السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 112

إِذۡ قَالَ ٱلۡحَوَارِيُّونَ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ هَلۡ يَسۡتَطِيعُ رَبُّكَ أَن يُنَزِّلَ عَلَيۡنَا مَآئِدَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِۖ قَالَ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Lokacin da Hawariyyawa suka ce: “Ya Isa xan Maryamu, shin Ubangijinka Yana iya saukar mana da kavaki daga sama?” Ya ce: “Ku kiyayi Allah, idan har kun kasance muminai.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 113

قَالُواْ نُرِيدُ أَن نَّأۡكُلَ مِنۡهَا وَتَطۡمَئِنَّ قُلُوبُنَا وَنَعۡلَمَ أَن قَدۡ صَدَقۡتَنَا وَنَكُونَ عَلَيۡهَا مِنَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

Suka ce: “Mu muna nufin mu ci daga gare shi, kuma zukatanmu su sami nutsuwa, sannan mu haqiqance cewa, lalle ka faxa mana gaskiya, kuma mu zamo masu ba da shaida a kansa.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 114

قَالَ عِيسَى ٱبۡنُ مَرۡيَمَ ٱللَّهُمَّ رَبَّنَآ أَنزِلۡ عَلَيۡنَا مَآئِدَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ تَكُونُ لَنَا عِيدٗا لِّأَوَّلِنَا وَءَاخِرِنَا وَءَايَةٗ مِّنكَۖ وَٱرۡزُقۡنَا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ

Isa xan Maryamu ya ce: “Ya Allah Ubangijinmu, Ka saukar mana da kavaki daga sama, wanda zai zame mana wani Idi, ga na farkonmu da na qarshenmu, kuma ya zamo wata aya daga gare Ka; kuma Ka arzuta mu, lalle Kai ne Fiyayyen masu arzutawa.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 115

قَالَ ٱللَّهُ إِنِّي مُنَزِّلُهَا عَلَيۡكُمۡۖ فَمَن يَكۡفُرۡ بَعۡدُ مِنكُمۡ فَإِنِّيٓ أُعَذِّبُهُۥ عَذَابٗا لَّآ أُعَذِّبُهُۥٓ أَحَدٗا مِّنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Allah Ya ce: “Lalle Ni Mai saukar muku da shi (kavakin) ne; amma duk wanda ya kafirta daga baya cikinku, to lalle Ni zan yi masa wata irin azaba wadda ba zan tava azabtar da wani daga cikin halittu irinta ba.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 116

وَإِذۡ قَالَ ٱللَّهُ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ءَأَنتَ قُلۡتَ لِلنَّاسِ ٱتَّخِذُونِي وَأُمِّيَ إِلَٰهَيۡنِ مِن دُونِ ٱللَّهِۖ قَالَ سُبۡحَٰنَكَ مَا يَكُونُ لِيٓ أَنۡ أَقُولَ مَا لَيۡسَ لِي بِحَقٍّۚ إِن كُنتُ قُلۡتُهُۥ فَقَدۡ عَلِمۡتَهُۥۚ تَعۡلَمُ مَا فِي نَفۡسِي وَلَآ أَعۡلَمُ مَا فِي نَفۡسِكَۚ إِنَّكَ أَنتَ عَلَّـٰمُ ٱلۡغُيُوبِ

Kuma (ka tuna) lokacin da Allah zai ce: “Ya kai Isa xan Maryamu, shin kai ne ka ce da mutane: ‘Ku riqe ni, ni da mahaifiyata a matsayin alloli biyu ban da Allah?’” Sai ya ce: “Tsarki ya tabbata gare Ka, bai dace ba a gare ni in faxi wani abu wanda ba ni da haqqin (faxar sa). Idan har na faxe shi, to haqiqa Ka riga Ka sani, Ka san abin da yake cikin raina, amma ni ban san abin da yake ranka ba. Lalle Kai ne Masanin abubuwan da suke voye



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 117

مَا قُلۡتُ لَهُمۡ إِلَّا مَآ أَمَرۡتَنِي بِهِۦٓ أَنِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ رَبِّي وَرَبَّكُمۡۚ وَكُنتُ عَلَيۡهِمۡ شَهِيدٗا مَّا دُمۡتُ فِيهِمۡۖ فَلَمَّا تَوَفَّيۡتَنِي كُنتَ أَنتَ ٱلرَّقِيبَ عَلَيۡهِمۡۚ وَأَنتَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

