السورة: Suratu Yunus

الآية : 24

إِنَّمَا مَثَلُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا كَمَآءٍ أَنزَلۡنَٰهُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ فَٱخۡتَلَطَ بِهِۦ نَبَاتُ ٱلۡأَرۡضِ مِمَّا يَأۡكُلُ ٱلنَّاسُ وَٱلۡأَنۡعَٰمُ حَتَّىٰٓ إِذَآ أَخَذَتِ ٱلۡأَرۡضُ زُخۡرُفَهَا وَٱزَّيَّنَتۡ وَظَنَّ أَهۡلُهَآ أَنَّهُمۡ قَٰدِرُونَ عَلَيۡهَآ أَتَىٰهَآ أَمۡرُنَا لَيۡلًا أَوۡ نَهَارٗا فَجَعَلۡنَٰهَا حَصِيدٗا كَأَن لَّمۡ تَغۡنَ بِٱلۡأَمۡسِۚ كَذَٰلِكَ نُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يَتَفَكَّرُونَ

Misalin rayuwar duniya kawai kamar ruwa ne da Muka saukar da shi daga sama, to sai shukokin da suke kan qasa suka cuxanya da shi daga abin da mutane da dabbobi suke ci; har lokacin da qasa ta qawata (da shi) ta kuma yi ado; masu ita kuma suka sakankance cewa su masu ikon cin amfaninta ne, sai qaddararmu ta zo mata cikin dare ko rana, sai Muka mayar da ita girbabbiya kamar daxai ba ta rayu ba a jiya. Kamar haka Muke bayyana ayoyi ga mutanen da suke tunani



السورة: Suratu Yunus

الآية : 25

وَٱللَّهُ يَدۡعُوٓاْ إِلَىٰ دَارِ ٱلسَّلَٰمِ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Allah kuwa Yana kira ne zuwa gidan aminci (wato Aljanna), Yana kuma shiryar da wanda Ya ga dama zuwa tafarki madaidaici



السورة: Suratu Yunus

الآية : 26

۞لِّلَّذِينَ أَحۡسَنُواْ ٱلۡحُسۡنَىٰ وَزِيَادَةٞۖ وَلَا يَرۡهَقُ وُجُوهَهُمۡ قَتَرٞ وَلَا ذِلَّةٌۚ أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡجَنَّةِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Waxanda suka kyautata aiki suna da sakamako mafi kyau (watau Aljanna) da kuma qari[1]. Wani qunci da qasqanci kuma ba za su same su ba. Waxannan su ne ‘yan Aljanna; su masu dawwama ne a cikinta


1- Watau shi ne ganin Fuskar Allah () bayan shigarsu Aljanna. Duba Muslim #181.


السورة: Suratu Yunus

الآية : 27

وَٱلَّذِينَ كَسَبُواْ ٱلسَّيِّـَٔاتِ جَزَآءُ سَيِّئَةِۭ بِمِثۡلِهَا وَتَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۖ مَّا لَهُم مِّنَ ٱللَّهِ مِنۡ عَاصِمٖۖ كَأَنَّمَآ أُغۡشِيَتۡ وُجُوهُهُمۡ قِطَعٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مُظۡلِمًاۚ أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Waxanda kuma suka yi mummunan aiki, to sakamakon mummunan aiki irinsa ne, kuma qasqanci zai lulluve su; ba su da wani mai kare su daga (azabar) Allah; kamar dai an lulluve fuskokinsu ne da wani yanki na dare mai duhu qirin. Waxannan su ne ‘yan wuta; su kuma masu dawwama ne a cikinta



السورة: Suratu Yunus

الآية : 28

وَيَوۡمَ نَحۡشُرُهُمۡ جَمِيعٗا ثُمَّ نَقُولُ لِلَّذِينَ أَشۡرَكُواْ مَكَانَكُمۡ أَنتُمۡ وَشُرَكَآؤُكُمۡۚ فَزَيَّلۡنَا بَيۡنَهُمۡۖ وَقَالَ شُرَكَآؤُهُم مَّا كُنتُمۡ إِيَّانَا تَعۡبُدُونَ

(Ka tuna) ranar da za mu tara su ga baki xaya, sannan mu ce da waxanda suka yi shirka: “Ku tsaya cak a wurarenku ku da abokan tarayyarku”. Sai kuma mu raba tsakaninsu; sai abokan tarayyarsu kuma su ce: “Ba mu ne kuka kasance kuna bauta wa ba



