السورة: Suratul A’araf

الآية : 171

۞وَإِذۡ نَتَقۡنَا ٱلۡجَبَلَ فَوۡقَهُمۡ كَأَنَّهُۥ ظُلَّةٞ وَظَنُّوٓاْ أَنَّهُۥ وَاقِعُۢ بِهِمۡ خُذُواْ مَآ ءَاتَيۡنَٰكُم بِقُوَّةٖ وَٱذۡكُرُواْ مَا فِيهِ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Ka tuna kuma lokacin da Muka xaga dutse a samansu kamar girgije, kuma suka sakankance cewa zai rikito musu, (Muka ce da su): “Ku riqe abin da Muka ba ku da kyau, kuma ku tuna abin da yake cikinsa, don su zamo masu kiyaye dokokin Allah.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 172

وَإِذۡ أَخَذَ رَبُّكَ مِنۢ بَنِيٓ ءَادَمَ مِن ظُهُورِهِمۡ ذُرِّيَّتَهُمۡ وَأَشۡهَدَهُمۡ عَلَىٰٓ أَنفُسِهِمۡ أَلَسۡتُ بِرَبِّكُمۡۖ قَالُواْ بَلَىٰ شَهِدۡنَآۚ أَن تَقُولُواْ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ إِنَّا كُنَّا عَنۡ هَٰذَا غَٰفِلِينَ

Ka tuna kuma lokacin da Ubangijinka Ya fitar da zurriyar ’yan’adam daga tsatsonsu[1], Ya kuma sa su suka yi wa kansu shaida, (Ya ce da su): “Yanzu ba Ni ne Ubangijinku ba?” Suka ce: “E Kai ne, mun shaida.” Don kada a ranar alqiyama ku ce: “Lalle mu mun kasance gafalallu a kan wannan.”


1- Bayan Allah () ya halicci Adamu () sai ya shafa bayansa sai duk wani rai da Allah zai halicce shi daga cikin zuriyyarsa har zuwa tashin qiyama ya fito daga tsatsonsa.


السورة: Suratul A’araf

الآية : 173

أَوۡ تَقُولُوٓاْ إِنَّمَآ أَشۡرَكَ ءَابَآؤُنَا مِن قَبۡلُ وَكُنَّا ذُرِّيَّةٗ مِّنۢ بَعۡدِهِمۡۖ أَفَتُهۡلِكُنَا بِمَا فَعَلَ ٱلۡمُبۡطِلُونَ

Ko kuma ku ce: “Iyayenmu da suka gabace mu kawai suka yi shirka, mu kuma zurriya ce da muka kasance a bayansu; yanzu Ka hallakar da mu saboda abin da mavarnata suka yi?”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 174

وَكَذَٰلِكَ نُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ وَلَعَلَّهُمۡ يَرۡجِعُونَ

Kuma kamar haka ne Muke bayyana ayoyi, don su komo wa (gaskiya)



السورة: Suratul A’araf

الآية : 175

وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ ٱلَّذِيٓ ءَاتَيۡنَٰهُ ءَايَٰتِنَا فَٱنسَلَخَ مِنۡهَا فَأَتۡبَعَهُ ٱلشَّيۡطَٰنُ فَكَانَ مِنَ ٱلۡغَاوِينَ

Ka kuma karanta musu labarin wannan da Muka ba shi ayoyinmu, sai ya saluve (jikinsa) daga gare su, sai Shaixan ya bi shi, don haka ya kasance cikin halakakku



السورة: Suratul A’araf

الآية : 176

وَلَوۡ شِئۡنَا لَرَفَعۡنَٰهُ بِهَا وَلَٰكِنَّهُۥٓ أَخۡلَدَ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُۚ فَمَثَلُهُۥ كَمَثَلِ ٱلۡكَلۡبِ إِن تَحۡمِلۡ عَلَيۡهِ يَلۡهَثۡ أَوۡ تَتۡرُكۡهُ يَلۡهَثۚ ذَّـٰلِكَ مَثَلُ ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَاۚ فَٱقۡصُصِ ٱلۡقَصَصَ لَعَلَّهُمۡ يَتَفَكَّرُونَ

Kuma da Mun ga dama da Mun xaukaka shi a sanadiyyarsu, amma kuma shi ya karkata zuwa ga duniya, don haka ya biye wa son zuciyarsa. To misalinsa kamar misalin kare ne, idan ka kai masa xauki ya yi lallage, idan ma ka qyale shi zai yi lallage, wannan shi ne misalin waxanda suka qaryata ayoyinmu. Don haka ka ba da labari don su yi tunani



