السورة: Suratur Rahman

الآية : 61

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 62

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ

A qasa da su kuma akwai wasu aljannatai guda biyu



السورة: Suratur Rahman

الآية : 63

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 64

مُدۡهَآمَّتَانِ

Masu tsananin kore



السورة: Suratur Rahman

الآية : 65

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 66

فِيهِمَا عَيۡنَانِ نَضَّاخَتَانِ

A cikinsu (kuma) akwai idanuwan (ruwa) guda biyu masu feshi



السورة: Suratur Rahman

الآية : 67

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 68

فِيهِمَا فَٰكِهَةٞ وَنَخۡلٞ وَرُمَّانٞ

A cikinsu (kuma) akwai abin marmari da dabino da ruman



السورة: Suratur Rahman

الآية : 69

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 70

فِيهِنَّ خَيۡرَٰتٌ حِسَانٞ

A cikinsu (watau gidajen Aljannar) akwai mata nagartattu kyawawa



السورة: Suratur Rahman

الآية : 71

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 72

حُورٞ مَّقۡصُورَٰتٞ فِي ٱلۡخِيَامِ

(Matayen) masu fari da baqin ido ne, suna kawwame cikin tantuna



السورة: Suratur Rahman

الآية : 73

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 74

لَمۡ يَطۡمِثۡهُنَّ إِنسٞ قَبۡلَهُمۡ وَلَا جَآنّٞ

Wani mutum ko aljan bai tava shafar su ba a gabaninsu



السورة: Suratur Rahman

الآية : 75

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 76

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ رَفۡرَفٍ خُضۡرٖ وَعَبۡقَرِيٍّ حِسَانٖ

Suna kishingixe a kan matasan kai koraye, da kuma kilisai kyawawa



السورة: Suratur Rahman

الآية : 77

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



السورة: Suratur Rahman

الآية : 78

تَبَٰرَكَ ٱسۡمُ رَبِّكَ ذِي ٱلۡجَلَٰلِ وَٱلۡإِكۡرَامِ

Albarkatun sunan Ubangijinka Ma’abocin girma da xaukaka sun yawaita



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 1

إِذَا وَقَعَتِ ٱلۡوَاقِعَةُ

Idan mai afkowa ta afku (watau alqiyama)



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 2

لَيۡسَ لِوَقۡعَتِهَا كَاذِبَةٌ

Babu wani (rai) mai qaryata aukuwarta



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 3

خَافِضَةٞ رَّافِعَةٌ

Mai qasqantarwa ce mai xaukakawa



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 4

إِذَا رُجَّتِ ٱلۡأَرۡضُ رَجّٗا

Idan aka girgiza qasa girgizawa



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 5

وَبُسَّتِ ٱلۡجِبَالُ بَسّٗا

Aka kuma dandaqe duwatsu dandaqewa



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 6

فَكَانَتۡ هَبَآءٗ مُّنۢبَثّٗا

Suka zama qura abar sheqewa



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 7

وَكُنتُمۡ أَزۡوَٰجٗا ثَلَٰثَةٗ

Kuka kuma kasance dangogi guda uku



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 8

فَأَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

To ma’abota dama fa, mamakin darajar ma’abota dama!



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 9

وَأَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ مَآ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Da kuma ma’abota hagu, mamakin wulaqantar ma’abota hagu!



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 10

وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ

Da kuma masu rige-rige (zuwa alheri)



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 11

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡمُقَرَّبُونَ

Waxannan su ne makusanta



السورة: Suratul Waqi’a

الآية : 12

فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

A cikin gidajen Aljanna na ni’ima