السورة: Suratu Yunus

الآية : 29

فَكَفَىٰ بِٱللَّهِ شَهِيدَۢا بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمۡ إِن كُنَّا عَنۡ عِبَادَتِكُمۡ لَغَٰفِلِينَ

“To kuma Allah Ya isa shaida tsakaninmu da ku: mu kam lalle mun kasance ba mu ma san kuna bautar mu ba.”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 30

هُنَالِكَ تَبۡلُواْ كُلُّ نَفۡسٖ مَّآ أَسۡلَفَتۡۚ وَرُدُّوٓاْ إِلَى ٱللَّهِ مَوۡلَىٰهُمُ ٱلۡحَقِّۖ وَضَلَّ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يَفۡتَرُونَ

A can ne kowane rai zai samu sakamakon abin da ya gabatar (a duniya). An kuma mayar da su zuwa ga Allah Majivincinsu na gaskiya; abin da kuma suka kasance suna qirqira ya vace musu



السورة: Suratu Yunus

الآية : 31

قُلۡ مَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أَمَّن يَمۡلِكُ ٱلسَّمۡعَ وَٱلۡأَبۡصَٰرَ وَمَن يُخۡرِجُ ٱلۡحَيَّ مِنَ ٱلۡمَيِّتِ وَيُخۡرِجُ ٱلۡمَيِّتَ مِنَ ٱلۡحَيِّ وَمَن يُدَبِّرُ ٱلۡأَمۡرَۚ فَسَيَقُولُونَ ٱللَّهُۚ فَقُلۡ أَفَلَا تَتَّقُونَ

Ka ce: “Wane ne yake arzuta ku ta sama da qasa? Ko kuma wane ne mamallakin ji da gani? Kuma wane ne yake fitar da mai rai daga matacce, ya kuma fitar da matacce daga mai rai? Wane ne kuma yake tsara al’amura?” To ai za su ce: “Allah ne.” To ka ce: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokinsa ba?”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 32

فَذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمُ ٱلۡحَقُّۖ فَمَاذَا بَعۡدَ ٱلۡحَقِّ إِلَّا ٱلضَّلَٰلُۖ فَأَنَّىٰ تُصۡرَفُونَ

To wannan Shi ne Allah Ubangijinku na gaskiya. Bayan gaskiya kuwa babu wani abu sai vata. To yaya ake karkatar da ku?



السورة: Suratu Yunus

الآية : 33

كَذَٰلِكَ حَقَّتۡ كَلِمَتُ رَبِّكَ عَلَى ٱلَّذِينَ فَسَقُوٓاْ أَنَّهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Kamar haka ne kalmar Ubangijinka ta tabbata a kan waxanda suka yi fasiqanci cewa su ba za su yi imani ba



السورة: Suratu Yunus

الآية : 34

قُلۡ هَلۡ مِن شُرَكَآئِكُم مَّن يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥۚ قُلِ ٱللَّهُ يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥۖ فَأَنَّىٰ تُؤۡفَكُونَ

Ka ce: “Shin daga cikin abokan tarayyarku ko akwai wanda yake qaga halitta, sannan ya maimaita ta?” Ka ce: “Allah Shi ne Wanda Yake qaga halitta sannan Ya maimaita ta. To ta yaya ake kautar da ku?”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 35

قُلۡ هَلۡ مِن شُرَكَآئِكُم مَّن يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلۡحَقِّۚ قُلِ ٱللَّهُ يَهۡدِي لِلۡحَقِّۗ أَفَمَن يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلۡحَقِّ أَحَقُّ أَن يُتَّبَعَ أَمَّن لَّا يَهِدِّيٓ إِلَّآ أَن يُهۡدَىٰۖ فَمَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ

Ka ce: “Shin daga abokan tarayyarku ko akwai wanda yake shiryarwa zuwa gaskiya?” Ka ce: “Allah Shi ne Yake shiryarwa zuwa ga gaskiya. To yanzu wanda yake shiryarwa zuwa gaskiya shi ya fi cancanta a bi, ko kuwa wanda ba ya shiryarwa sai dai a shiryar da shi? To me ya same ku ne? Yaya kuke wannan hukuncin?