السورة: Suratul A’araf

الآية : 177

سَآءَ مَثَلًا ٱلۡقَوۡمُ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَأَنفُسَهُمۡ كَانُواْ يَظۡلِمُونَ

Misalin waxanda suka qaryata ayoyinmu ya munana, kuma kawunansu suka kasance suna zalunta



السورة: Suratul A’araf

الآية : 178

مَن يَهۡدِ ٱللَّهُ فَهُوَ ٱلۡمُهۡتَدِيۖ وَمَن يُضۡلِلۡ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Wanda Allah Ya shiryar, to wannan shi ne shiryayye; wanda kuwa Ya vatar, to waxannan su ne hasararru



السورة: Suratul A’araf

الآية : 179

وَلَقَدۡ ذَرَأۡنَا لِجَهَنَّمَ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلۡجِنِّ وَٱلۡإِنسِۖ لَهُمۡ قُلُوبٞ لَّا يَفۡقَهُونَ بِهَا وَلَهُمۡ أَعۡيُنٞ لَّا يُبۡصِرُونَ بِهَا وَلَهُمۡ ءَاذَانٞ لَّا يَسۡمَعُونَ بِهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ كَٱلۡأَنۡعَٰمِ بَلۡ هُمۡ أَضَلُّۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡغَٰفِلُونَ

Kuma lalle haqiqa Mun halitta wa Jahannama da yawa daga cikin aljannu da mutane; ga su da zukata da ba sa hankalta da su, ga kuma idanu da ba sa kallo da su, ga kunnuwa da ba sa sauraro da su. Waxannan kamar dabbobi suke; a’a, sun ma fi (dabbobi) vacewa. Waxannan su ne gafalallu



السورة: Suratul A’araf

الآية : 180

وَلِلَّهِ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰ فَٱدۡعُوهُ بِهَاۖ وَذَرُواْ ٱلَّذِينَ يُلۡحِدُونَ فِيٓ أَسۡمَـٰٓئِهِۦۚ سَيُجۡزَوۡنَ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Allah kuma Yana da sunaye mafiya kyau, don haka ku roqe Shi da su; kuma ku rabu da waxanda suke fanxarewa game da sunayensa; da sannu za a yi musu sakamakon abin da suka kasance suna aikatawa



السورة: Suratul A’araf

الآية : 181

وَمِمَّنۡ خَلَقۡنَآ أُمَّةٞ يَهۡدُونَ بِٱلۡحَقِّ وَبِهِۦ يَعۡدِلُونَ

Kuma akwai wata al’umma daga cikin waxanda Muka halitta suna shiryarwa da gaskiya, kuma da ita suke adalci



السورة: Suratul A’araf

الآية : 182

وَٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا سَنَسۡتَدۡرِجُهُم مِّنۡ حَيۡثُ لَا يَعۡلَمُونَ

Kuma waxanda suka qaryata ayoyinmu, za Mu yi musu talala ta inda ba su sani ba



السورة: Suratul A’araf

الآية : 183

وَأُمۡلِي لَهُمۡۚ إِنَّ كَيۡدِي مَتِينٌ

Kuma Ina yi musu jinkiri ne; lalle kaidina mai qarfi ne



السورة: Suratul A’araf

الآية : 184

أَوَلَمۡ يَتَفَكَّرُواْۗ مَا بِصَاحِبِهِم مِّن جِنَّةٍۚ إِنۡ هُوَ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٌ

Shin ba za su yi tunani ba. Lalle abokin nasu fa babu hauka a tattare da shi. Ba kowa ne shi ba, face mai gargaxi, mai bayyanarwa?



السورة: Suratul A’araf

الآية : 185

أَوَلَمۡ يَنظُرُواْ فِي مَلَكُوتِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا خَلَقَ ٱللَّهُ مِن شَيۡءٖ وَأَنۡ عَسَىٰٓ أَن يَكُونَ قَدِ ٱقۡتَرَبَ أَجَلُهُمۡۖ فَبِأَيِّ حَدِيثِۭ بَعۡدَهُۥ يُؤۡمِنُونَ

Shin ba za su yi duba cikin mulkin sammai da qasa da kuma abin da Allah Ya halitta ba, kuma lalle ya kusata a ce ajalinsu yana gab da zuwa, to da wane zance ne za su yi imani bayansa (wato Alqur’ani)?



