السورة: Suratus Sharh

الآية : 3

ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ

Wanda ya nauyayi bayanka?



السورة: Suratus Sharh

الآية : 4

وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ

Muka kuma xaukaka maka ambatonka[1]?


1- Watau kamar ambatonsa a cikin kiran salla da iqama da tahiya da sauransu.


السورة: Suratus Sharh

الآية : 5

فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا

To lalle tsanani yana tare da sauqi



السورة: Suratus Sharh

الآية : 6

إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا

Lalle tsananin yana tare da sauqi



السورة: Suratus Sharh

الآية : 7

فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ

Saboda haka idan ka gama (harkokinka) sai ka kafu (wajen bautar Allah)



السورة: Suratus Sharh

الآية : 8

وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب

Sannan kuma ka yi kwaxayi wajen Ubangijinka kawai



السورة: Suratut Tin

الآية : 1

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ

Na rantse da vaure da zaitun[1]


1- Watau wuraren tsirowarsu, watau Sham, ko kuma su kansu waxanan bishiyoyin.


السورة: Suratut Tin

الآية : 2

وَطُورِ سِينِينَ

Da (dutsen) Xuri Sinina



السورة: Suratut Tin

الآية : 3

وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ

Da wannan garin amintacce (watau Makka)



السورة: Suratut Tin

الآية : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ

Haqiqa Mun halicci mutum a kan mafi kyan diri



السورة: Suratut Tin

الآية : 5

ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ

Sannan Muka mayar da shi mafi qasqancin qasqantattu[1]


1- Watau ya mayar da shi tsoho tukuf a duniya, ko kuma a lahira ya zamanto xan wuta.


السورة: Suratut Tin

الآية : 6

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ

Sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, to su kam suna da lada ba mai yankewa ba



السورة: Suratut Tin

الآية : 7

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ

To (kai kafiri) me ya sa kake qaryata ranar sakamako bayan haka?



السورة: Suratut Tin

الآية : 8

أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ

Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?



السورة: Suratul Alaq

الآية : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta



السورة: Suratul Alaq

الآية : 2

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ

Ya halicci mutum daga gudan jini[1]


1- Watau bayan yana xigon maniyyi.


السورة: Suratul Alaq

الآية : 3

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ

Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci



السورة: Suratul Alaq

الآية : 4

ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ

Wanda Ya koyar ta (hanyar) alqalami



السورة: Suratul Alaq

الآية : 5

عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ

Ya koyar da mutum abin da bai sani ba



السورة: Suratul Alaq

الآية : 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ

Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa



السورة: Suratul Alaq

الآية : 7

أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ

Don ya ga kansa yana cikin wadata



السورة: Suratul Alaq

الآية : 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ

Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take



السورة: Suratul Alaq

الآية : 9

أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ

Ka ba ni labarin wanda yake hana



السورة: Suratul Alaq

الآية : 10

عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

Bawa yayin da ya yi salla



السورة: Suratul Alaq

الآية : 11

أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi Bawan) ya kasance a kan shiriya



السورة: Suratul Alaq

الآية : 12

أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ

Ko kuma ya yi umarni da taqawa



السورة: Suratul Alaq

الآية : 13

أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi mai hanawar) ya qaryata ya kuma ba da baya



السورة: Suratul Alaq

الآية : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



السورة: Suratul Alaq

الآية : 15

كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

A’aha! Tabbas idan bai hanu ba to za Mu ja shi ta makwarkwaxar kai



السورة: Suratul Alaq

الآية : 16

نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ

Makwarkwaxar kai mai qaryatawa, mai aikata laifi