-
الحزب 53
الحزب 53
-
عدد الآيات :
196
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 10
فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَغۡلُوبٞ فَٱنتَصِرۡ
Sai ya roqi Ubangijinsa (cewa): “Lalle an fi qarfina, sai Ka taimaka.”
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 11
فَفَتَحۡنَآ أَبۡوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٖ مُّنۡهَمِرٖ
Sai Muka buxe qofofin sama da ruwa mai kwararowa
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 12
وَفَجَّرۡنَا ٱلۡأَرۡضَ عُيُونٗا فَٱلۡتَقَى ٱلۡمَآءُ عَلَىٰٓ أَمۡرٖ قَدۡ قُدِرَ
Muka kuma vuvvugar da idanuwan ruwa daga qasa, sai ruwayen suka haxu a bisa al’amarin da aka riga aka qaddara
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 13
وَحَمَلۡنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلۡوَٰحٖ وَدُسُرٖ
Muka kuma xauke shi a kan (jirgin ruwa) mai alluna da qusoshi
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 14
تَجۡرِي بِأَعۡيُنِنَا جَزَآءٗ لِّمَن كَانَ كُفِرَ
Yana gudu a kan idonmu, don ya zama sakayya ga wanda aka kafirce wa (watau Nuhu)
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 15
وَلَقَد تَّرَكۡنَٰهَآ ءَايَةٗ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ
Haqiqa kuma Mun bar (abin da ya faru) ya zama aya, to ko akwai mai wa’azantuwa?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 16
فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 17
وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ
Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunasarwa da hadda, to ko akwai mai wa’azantuwa?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 18
كَذَّبَتۡ عَادٞ فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
Adawa sun qaryata (Annabinsu), to qaqa azabata da gargaxina suka kasance?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 19
إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ رِيحٗا صَرۡصَرٗا فِي يَوۡمِ نَحۡسٖ مُّسۡتَمِرّٖ
Lalle Mu Mun aiko musu da iska mai qarfi a ranar shu’umci mai zarcewa
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 20
تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمۡ أَعۡجَازُ نَخۡلٖ مُّنقَعِرٖ
Tana tumvuko mutane[1] ta kayar su, kai ka ce su kututturan dabinai ne da aka tuttunvuke
1- Watau daga doron qasa ta yi sama da su sannan ta kifo da su ta kawunansu su faxo qasa a mace.
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 21
فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 22
وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ
Kuma haqiqa Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 23
كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ
Samudawa sun qaryata gargaxi
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 24
فَقَالُوٓاْ أَبَشَرٗا مِّنَّا وَٰحِدٗا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذٗا لَّفِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٍ
Sannan suka ce: “Yanzu mutum xaya daga cikinmu ne za mu bi? To lalle idan mun yi haka, mun tabbata cikin vata da hauka
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 25
أَءُلۡقِيَ ٱلذِّكۡرُ عَلَيۡهِ مِنۢ بَيۡنِنَا بَلۡ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٞ
“Yanzu (zai yiwu) a saukar masa da wahayi a tsakaninmu? A’a, shi dai maqaryaci ne mai tsananin girman kai.”
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 26
سَيَعۡلَمُونَ غَدٗا مَّنِ ٱلۡكَذَّابُ ٱلۡأَشِرُ
A gobe lalle za su san wane ne maqaryacin mai girman kai
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 27
إِنَّا مُرۡسِلُواْ ٱلنَّاقَةِ فِتۡنَةٗ لَّهُمۡ فَٱرۡتَقِبۡهُمۡ وَٱصۡطَبِرۡ
Lalle Mu Masu aiko taguwa ne don ta zama fitina a gare su, saboda haka ka saurara musu, kuma ka jure
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 28
وَنَبِّئۡهُمۡ أَنَّ ٱلۡمَآءَ قِسۡمَةُۢ بَيۡنَهُمۡۖ كُلُّ شِرۡبٖ مُّحۡتَضَرٞ
Kuma ka ba su labarin cewa ruwan sha an raba ne tsakaninsu (da ita taguwar); kowane akwai ranar shansa
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 29
فَنَادَوۡاْ صَاحِبَهُمۡ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ
Sai suka kirawo (shaqiyin) abokin nasu sai ya xauki (abin sara) sai ya sare ta
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 30
فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ
To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 31
إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ فَكَانُواْ كَهَشِيمِ ٱلۡمُحۡتَظِرِ
Lalle Mun aika musu da tsawa guda xaya, sai suka zamo kamar duddugar ciyawa a garken makiyayi
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 32
وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ
Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 33
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطِۭ بِٱلنُّذُرِ
Mutanen Luxu sun qaryata gargaxi
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 34
إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٖۖ نَّجَّيۡنَٰهُم بِسَحَرٖ
Lalle Mun aika musu da iska cike da duwatsu (ta hallaka su), sai dai iyalin Luxu kaxai Muka tserar da su a lokacin asuba
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 35
نِّعۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَاۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي مَن شَكَرَ
(Wannan) ni’ima ce daga wurinmu. Kamar haka Muke saka wa wanda ya yi godiya
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 36
وَلَقَدۡ أَنذَرَهُم بَطۡشَتَنَا فَتَمَارَوۡاْ بِٱلنُّذُرِ
Kuma haqiqa ya tsoratar da su irin damqarmu, sai suka yi jayayya da gargaxin (da ya yi musu)
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 37
وَلَقَدۡ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيۡفِهِۦ فَطَمَسۡنَآ أَعۡيُنَهُمۡ فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ
Haqiqa kuma sun nemi baqinsa[1] da lalata, sai Muka shafe idanuwansu, (Muka ce da su): “Sai ku xanxani azabata da gargaxina.
1- Su ne mala’iku da suka zo masa a siffar mutane matasa kyawawa.
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 38
وَلَقَدۡ صَبَّحَهُم بُكۡرَةً عَذَابٞ مُّسۡتَقِرّٞ
Haqiqa kuma azaba matabbaciya ta yi musu sammako da asuba.
-
-
تم
خطأ
-
السورة:
Suratul Qamar
الآية : 39
فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ
Saboda haka ku xanxani azabata da gargaxina.”
-
-
تم
خطأ
-