السورة: Suratul A’araf

الآية : 186

مَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَلَا هَادِيَ لَهُۥۚ وَيَذَرُهُمۡ فِي طُغۡيَٰنِهِمۡ يَعۡمَهُونَ

Wanda duk Allah Ya vatar, to ba shi da mai shiryar da shi. Kuma zai qyale su a cikin qetare iyakar da suke yi suna ximuwa



السورة: Suratul A’araf

الآية : 187

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ رَبِّيۖ لَا يُجَلِّيهَا لِوَقۡتِهَآ إِلَّا هُوَۚ ثَقُلَتۡ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَا تَأۡتِيكُمۡ إِلَّا بَغۡتَةٗۗ يَسۡـَٔلُونَكَ كَأَنَّكَ حَفِيٌّ عَنۡهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Suna tambayar ka game da tashin alqiyama yaushe ne matabbatarta take? Ka ce: “Sanin lokacinta yana wajen Ubangijina; ba mai bayyanar da lokacinta sai Shi. Ta yi nauyi a cikin sammai da qasa. Ba za ta zo muku ba sai katsahan.” Suna tambayar ka kamar ka nace a kanta, ka ce: “Iliminta yana wajen Allah kaxai”, sai dai da yawa daga cikin mutane ba su sani ba



السورة: Suratul A’araf

الآية : 188

قُل لَّآ أَمۡلِكُ لِنَفۡسِي نَفۡعٗا وَلَا ضَرًّا إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ وَلَوۡ كُنتُ أَعۡلَمُ ٱلۡغَيۡبَ لَٱسۡتَكۡثَرۡتُ مِنَ ٱلۡخَيۡرِ وَمَا مَسَّنِيَ ٱلسُّوٓءُۚ إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ وَبَشِيرٞ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Ka ce, “Ba na iya mallakar wa kaina wani amfani, ko wata cuta sai abin da Allah Ya ga dama. Kuma in da na kasance na san gaibu, lalle da na yawaita alheri, da kuma wani mummunan abu bai shafe ni ba. Ni ba wani ne ba face mai gargaxi mai bushara ga mutanen da suke yin imani.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 189

۞هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَكُم مِّن نَّفۡسٖ وَٰحِدَةٖ وَجَعَلَ مِنۡهَا زَوۡجَهَا لِيَسۡكُنَ إِلَيۡهَاۖ فَلَمَّا تَغَشَّىٰهَا حَمَلَتۡ حَمۡلًا خَفِيفٗا فَمَرَّتۡ بِهِۦۖ فَلَمَّآ أَثۡقَلَت دَّعَوَا ٱللَّهَ رَبَّهُمَا لَئِنۡ ءَاتَيۡتَنَا صَٰلِحٗا لَّنَكُونَنَّ مِنَ ٱلشَّـٰكِرِينَ

Shi ne Wanda Ya halicce ku daga rai guda xaya, kuma Ya halicci matarsa daga gare shi, don ya sami nutsuwa tare da ita; to yayin da ya kusance ta, sai ta xauki yaron ciki, sai ta ci gaba (da harkokinta) da shi, to yayin da (cikin) ya yi nauyi, sai suka roqi Allah Ubangijinsu cewa: “Lalle idan Ka ba mu xa lafiyayye[1], lalle za mu kasance masu godiya.”


1- Watau lafiyayye kuma nagari.


السورة: Suratul A’araf

الآية : 190

فَلَمَّآ ءَاتَىٰهُمَا صَٰلِحٗا جَعَلَا لَهُۥ شُرَكَآءَ فِيمَآ ءَاتَىٰهُمَاۚ فَتَعَٰلَى ٱللَّهُ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

To yayin da Ya ba su[1] xa lafiyayye, sai suka sanya masa abubuwan tarayya cikin abin da ya ba su. Allah kuwa ya xaukaka ga barin abin da suke shirka da Shi


1- Watau ana nufin cikin zuriyyar Adamu da Hauwa’u waxanda suka riqa yi wa Allah kishiyoyi bayan ni’imar da ya yi musu.


السورة: Suratul A’araf

الآية : 191

أَيُشۡرِكُونَ مَا لَا يَخۡلُقُ شَيۡـٔٗا وَهُمۡ يُخۡلَقُونَ

Shin sa riqa haxa (Allah) da abin da ba ya halittar komai, hasali ma su ne ake halitta?