“Ban faxa musu komai ba sai abin da Ka umarce ni da shi, cewa: ‘Ku bauta wa Allah Ubangijina, kuma Ubangijinku.’ Kuma na kasance mai sa ido a kansu lokacin da nake cikinsu. Amma yayin da Ka karvi rayuwata, Ka zama Kai ne Mai kula da su. Kuma lalle Kai Mai kula ne a kan komai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 118

إِن تُعَذِّبۡهُمۡ فَإِنَّهُمۡ عِبَادُكَۖ وَإِن تَغۡفِرۡ لَهُمۡ فَإِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Idan har Ka azabtar da su, haqiqa su bayinka ne; idan kuwa Ka yafe musu, to lalle Kai Mabuwayi ne, Mai hikima.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 119

قَالَ ٱللَّهُ هَٰذَا يَوۡمُ يَنفَعُ ٱلصَّـٰدِقِينَ صِدۡقُهُمۡۚ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ رَّضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Allah zai ce: “Wannan ita ce rana wadda gaskiya za ta amfani masu ita. Suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, za su dawwama a cikinsu har abada. Allah Ya yarda da su, su kuma sun yarda da Shi. Wannan shi ne rabo mai girma.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 120

لِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا فِيهِنَّۚ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرُۢ

Mulkin sammai da qasa da abin da yake cikinsu na Allah ne. Kuma Shi Mai iko ne a kan komai



السورة: Suratul An’am

الآية : 1

ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَجَعَلَ ٱلظُّلُمَٰتِ وَٱلنُّورَۖ ثُمَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡ يَعۡدِلُونَ

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Wanda Ya halicci sammai da qasa, kuma Ya halicci duffai da haske; sannan waxanda suka kafirta suna daidaita Ubangijinsu da (wasu)



السورة: Suratul An’am

الآية : 2

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَكُم مِّن طِينٖ ثُمَّ قَضَىٰٓ أَجَلٗاۖ وَأَجَلٞ مُّسَمًّى عِندَهُۥۖ ثُمَّ أَنتُمۡ تَمۡتَرُونَ

Shi ne Wanda Ya halicce ku daga tavo, sannan Ya yanka (muku) ajali; da kuma wani ajalin sananne a wurinsa; sannan sai ga shi kuna jayayya



السورة: Suratul An’am

الآية : 3

وَهُوَ ٱللَّهُ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَفِي ٱلۡأَرۡضِ يَعۡلَمُ سِرَّكُمۡ وَجَهۡرَكُمۡ وَيَعۡلَمُ مَا تَكۡسِبُونَ

Kuma Shi ne Allah a cikin sammai da kuma cikin qasa; Yana sane da abin da kuke voyewa da abin da kuke bayyanawa, kuma Yana sane da abin da kuke aikatawa



السورة: Suratul An’am

الآية : 4

وَمَا تَأۡتِيهِم مِّنۡ ءَايَةٖ مِّنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِمۡ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهَا مُعۡرِضِينَ

Kuma babu wata aya cikin ayoyin Ubangijinsu da za ta zo musu, face sai sun kasance masu bijire mata



السورة: Suratul An’am

الآية : 5

فَقَدۡ كَذَّبُواْ بِٱلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُمۡ فَسَوۡفَ يَأۡتِيهِمۡ أَنۢبَـٰٓؤُاْ مَا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

To haqiqa sun qaryata gaskiya lokacin da ta zo musu; don haka da sannu labaran abin da suka kasance suna izgili da shi zai zo musu



السورة: Suratul An’am

الآية : 6

أَلَمۡ يَرَوۡاْ كَمۡ أَهۡلَكۡنَا مِن قَبۡلِهِم مِّن قَرۡنٖ مَّكَّنَّـٰهُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ مَا لَمۡ نُمَكِّن لَّكُمۡ وَأَرۡسَلۡنَا ٱلسَّمَآءَ عَلَيۡهِم مِّدۡرَارٗا وَجَعَلۡنَا ٱلۡأَنۡهَٰرَ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهِمۡ فَأَهۡلَكۡنَٰهُم بِذُنُوبِهِمۡ وَأَنشَأۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِمۡ قَرۡنًا ءَاخَرِينَ

