السورة: Suratul Muddassir

الآية : 47

حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ

“Har mutuwa ta zo mana.”



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 48

فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ

Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 49

فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ

To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 50

كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ

Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 51

فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ

Da suka guje wa zaki



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 52

بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ

A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)


1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.


السورة: Suratul Muddassir

الآية : 53

كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 54

كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ

Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 55

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu



السورة: Suratul Muddassir

الآية : 56

وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ

Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Ina rantsuwa da ranar alqiyama



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 2

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ

Ina kuma rantsuwa da rai mai yawan zargin (kansa)[1]


1- Watau a kan gazawarsa wajen ayyukan alheri ko a kan aikata laifuka.


السورة: Suratul Qiyama

الآية : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 5

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ

Ba haka ba ne, mutum yana nufi ne kawai ya gurvata gabansa (da savon Allah)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 6

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Yana tambaya yaushe ne ranar alqiyamar?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ

To lokacin da gani ya ruxe



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 8

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ

Wata kuma ya yi duhu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ

Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 16

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ

(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 17

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ

Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 18

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ

Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ

Sannan kuma bayaninsa yana kanmu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 20

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ

Haba, ku dai kawai kuna son duniya ne