السورة: Suratul A’araf

الآية : 192

وَلَا يَسۡتَطِيعُونَ لَهُمۡ نَصۡرٗا وَلَآ أَنفُسَهُمۡ يَنصُرُونَ

Kuma ba za su iya taimaka musu ba, ba kuma za su iya taimaka wa kawunansu ba?



السورة: Suratul A’araf

الآية : 193

وَإِن تَدۡعُوهُمۡ إِلَى ٱلۡهُدَىٰ لَا يَتَّبِعُوكُمۡۚ سَوَآءٌ عَلَيۡكُمۡ أَدَعَوۡتُمُوهُمۡ أَمۡ أَنتُمۡ صَٰمِتُونَ

Kuma in da za ku kirawo su zuwa shiriya, to lalle ba za su bi ku ba. Duk xaya ne a gare ku kun kirawo su, ko kuma kun yi shiru?



السورة: Suratul A’araf

الآية : 194

إِنَّ ٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ عِبَادٌ أَمۡثَالُكُمۡۖ فَٱدۡعُوهُمۡ فَلۡيَسۡتَجِيبُواْ لَكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Lalle waxanda kuke kira ba Allah ba bayi ne kamarku, to ku kirawo su mana, sai su kuma su amsa muku idan kun kasance masu gaskiya ne



السورة: Suratul A’araf

الآية : 195

أَلَهُمۡ أَرۡجُلٞ يَمۡشُونَ بِهَآۖ أَمۡ لَهُمۡ أَيۡدٖ يَبۡطِشُونَ بِهَآۖ أَمۡ لَهُمۡ أَعۡيُنٞ يُبۡصِرُونَ بِهَآۖ أَمۡ لَهُمۡ ءَاذَانٞ يَسۡمَعُونَ بِهَاۗ قُلِ ٱدۡعُواْ شُرَكَآءَكُمۡ ثُمَّ كِيدُونِ فَلَا تُنظِرُونِ

Shin wai suna da qafafun da suke tafiya da su ne; ko suna da hannayen da suke damqa da su, ko kuma suna da wasu idanuwa da suke gani da su; ko suna da wasu kunnuwa da suke saurare da su? Ka ce: “Ku kirawo abokan tarayyarku, sannan ku shirya mini makirci kuma kada ku saurara mini.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 196

إِنَّ وَلِـِّۧيَ ٱللَّهُ ٱلَّذِي نَزَّلَ ٱلۡكِتَٰبَۖ وَهُوَ يَتَوَلَّى ٱلصَّـٰلِحِينَ

“Lalle Majivincin lamarina Shi ne Allah Wanda Ya saukar da Littafi; kuma Shi Yake jivintar lamarin salihan bayi.”



السورة: Suratul A’araf

الآية : 197

وَٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ لَا يَسۡتَطِيعُونَ نَصۡرَكُمۡ وَلَآ أَنفُسَهُمۡ يَنصُرُونَ

Waxanda kuke kira ba Shi ba kuwa, ba za su iya taimakon ku ba, kuma ba za su iya taimaka wa kawunansu ba



السورة: Suratul A’araf

الآية : 198

وَإِن تَدۡعُوهُمۡ إِلَى ٱلۡهُدَىٰ لَا يَسۡمَعُواْۖ وَتَرَىٰهُمۡ يَنظُرُونَ إِلَيۡكَ وَهُمۡ لَا يُبۡصِرُونَ

Kuma idan da za ku yi kiran su zuwa ga shiriya, to fa ba za su ji ba; kuma za ka gan su suna kallon ka, alhali kuwa ba sa gani



السورة: Suratul A’araf

الآية : 199

خُذِ ٱلۡعَفۡوَ وَأۡمُرۡ بِٱلۡعُرۡفِ وَأَعۡرِضۡ عَنِ ٱلۡجَٰهِلِينَ

Ka yi riqo da afuwa, kuma ka yi umarni da kyakkyawan abu, ka kuma kawar da kai daga wawaye



السورة: Suratul A’araf

الآية : 200

وَإِمَّا يَنزَغَنَّكَ مِنَ ٱلشَّيۡطَٰنِ نَزۡغٞ فَٱسۡتَعِذۡ بِٱللَّهِۚ إِنَّهُۥ سَمِيعٌ عَلِيمٌ

Idan wani tunzuri daga Shaixan ya tunzura ka, to ka nemi tsarin Allah. Lalle Shi Mai ji ne, Masani