السورة: Suratul Insan

الآية : 11

فَوَقَىٰهُمُ ٱللَّهُ شَرَّ ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمِ وَلَقَّىٰهُمۡ نَضۡرَةٗ وَسُرُورٗا

Sai Allah Ya kare su (daga) sharrin wannan ranar Ya kuma ba su haske (a fuskokinsu) da kuma farin ciki



السورة: Suratul Insan

الآية : 12

وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا

Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi



السورة: Suratul Insan

الآية : 13

مُّتَّكِـِٔينَ فِيهَا عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِۖ لَا يَرَوۡنَ فِيهَا شَمۡسٗا وَلَا زَمۡهَرِيرٗا

Suna masu kishingixa a cikinta a kan gadaje; ba sa ganin rana ko jin tsananin sanyi a cikinta



السورة: Suratul Insan

الآية : 14

وَدَانِيَةً عَلَيۡهِمۡ ظِلَٰلُهَا وَذُلِّلَتۡ قُطُوفُهَا تَذۡلِيلٗا

Inuwoyinta kuma suna kusa da su, an kuma hore musu ‘ya’yan itatuwanta matuqar horewa



السورة: Suratul Insan

الآية : 15

وَيُطَافُ عَلَيۡهِم بِـَٔانِيَةٖ مِّن فِضَّةٖ وَأَكۡوَابٖ كَانَتۡ قَوَارِيرَا۠

Ana kuma kai-kawo a tsakaninsu da qorai na azurfa da kofuna waxanda suka kasance na qarau



السورة: Suratul Insan

الآية : 16

قَوَارِيرَاْ مِن فِضَّةٖ قَدَّرُوهَا تَقۡدِيرٗا

Qarau xin na azurfa ne, sun auna su, aunawa daidai da buqata



السورة: Suratul Insan

الآية : 17

وَيُسۡقَوۡنَ فِيهَا كَأۡسٗا كَانَ مِزَاجُهَا زَنجَبِيلًا

Ana kuma shayar da su wata giya a cikinta, wadda mahaxinta ya kasance citta mai yatsu ce



السورة: Suratul Insan

الآية : 18

عَيۡنٗا فِيهَا تُسَمَّىٰ سَلۡسَبِيلٗا

Wani marmaro ne a cikinta da ake kiran sa Salsabilu



السورة: Suratul Insan

الآية : 19

۞وَيَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ وِلۡدَٰنٞ مُّخَلَّدُونَ إِذَا رَأَيۡتَهُمۡ حَسِبۡتَهُمۡ لُؤۡلُؤٗا مَّنثُورٗا

Samari hadimai dawwamammu (da ba sa tsufa) kuma suna kai-kawo tsakaninsu, idan ka gan su sai ka yi tsammanin su wani lu’ulu’u ne da aka baza



السورة: Suratul Insan

الآية : 20

وَإِذَا رَأَيۡتَ ثَمَّ رَأَيۡتَ نَعِيمٗا وَمُلۡكٗا كَبِيرًا

Idan kuma ka yi kallo a can, za ka ga ni’ima da kuma mulki qasaitacce



السورة: Suratul Insan

الآية : 21

عَٰلِيَهُمۡ ثِيَابُ سُندُسٍ خُضۡرٞ وَإِسۡتَبۡرَقٞۖ وَحُلُّوٓاْ أَسَاوِرَ مِن فِضَّةٖ وَسَقَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ شَرَابٗا طَهُورًا

Suna sanye da korayen tufafin alharini marar kauri da na alharini mai kauri; aka kuma yi musu ado da warawarai na azurfa, Ubangijinsu kuma Ya shayar da su abin sha mai tsarki



السورة: Suratul Insan

الآية : 22

إِنَّ هَٰذَا كَانَ لَكُمۡ جَزَآءٗ وَكَانَ سَعۡيُكُم مَّشۡكُورًا

Lalle wannan ya kasance sakamako ne a gare ku, kuma aikinku ya kasance abin godewa