السورة: Suratu Yunus

الآية : 36

وَمَا يَتَّبِعُ أَكۡثَرُهُمۡ إِلَّا ظَنًّاۚ إِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـًٔاۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Yawancinsu kuma ba abin da suke bi sai zato. Lalle zato ba ya wadatar da komai game da gaskiya. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne



السورة: Suratu Yunus

الآية : 37

وَمَا كَانَ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانُ أَن يُفۡتَرَىٰ مِن دُونِ ٱللَّهِ وَلَٰكِن تَصۡدِيقَ ٱلَّذِي بَيۡنَ يَدَيۡهِ وَتَفۡصِيلَ ٱلۡكِتَٰبِ لَا رَيۡبَ فِيهِ مِن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Wannan Alqur’ani bai yiwuwa a qage shi daga (tunanin) wani wanda ba Allah ba, sai dai (shi) gaskatawa ne ga abin da ya gabace shi (na littattafan da aka saukar), kuma bayani ne dalla-dalla na hukunce-hukuncen (da Allah ya saukar); babu kokwanto a cikinsa cewa daga Ubangijin talikai yake



السورة: Suratu Yunus

الآية : 38

أَمۡ يَقُولُونَ ٱفۡتَرَىٰهُۖ قُلۡ فَأۡتُواْ بِسُورَةٖ مِّثۡلِهِۦ وَٱدۡعُواْ مَنِ ٱسۡتَطَعۡتُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ko kuma cewa suke yi: “Qagar sa ya yi ne?” Ka ce: “To ku kawo sura (xaya tal) irinsa, kuma ku kirawo wanda duk za ku iya (ya taimaka muku) wanda ba Allah ba idan kun kasance masu gaskiya!”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 39

بَلۡ كَذَّبُواْ بِمَا لَمۡ يُحِيطُواْ بِعِلۡمِهِۦ وَلَمَّا يَأۡتِهِمۡ تَأۡوِيلُهُۥۚ كَذَٰلِكَ كَذَّبَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۖ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلظَّـٰلِمِينَ

A’a, ba haka ba ne, sun dai qaryata abin da ba su da iliminsa ne, kuma har yanzu haqiqanin fassararsa ba ta zo musu ba. Kamar haka ne waxanda suka gabace su suka qaryata. To duba ka ga yadda qarshen azzalumai ya zama



السورة: Suratu Yunus

الآية : 40

وَمِنۡهُم مَّن يُؤۡمِنُ بِهِۦ وَمِنۡهُم مَّن لَّا يُؤۡمِنُ بِهِۦۚ وَرَبُّكَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُفۡسِدِينَ

Daga cikinsu kuma akwai wanda yake yin imani da shi (Alqur’ani), akwai kuma wanda ba ya yin imani da shi. Ubangijinka kuma Shi ne Mafi sanin mavarnata



السورة: Suratu Yunus

الآية : 41

وَإِن كَذَّبُوكَ فَقُل لِّي عَمَلِي وَلَكُمۡ عَمَلُكُمۡۖ أَنتُم بَرِيٓـُٔونَ مِمَّآ أَعۡمَلُ وَأَنَا۠ بَرِيٓءٞ مِّمَّا تَعۡمَلُونَ

Idan kuwa suka qaryata ka, to ka ce: “Aikina nawa ne ku ma aikinku naku ne. Ku babu ruwanku da abin da nake aikatawa, ni ma kuma babu ruwana da abin da kuke aikatawa.”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 42

وَمِنۡهُم مَّن يَسۡتَمِعُونَ إِلَيۡكَۚ أَفَأَنتَ تُسۡمِعُ ٱلصُّمَّ وَلَوۡ كَانُواْ لَا يَعۡقِلُونَ

Daga cikinsu akwai waxanda suke sauraron ka. Yanzu kai za ka iya jiyar da kurame ko da ba su da hankali?



السورة: Suratu Yunus

الآية : 43

وَمِنۡهُم مَّن يَنظُرُ إِلَيۡكَۚ أَفَأَنتَ تَهۡدِي ٱلۡعُمۡيَ وَلَوۡ كَانُواْ لَا يُبۡصِرُونَ

Daga cikinsu kuma akwai wanda yake qura maka ido. Yanzu kai za ka iya shiryar da makafi ko da ba sa gani?



