قَالُواْ ٱطَّيَّرۡنَا بِكَ وَبِمَن مَّعَكَۚ قَالَ طَـٰٓئِرُكُمۡ عِندَ ٱللَّهِۖ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ تُفۡتَنُونَ
Sai suka ce: “Mu mun camfa ka kai da waxanda suke tare da kai.” Sai ya ce: “Camfinku na ga Allah. A’a, ku dai mutane ne da ake jarraba ku.”
وَكَانَ فِي ٱلۡمَدِينَةِ تِسۡعَةُ رَهۡطٖ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ
A cikin birnin kuma akwai wani gungu na mutum tara waxanda suke varna a bayan qasa kuma ba sa gyara
قَالُواْ تَقَاسَمُواْ بِٱللَّهِ لَنُبَيِّتَنَّهُۥ وَأَهۡلَهُۥ ثُمَّ لَنَقُولَنَّ لِوَلِيِّهِۦ مَا شَهِدۡنَا مَهۡلِكَ أَهۡلِهِۦ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ
Sai suka ce wa (juna): “Ku rantse da Allah cewa, lalle za mu kashe shi cikin dare shi da iyalinsa, sannan za mu faxa wa mai neman jininsa cewa, ba mu halarci wurin kashe iyalinsa ba, kuma lalle mu masu gaskiya ne.”
وَمَكَرُواْ مَكۡرٗا وَمَكَرۡنَا مَكۡرٗا وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ
Kuma suka shirya makirci, Mu kuma Muka shirya rusa makircinsu alhali kuwa su ba su sani ba
فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ مَكۡرِهِمۡ أَنَّا دَمَّرۡنَٰهُمۡ وَقَوۡمَهُمۡ أَجۡمَعِينَ
Sai ka duba ka ga yadda qarshen makircinsu ya zama, watau Mun hallakar da su tare da mutanensu baki xaya
فَتِلۡكَ بُيُوتُهُمۡ خَاوِيَةَۢ بِمَا ظَلَمُوٓاْۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ
To ga gidajensu can a rugurguje babu kowa saboda zaluncinsu. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga mutanen da suke ganewa
وَأَنجَيۡنَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَكَانُواْ يَتَّقُونَ
Muka kuma tserar da waxanda suka yi imani, suka kuma kasance suna kiyaye dokokin Allah
وَلُوطًا إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَتَأۡتُونَ ٱلۡفَٰحِشَةَ وَأَنتُمۡ تُبۡصِرُونَ
Kuma ka (ambaci) Luxu lokacin da ya ce da mutanensa: “Yanzu kwa riqa zaike wa alfasha alhali kuwa kuna gani?
أَئِنَّكُمۡ لَتَأۡتُونَ ٱلرِّجَالَ شَهۡوَةٗ مِّن دُونِ ٱلنِّسَآءِۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ تَجۡهَلُونَ
“Yanzu kwa riqa zaike wa maza don sha’awa ba mata ba? A’a, ku dai wasu irin mutane ne da kuke da jahilci”