السورة: Suratul Insan

الآية : 23

إِنَّا نَحۡنُ نَزَّلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ تَنزِيلٗا

Lalle Mu Muka saukar maka da Alqur’ani daki-daki



السورة: Suratul Insan

الآية : 24

فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تُطِعۡ مِنۡهُمۡ ءَاثِمًا أَوۡ كَفُورٗا

Saboda haka ka yi haquri da hukuncin Ubangijinka kada kuwa ka bi mai yawan savo ko mai yawan kafircewa daga cikinsu



السورة: Suratul Insan

الآية : 25

وَٱذۡكُرِ ٱسۡمَ رَبِّكَ بُكۡرَةٗ وَأَصِيلٗا

Ka kuma ambaci sunan Ubangijinka safe da yamma



السورة: Suratul Insan

الآية : 26

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَٱسۡجُدۡ لَهُۥ وَسَبِّحۡهُ لَيۡلٗا طَوِيلًا

Da daddare kuma sai ka yi sujjada a gare Shi, ka kuma yi nafiloli saboda Shi a tsawon dare



السورة: Suratul Insan

الآية : 27

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ يُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ وَيَذَرُونَ وَرَآءَهُمۡ يَوۡمٗا ثَقِيلٗا

Lalle waxannan suna son mai gaggawar qarewa (watau duniya), suna kuma watsi da rana mai nauyi[1] a bayansu


1- Watau ranar alqiyama mai cike da wahalhalu da musibu iri-iri.


السورة: Suratul Insan

الآية : 28

نَّحۡنُ خَلَقۡنَٰهُمۡ وَشَدَدۡنَآ أَسۡرَهُمۡۖ وَإِذَا شِئۡنَا بَدَّلۡنَآ أَمۡثَٰلَهُمۡ تَبۡدِيلًا

Mu Muka halicce su Muka kuma qarfafa gavovinsu; idan kuwa Muka ga dama sai Mu musanya irinsu (kyakkyawar) musanyawa



السورة: Suratul Insan

الآية : 29

إِنَّ هَٰذِهِۦ تَذۡكِرَةٞۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ سَبِيلٗا

Lalle wannan wa’azi ne; saboda haka wanda ya ga dama sai ya riqi hanya zuwa ga Ubangijinsa



السورة: Suratul Insan

الآية : 30

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma ba ganin damarku ba ce sai abin da Allah ya ga dama. Lalle Allah Ya kasance Masani, Mai hikima



السورة: Suratul Insan

الآية : 31

يُدۡخِلُ مَن يَشَآءُ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ وَٱلظَّـٰلِمِينَ أَعَدَّ لَهُمۡ عَذَابًا أَلِيمَۢا

Yana shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Azzalumai kuwa Ya tanadar musu azaba mai raxaxi



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 1

وَٱلۡمُرۡسَلَٰتِ عُرۡفٗا

Na rantse da iska mai bibiyar juna



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 2

فَٱلۡعَٰصِفَٰتِ عَصۡفٗا

Da kuma iska mai tasowa da tsanani



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 3

وَٱلنَّـٰشِرَٰتِ نَشۡرٗا

Da iska mai watso ruwa watsowa



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 4

فَٱلۡفَٰرِقَٰتِ فَرۡقٗا

Da kuma (mala’iku) masu rarrabe qarya da gaskiya iya rarrabewa



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 5

فَٱلۡمُلۡقِيَٰتِ ذِكۡرًا

Sannan masu sauko da wahayi



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 6

عُذۡرًا أَوۡ نُذۡرًا

Don yanke hanzari ko don gargaxi



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 7

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَوَٰقِعٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawari tabbas mai afkuwa ne



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 8

فَإِذَا ٱلنُّجُومُ طُمِسَتۡ

To idan taurari aka shafe haskensu



السورة: Suratul Mursalat

الآية : 9

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ فُرِجَتۡ

Idan kuma sama aka tsattsage ta