السورة: Suratu Yunus

الآية : 44

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَظۡلِمُ ٱلنَّاسَ شَيۡـٔٗا وَلَٰكِنَّ ٱلنَّاسَ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Lalle Allah ba Ya zaluntar mutane da komai, sai dai mutane kawunansu kawai suke zalunta



السورة: Suratu Yunus

الآية : 45

وَيَوۡمَ يَحۡشُرُهُمۡ كَأَن لَّمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا سَاعَةٗ مِّنَ ٱلنَّهَارِ يَتَعَارَفُونَ بَيۡنَهُمۡۚ قَدۡ خَسِرَ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِلِقَآءِ ٱللَّهِ وَمَا كَانُواْ مُهۡتَدِينَ

Ranar da zai tattara su kuwa (za su ga) kamar ba su zauna ba sai wani xan lokaci na rana da suke gane junansu (a cikinsa). Haqiqa waxanda suka qaryata gamuwa da Allah sun tave, ba su kuma zamanto shiryayyu ba



السورة: Suratu Yunus

الآية : 46

وَإِمَّا نُرِيَنَّكَ بَعۡضَ ٱلَّذِي نَعِدُهُمۡ أَوۡ نَتَوَفَّيَنَّكَ فَإِلَيۡنَا مَرۡجِعُهُمۡ ثُمَّ ٱللَّهُ شَهِيدٌ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ

Ko dai Mu nuna maka sashin abin da Muke musu alkawarinsa ko kuma Mu karvi ranka, to makomarsu dai gare Mu take, sannan Allah Yana sane da abin da suke aikatawa



السورة: Suratu Yunus

الآية : 47

وَلِكُلِّ أُمَّةٖ رَّسُولٞۖ فَإِذَا جَآءَ رَسُولُهُمۡ قُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡقِسۡطِ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Kowacce al’umma kuma tana da manzo. To idan manzonsu ya zo (suka qaryata shi) to sai a yi hukunci a tsakaninsu da adalci, su kuma ba za a zalunce su ba



السورة: Suratu Yunus

الآية : 48

وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلۡوَعۡدُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Suna kuma cewa: “To yaushe ne wannan alqawari (zai zo) idan kun kasance masu gaskiya?”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 49

قُل لَّآ أَمۡلِكُ لِنَفۡسِي ضَرّٗا وَلَا نَفۡعًا إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۗ لِكُلِّ أُمَّةٍ أَجَلٌۚ إِذَا جَآءَ أَجَلُهُمۡ فَلَا يَسۡتَـٔۡخِرُونَ سَاعَةٗ وَلَا يَسۡتَقۡدِمُونَ

Ka ce: “Ba na mallakar wata cuta, ko wani amfani ga kaina sai dai abin da Allah Ya ga dama. Kowacce al’umma tana da lokacin (da aka iyakance mata). Idan lokacin nasu ya yi, to ba za su yi jinkiri na sa’a guda ba, kuma ba za su gaggauto ba.”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 50

قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَتَىٰكُمۡ عَذَابُهُۥ بَيَٰتًا أَوۡ نَهَارٗا مَّاذَا يَسۡتَعۡجِلُ مِنۡهُ ٱلۡمُجۡرِمُونَ

Ka ce: “Yanzu ku ba ni labari (yadda za ku yi) idan azabar Allah ta zo muku da daddare ko da rana; mene ne masu laifi suke yi wa gaggawar zuwansa?



السورة: Suratu Yunus

الآية : 51

أَثُمَّ إِذَا مَا وَقَعَ ءَامَنتُم بِهِۦٓۚ ءَآلۡـَٰٔنَ وَقَدۡ كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ

“Shin sai idan (azabar) ta afka (muku) ne za ku yi imani da Shi (Allah)? Sai yanzu ne, alhali kuwa da can kun kasance kuna neman gaggautowarta?”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 52

ثُمَّ قِيلَ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ ذُوقُواْ عَذَابَ ٱلۡخُلۡدِ هَلۡ تُجۡزَوۡنَ إِلَّا بِمَا كُنتُمۡ تَكۡسِبُونَ

Sannan aka ce da waxanda suka yi zalunci: “Ku xanxani azaba mai dawwama; shin za a saka muku (da wani abu ne) in ban da abin da kuka kasance kuna aikatawa?.”



السورة: Suratu Yunus

الآية : 53

۞وَيَسۡتَنۢبِـُٔونَكَ أَحَقٌّ هُوَۖ قُلۡ إِي وَرَبِّيٓ إِنَّهُۥ لَحَقّٞۖ وَمَآ أَنتُم بِمُعۡجِزِينَ

Suna kuma tambayar ka cewa: “Yanzu (batun azabar nan) gaskiya ne kuwa?” Ka ce: “I mana, na ko ranste da Allah lalle shi gaskiya ne; ba kuma za ku kuvuce ba.”