Shin ba su ga yawan al’ummun da Muka halakar a gabaninsu ba, waxanda Muka kafa su a banqasa suka yi qarfi irin kafawar da ba Mu yi muku ba[1], kuma Muka aiko musu da ruwan sama a kai a kai, kuma Muka sanya qoramu suna gudana ta qarqashinsu, sai Muka hallakar da su saboda zunubansu, kuma bayan shuxewarsu Muka halicci wata sabuwar al’ummar daban?


1- Allah ya ba su qarfin jiki da yawan dukiya da ‘ya’ya. Dubi Suratur Rum aya ta 9-10 da Suratus Saba’i aya ta 45.


السورة: Suratul An’am

الآية : 7

وَلَوۡ نَزَّلۡنَا عَلَيۡكَ كِتَٰبٗا فِي قِرۡطَاسٖ فَلَمَسُوهُ بِأَيۡدِيهِمۡ لَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٞ

Kuma in da Mun saukar maka da wani littafin a rubuce a takardu, har suka tava shi da hannayensu, lalle da waxanda suka kafirta sun ce: “Wannan ba komai ba ne, face sihiri bayyananne.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 8

وَقَالُواْ لَوۡلَآ أُنزِلَ عَلَيۡهِ مَلَكٞۖ وَلَوۡ أَنزَلۡنَا مَلَكٗا لَّقُضِيَ ٱلۡأَمۡرُ ثُمَّ لَا يُنظَرُونَ

Kuma suka ce: “Don me ba a saukar masa da mala’ika ba?” Da kuwa Mun saukar da mala’ikan, to da ta faru ta qare (an hallaka su), sannan ba za a saurara musu ba



السورة: Suratul An’am

الآية : 9

وَلَوۡ جَعَلۡنَٰهُ مَلَكٗا لَّجَعَلۡنَٰهُ رَجُلٗا وَلَلَبَسۡنَا عَلَيۡهِم مَّا يَلۡبِسُونَ

Kuma in da Mun yo shi mala’ika ne, to lalle da Mun mayar da shi mutum, kuma da lalle Mun rikitar da su kamar yadda suka rikitar da kansu



السورة: Suratul An’am

الآية : 10

وَلَقَدِ ٱسۡتُهۡزِئَ بِرُسُلٖ مِّن قَبۡلِكَ فَحَاقَ بِٱلَّذِينَ سَخِرُواْ مِنۡهُم مَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Kuma haqiqa an yi wa waxansu manzanni da suka gabace ka izgili, sai sakamakon abin da suka kasance suna yin izgili da shi ya sauka kan masu izgilin



السورة: Suratul An’am

الآية : 11

قُلۡ سِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ ثُمَّ ٱنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Ka ce: “Ku yi tafiya a bayan qasa, sannan ku duba ku ga, yaya qarshen lamarin masu qaryatawa ya kasance?”



السورة: Suratul An’am

الآية : 12

قُل لِّمَن مَّا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ قُل لِّلَّهِۚ كَتَبَ عَلَىٰ نَفۡسِهِ ٱلرَّحۡمَةَۚ لَيَجۡمَعَنَّكُمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَا رَيۡبَ فِيهِۚ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Ka ce: “Abin da yake cikin sammai da qasa na wane ne?” Ka ce: “Na Allah ne.” Ya wajabta wa kansa yin rahama. Lalle tabbas zai tattara ku zuwa ranar tashin alqiyama wadda babu kokwanto game da ita. Waxanda suka yi hasarar kawunansu ba za su yi imani ba



السورة: Suratul An’am

الآية : 13

۞وَلَهُۥ مَا سَكَنَ فِي ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِۚ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

“Kuma abin da ya nutsu a cikin dare ko rana nasa ne, kuma Shi ne Mai ji, Mai yawan sani.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 14

