السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 84

وَهُوَ ٱلَّذِي فِي ٱلسَّمَآءِ إِلَٰهٞ وَفِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَٰهٞۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ

Shi ne kuma Wanda Yake Abin bauta a cikin sama kuma Abin bauta a qasa. Kuma Shi Mai hikima ne, Masani



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 85

وَتَبَارَكَ ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلسَّاعَةِ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Kuma wanda Yake da mulkin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu alhairansa sun yi yawa, kuma a wurinsa sanin (ranar) alqiyama yake, wurinsa kuma za a komar da ku



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 86

وَلَا يَمۡلِكُ ٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ مِن دُونِهِ ٱلشَّفَٰعَةَ إِلَّا مَن شَهِدَ بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ يَعۡلَمُونَ

Waxanda kuwa suke bauta wa wani abu ba Shi ba, ba sa mallakar ceto, sai dai waxanda suka yi Kalmar Shahada ta gaskiya, alhalin suna sane (da ma’anarta)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 87

وَلَئِن سَأَلۡتَهُم مَّنۡ خَلَقَهُمۡ لَيَقُولُنَّ ٱللَّهُۖ فَأَنَّىٰ يُؤۡفَكُونَ

Tabbas kuma da za ka tambaye su, wane ne ya halicce su? Lalle za su ce: “Allah ne;” to ta yaya ake kautar da su?



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 88

وَقِيلِهِۦ يَٰرَبِّ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوۡمٞ لَّا يُؤۡمِنُونَ

Kuma (sanin) faxarsa (wato Ma’aiki) cewa: “Ya Ubangiji lalle waxannan mutane ne da ba sa yin imani,” (yana a wurinsa)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 89

فَٱصۡفَحۡ عَنۡهُمۡ وَقُلۡ سَلَٰمٞۚ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

To ka kawar musu kai, kuma ka ce: “Na kuvuta (daga haqqinku). Don haka ba da daxewa ba za ku sani.”



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 1

حمٓ

HA MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


السورة: Suratud Dukhan

الآية : 2

وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Na rantse da Littafi mai bayyanawa (shi ne Alqur’ani)



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 3

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةٖ مُّبَٰرَكَةٍۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ

Lalle Mu Muka saukar da shi a cikin dare mai albarka[1]. Lalle Mu Mun kasance Masu gargaxi


1- Shi ne daren Lailatul Qadari. Duba Suratul Qadri.


السورة: Suratud Dukhan

الآية : 4

فِيهَا يُفۡرَقُ كُلُّ أَمۡرٍ حَكِيمٍ

A cikinsa ne (daren) ake fasalta kowane tabbataccen al’amari (na wannan shekara)[1]


1- Watau al’amarin da ya shafi rabon arziqi da tsawon rai da sauran abubuwa da Allah ya qaddara za su faru a wannan shekarar.


السورة: Suratud Dukhan

الآية : 5

أَمۡرٗا مِّنۡ عِندِنَآۚ إِنَّا كُنَّا مُرۡسِلِينَ

Al’amari ne (da Muke fasaltawa) daga wurinmu. Lalle Mun kasance Mu ne Masu aikowa (da manzanni)



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 6

رَحۡمَةٗ مِّن رَّبِّكَۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Don rahama daga Ubangijinka. Lalle shi Mai ji ne, Masani



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 7

رَبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ

Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu; idan kun kasance masu sakankancewa



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 8

لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۖ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi, Shi ne Yake rayarwa Yake kuma kashewa; (Shi ne) Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 9

بَلۡ هُمۡ فِي شَكّٖ يَلۡعَبُونَ

A’a, su dai suna cikin shakka ne, suna wasanni



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 10

فَٱرۡتَقِبۡ يَوۡمَ تَأۡتِي ٱلسَّمَآءُ بِدُخَانٖ مُّبِينٖ

Sai ka saurari ranar da sama za ta zo da hayaqi bayyananne[1]


1- Shi ne hayaqi da idanuwansu za su riqa nuna musu, shi saboda tsananin yunwa.


السورة: Suratud Dukhan

الآية : 11

يَغۡشَى ٱلنَّاسَۖ هَٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٞ

Zai lulluve (idanuwan) mutane; wannan azaba ce mai raxaxi



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 12

رَّبَّنَا ٱكۡشِفۡ عَنَّا ٱلۡعَذَابَ إِنَّا مُؤۡمِنُونَ

(Za su ce): “Ya Ubangijinmu, Ka yaye mana wannan azaba, lalle mu masu yin imani ne.”



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 13

أَنَّىٰ لَهُمُ ٱلذِّكۡرَىٰ وَقَدۡ جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مُّبِينٞ

Ta ina wa’azi zai amfane su, alhali kuwa haqiqa Manzo mai bayani ya zo musu?



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 14

ثُمَّ تَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ وَقَالُواْ مُعَلَّمٞ مَّجۡنُونٌ

Sannan suka juya masa baya suka ce: “Ai wani ne ya koya masa, (kuma shi) tavavve ne



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 15

إِنَّا كَاشِفُواْ ٱلۡعَذَابِ قَلِيلًاۚ إِنَّكُمۡ عَآئِدُونَ

Lalle Mu Masu yaye muku azabar ne xan lokaci kaxan. Lalle (kuma) ku masu komawa ne



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 16

يَوۡمَ نَبۡطِشُ ٱلۡبَطۡشَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ إِنَّا مُنتَقِمُونَ

(Ka tuna) ranar da za Mu damqe su babbar damqa[1], lalle Mu Masu sakawa ne


1- Ita ce ranar yaqin Badar lokacin da Allah ya damqi manyan kafiran Makka aka karkashe su.


السورة: Suratud Dukhan

الآية : 17

۞وَلَقَدۡ فَتَنَّا قَبۡلَهُمۡ قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَ وَجَآءَهُمۡ رَسُولٞ كَرِيمٌ

Haqiqa kuma Mun jarrabi mutanen Fir’auna tun kafin su, kuma Manzo mai karamci ya zo musu



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 18

أَنۡ أَدُّوٓاْ إِلَيَّ عِبَادَ ٱللَّهِۖ إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

(Da cewa): “Ku ba ni bayin Allah (watau Banu Isra’ila); lalle ni Manzo ne amintacce a gare ku



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 19

وَأَن لَّا تَعۡلُواْ عَلَى ٱللَّهِۖ إِنِّيٓ ءَاتِيكُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

“Kuma kada ku yi wa Allah girman kai; lalle ni zan kawo muku hujjoji mabayyana



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 20

وَإِنِّي عُذۡتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُمۡ أَن تَرۡجُمُونِ

“Kuma lalle ni ina neman tsari na Ubangijina kuma Ubangijinku, don kada ku jefe ni



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 21

وَإِن لَّمۡ تُؤۡمِنُواْ لِي فَٱعۡتَزِلُونِ

“Idan kuma ba ku yi imani da ni ba sai ku qyale ni.”



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 22

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوۡمٞ مُّجۡرِمُونَ

Sai ya roqi Ubangijinsa cewa: “Lalle waxannan mutane ne masu manyan laifuka.”



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 23

فَأَسۡرِ بِعِبَادِي لَيۡلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Sai (aka ce masa): “Ka tafi da bayina da daddare, lalle ku za a biyo bayanku



السورة: Suratud Dukhan

الآية : 24

وَٱتۡرُكِ ٱلۡبَحۡرَ رَهۡوًاۖ إِنَّهُمۡ جُندٞ مُّغۡرَقُونَ

“Kuma ka bar kogi a tsaye cak (bayan tsallakewa); lalle su runduna ne da za a nutsar.”