السورة: Suratul Balad

الآية : 16

أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ

Ko miskini ma’abocin talauci



السورة: Suratul Balad

الآية : 17

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ

Sannan kuma ya zama daga waxanda suka yi imani, suka yi wa junansu wasiyya da yin haquri kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayawa



السورة: Suratul Balad

الآية : 18

أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

Waxannan su ne ma’abota dama[1]


1- Watau ‘yan Aljanna.


السورة: Suratul Balad

الآية : 19

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyinmu, su ne ma’abota hagu[1]


1- Watau ‘yan wuta.


السورة: Suratul Balad

الآية : 20

عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ

A kansu akwai wuta abar kullewa



السورة: Suratus Shams

الآية : 1

وَٱلشَّمۡسِ وَضُحَىٰهَا

Na rantse da rana da walaharta



السورة: Suratus Shams

الآية : 2

وَٱلۡقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا

Da kuma wata idan ya bi ta (wato ranar)[1]


1- Watau ya biyo bayan faxuwar rana.


السورة: Suratus Shams

الآية : 3

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا

Da kuma wuni idan ya bayyana ta



السورة: Suratus Shams

الآية : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰهَا

Da kuma dare idan ya lulluve ta



السورة: Suratus Shams

الآية : 5

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا

Da kuma sama da gininta



السورة: Suratus Shams

الآية : 6

وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا طَحَىٰهَا

Da kuma qasa da shimfixarta



السورة: Suratus Shams

الآية : 7

وَنَفۡسٖ وَمَا سَوَّىٰهَا

Da kuma rai da daidaitarsa



السورة: Suratus Shams

الآية : 8

فَأَلۡهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقۡوَىٰهَا

Sai Ya kimsa masa (gane) lalacewarsa da taqawarsa



السورة: Suratus Shams

الآية : 9

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن زَكَّىٰهَا

Haqiqa wanda ya tsarkake shi (ran) ya rabauta



السورة: Suratus Shams

الآية : 10

وَقَدۡ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا

Haqiqa kuma wanda ya binne shi da savo ya tave



السورة: Suratus Shams

الآية : 11

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ

Samudawa sun qaryata saboda xagawarsu



السورة: Suratus Shams

الآية : 12

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا

Yayin da mafi tsagerancinsu ya zabura



السورة: Suratus Shams

الآية : 13

فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا

Sai Manzon Allah[1] ya ce da su: “Ku bar taguwar Allah da (ranar) shanta.”


1- Watau Annabi Salihu ().


السورة: Suratus Shams

الآية : 14

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا

Sai suka qaryata shi sannan suka soke ta, sai Ubangijinsu Ya kama su da azaba saboda zunubinsu, sai Ya daidaita ta (watau qabilar wajen azaba)



السورة: Suratus Shams

الآية : 15

وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا

Kuma ba Ya tsoron abin da zai biyo bayanta[1]


1- Watau ba ya jin tsoron wani abu da hallaka su za ta haifar nan gaba.


السورة: Suratul Lail

الآية : 1

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰ

Na rantse da dare idan ya lulluve (da duhunsa)



السورة: Suratul Lail

الآية : 2

وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ

Da kuma wuni idan ya bayyana



السورة: Suratul Lail

الآية : 3

وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Da kuma halittar namiji da mace



السورة: Suratul Lail

الآية : 4

إِنَّ سَعۡيَكُمۡ لَشَتَّىٰ

Lalle aikinku ya sha bamban



السورة: Suratul Lail

الآية : 5

فَأَمَّا مَنۡ أَعۡطَىٰ وَٱتَّقَىٰ

To wanda ya ba da (haqqoqin da ke kansa) ya kuma yi taqawa



السورة: Suratul Lail

الآية : 6

وَصَدَّقَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Ya kuma gaskata (sakamako) mafi kyau



السورة: Suratul Lail

الآية : 7

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡيُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu sauqaqa masa (hanyar) Aljanna



السورة: Suratul Lail

الآية : 8

وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسۡتَغۡنَىٰ

Amma kuma wanda ya yi rowa (da haqqin Allah) ya kuma wadatu (da neman lada)



السورة: Suratul Lail

الآية : 9

وَكَذَّبَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ

Kuma ya qaryata (sakamako) mafi kyau



السورة: Suratul Lail

الآية : 10

فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡعُسۡرَىٰ

To lalle ne za Mu hore masa (hanyar) wuta