قُلۡ أَغَيۡرَ ٱللَّهِ أَتَّخِذُ وَلِيّٗا فَاطِرِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَهُوَ يُطۡعِمُ وَلَا يُطۡعَمُۗ قُلۡ إِنِّيٓ أُمِرۡتُ أَنۡ أَكُونَ أَوَّلَ مَنۡ أَسۡلَمَۖ وَلَا تَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ka ce: “Shin yanzu wanin Allah ne zan riqa a matsayin majivinci, alhalin Shi ne Ya halicci sammai da qasa, kuma Shi Yake ciyarwa, ba a ciyar da Shi?” Ka ce: “Lalle ni an umarce ni da in zamo farkon mai miqa wuya; kuma lalle kada ka kasance daga masu shirka.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 15

قُلۡ إِنِّيٓ أَخَافُ إِنۡ عَصَيۡتُ رَبِّي عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

Ka ce: “Lalle ni ina jin tsoron azabar rana mai girma, idan na sava wa Ubangijina.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 16

مَّن يُصۡرَفۡ عَنۡهُ يَوۡمَئِذٖ فَقَدۡ رَحِمَهُۥۚ وَذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡمُبِينُ

Wanda duk aka kawar masa da (azaba) a wannan rana, to haqiqa (Allah) Ya ji qan sa. Kuma wannan Shi ne rabo mabayyani



السورة: Suratul An’am

الآية : 17

وَإِن يَمۡسَسۡكَ ٱللَّهُ بِضُرّٖ فَلَا كَاشِفَ لَهُۥٓ إِلَّا هُوَۖ وَإِن يَمۡسَسۡكَ بِخَيۡرٖ فَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Kuma idan Allah Ya shafe ka da wata cuta, to ba wanda ya isa ya yaye ta sai Shi; kuma idan Ya shafe ka da wani alheri, to Shi Mai iko ne a kan komai



السورة: Suratul An’am

الآية : 18

وَهُوَ ٱلۡقَاهِرُ فَوۡقَ عِبَادِهِۦۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡخَبِيرُ

Kuma Shi ne Mai rinjaye a kan bayinsa. Kuma Shi Mai hikima ne, Masani



السورة: Suratul An’am

الآية : 19

قُلۡ أَيُّ شَيۡءٍ أَكۡبَرُ شَهَٰدَةٗۖ قُلِ ٱللَّهُۖ شَهِيدُۢ بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡۚ وَأُوحِيَ إِلَيَّ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانُ لِأُنذِرَكُم بِهِۦ وَمَنۢ بَلَغَۚ أَئِنَّكُمۡ لَتَشۡهَدُونَ أَنَّ مَعَ ٱللَّهِ ءَالِهَةً أُخۡرَىٰۚ قُل لَّآ أَشۡهَدُۚ قُلۡ إِنَّمَا هُوَ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞ وَإِنَّنِي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تُشۡرِكُونَ

Ka ce: “Mene ne mafi girman shaida?” Ka ce; “Allah Shi ne shaida tsakanina da ku. Kuma an saukar mini wannan Alqur’anin ne don in yi muku gargaxi da shi da kuma duk wanda zai isa zuwa gare shi. Yanzu kuwa za ku shaida cewa, lalle akwai waxansu allolin tare da Allah?” Ka ce: “Ni kam ba zan shaida ba.” Ka ce: “Allah Shi Xaya ne, kuma lalle ni ba ruwana da dukkan abin da kuke haxa Allah da shi.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 20

ٱلَّذِينَ ءَاتَيۡنَٰهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ يَعۡرِفُونَهُۥ كَمَا يَعۡرِفُونَ أَبۡنَآءَهُمُۘ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Waxanda Muka ba su Littafi sun san shi kamar yadda suka san ‘ya’yansu. Waxanda suka yi hasarar kawunansu, to su kam ba za su tava yin imani ba



السورة: Suratul An’am

الآية : 21

وَمَنۡ أَظۡلَمُ مِمَّنِ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا أَوۡ كَذَّبَ بِـَٔايَٰتِهِۦٓۚ إِنَّهُۥ لَا يُفۡلِحُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Kuma ba mafi zalunci fiye da wanda ya qirqiri qarya ya jingina wa Allah, ko kuma ya qaryata ayoyinsa. Haqiqar lamarin dai su azzalumai ba za su tava rabauta ba