرَّحۡمَٰنُ ٱلۡمُسۡتَعَانُ عَلَىٰ مَا تَصِفُونَ

(Annabi Muhammadu) ya ce: “Ya Ubangijina, Ka yi hukunci (tsakanina da kafirai) da gaskiya. Ubangijinmu kuwa (Shi ne) Ar-Rahamanu Wanda ake neman taimakonsa a kan abin da kuke siffantawa.”



السورة: Suratul Hajji

الآية : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمۡۚ إِنَّ زَلۡزَلَةَ ٱلسَّاعَةِ شَيۡءٌ عَظِيمٞ

Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku. Lalle girgizar (ranar) alqiyama abu ne mai girma



السورة: Suratul Hajji

الآية : 2

يَوۡمَ تَرَوۡنَهَا تَذۡهَلُ كُلُّ مُرۡضِعَةٍ عَمَّآ أَرۡضَعَتۡ وَتَضَعُ كُلُّ ذَاتِ حَمۡلٍ حَمۡلَهَا وَتَرَى ٱلنَّاسَ سُكَٰرَىٰ وَمَا هُم بِسُكَٰرَىٰ وَلَٰكِنَّ عَذَابَ ٱللَّهِ شَدِيدٞ

Ranar da za ku gan ta, (don tsananin firgita) kowacce mai shayarwa za ta manta da abin da ta shayar, kuma kowacce mai ciki ta zubar da cikinta, ka ga kuma mutane suna tangaxi, alhali kuwa ba bugaggu ba ne, sai dai azabar Allah ce mai tsanani



السورة: Suratul Hajji

الآية : 3

وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يُجَٰدِلُ فِي ٱللَّهِ بِغَيۡرِ عِلۡمٖ وَيَتَّبِعُ كُلَّ شَيۡطَٰنٖ مَّرِيدٖ

Daga mutane kuma akwai wanda yake jayayya game da Allah ba tare da wani ilimi ba, kuma yake bin kowanne shaixani mai tsaurin kai



السورة: Suratul Hajji

الآية : 4

كُتِبَ عَلَيۡهِ أَنَّهُۥ مَن تَوَلَّاهُ فَأَنَّهُۥ يُضِلُّهُۥ وَيَهۡدِيهِ إِلَىٰ عَذَابِ ٱلسَّعِيرِ

An qaddara masa (wato Shaixan) cewa duk wanda ya rungume shi to haqiqa zai vatar da shi kuma ya ja shi zuwa ga azaba ta (wutar) Sa’ira



السورة: Suratul Hajji

الآية : 5

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ إِن كُنتُمۡ فِي رَيۡبٖ مِّنَ ٱلۡبَعۡثِ فَإِنَّا خَلَقۡنَٰكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ مِن نُّطۡفَةٖ ثُمَّ مِنۡ عَلَقَةٖ ثُمَّ مِن مُّضۡغَةٖ مُّخَلَّقَةٖ وَغَيۡرِ مُخَلَّقَةٖ لِّنُبَيِّنَ لَكُمۡۚ وَنُقِرُّ فِي ٱلۡأَرۡحَامِ مَا نَشَآءُ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗى ثُمَّ نُخۡرِجُكُمۡ طِفۡلٗا ثُمَّ لِتَبۡلُغُوٓاْ أَشُدَّكُمۡۖ وَمِنكُم مَّن يُتَوَفَّىٰ وَمِنكُم مَّن يُرَدُّ إِلَىٰٓ أَرۡذَلِ ٱلۡعُمُرِ لِكَيۡلَا يَعۡلَمَ مِنۢ بَعۡدِ عِلۡمٖ شَيۡـٔٗاۚ وَتَرَى ٱلۡأَرۡضَ هَامِدَةٗ فَإِذَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡهَا ٱلۡمَآءَ ٱهۡتَزَّتۡ وَرَبَتۡ وَأَنۢبَتَتۡ مِن كُلِّ زَوۡجِۭ بَهِيجٖ

Ya ku mutane, idan kun zamanto cikin kokwanton tashi (bayan mutuwa), to lalle Mu Muka halicce ku daga qasa, sannan daga maniyyi, sannan daga gudan jini, sannan daga tsoka, mai cikakkiyar halitta da kuma wadda ba cikakkiya ba[1], don Mu bayyana muku (Ikonmu). Kuma Muna tabbatar da abin da Muka ga dama a cikin mahaifa har zuwa wani lokaci qayyadajje, sannan kuma Mu fito da ku kuna jarirai, sannan kuma don ku kai cikar qarfinku; daga cikinku akwai wanda za a karvi ransa, akwai kuma wanda za a bari har zuwa mafi qasqantar rayuwa don ya kai ga halin da ba zai san komai ba bayan kuwa da can ya sani. Za ka kuma ga qasa a qeqashe, sannan idan Muka saukar mata da ruwa sai ta girgiza ta kumbura kuma ta fitar da kowanne irin tsiro mai qayatarwa


1- Watau tsokar ta zama wata halitta wadda ba cikakken mutum ba, daga bisani a yi varin ta.


السورة: Suratul Hajji

الآية : 6

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡحَقُّ وَأَنَّهُۥ يُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَأَنَّهُۥ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Wannan (kuwa) saboda lalle Allah Shi ne gaskiya, kuma lalle Shi ne Yake raya matattu, kuma lalle Mai iko ne a kan komai



السورة: Suratul Hajji

الآية : 7

وَأَنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٞ لَّا رَيۡبَ فِيهَا وَأَنَّ ٱللَّهَ يَبۡعَثُ مَن فِي ٱلۡقُبُورِ

Kuma lalle Alqiyama za ta zo babu kokwanto game da ita, kuma lalle Allah zai tashi waxanda suke cikin qaburbura



السورة: Suratul Hajji

الآية : 8

وَمِنَ ٱلنَّاسِ مَن يُجَٰدِلُ فِي ٱللَّهِ بِغَيۡرِ عِلۡمٖ وَلَا هُدٗى وَلَا كِتَٰبٖ مُّنِيرٖ

Daga mutane kuma akwai wanda yake jayayya game da (al’amarin) Allah ba tare da ilimi ba ko shiriya ko kuma wani littafi mai haske