السورة: Suratul Baqara

الآية : 54

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ إِنَّكُمۡ ظَلَمۡتُمۡ أَنفُسَكُم بِٱتِّخَاذِكُمُ ٱلۡعِجۡلَ فَتُوبُوٓاْ إِلَىٰ بَارِئِكُمۡ فَٱقۡتُلُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ عِندَ بَارِئِكُمۡ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma ku tuna lokacin da Musa ya cewa mutanensa: “Ya ku mutanena, lalle ku kun zalunci kawunanku ta hanyar mayar da xan maraqi abin bauta, don haka ku tuba zuwa ga Mahaliccinku, kuma ku kashe kawunanku; wannan shi ne ya fi alheri a gare ku a wajen Mahaliccinku. Lalle shi Mai yawan karvar tuba ne, Mai yawan jin qai.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 55

وَإِذۡ قُلۡتُمۡ يَٰمُوسَىٰ لَن نُّؤۡمِنَ لَكَ حَتَّىٰ نَرَى ٱللَّهَ جَهۡرَةٗ فَأَخَذَتۡكُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَأَنتُمۡ تَنظُرُونَ

Kuma ku tuna lokacin da kuka ce: “Ya Musa ba za mu yi imani da kai ba har sai mun ga Allah a sarari”, sai tsawa ta halaka ku, alhali kuma kuna kallo



السورة: Suratul Baqara

الآية : 56

ثُمَّ بَعَثۡنَٰكُم مِّنۢ بَعۡدِ مَوۡتِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Sannan sai Muka tashe ku bayan mutuwarku, don ku yi godiya



السورة: Suratul Baqara

الآية : 57

وَظَلَّلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡغَمَامَ وَأَنزَلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَنَّ وَٱلسَّلۡوَىٰۖ كُلُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا رَزَقۡنَٰكُمۡۚ وَمَا ظَلَمُونَا وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Kuma Muka yi muku inuwa da girgije, kuma Muka saukar muku da mannu da (soyayyun) tsuntsayen salwa, ku ci daga daxaxan abin da Muka arzuta ku da shi; kuma ba su zalince Mu ba, sai dai kawunansu kaxai suke zalunta



السورة: Suratul Baqara

الآية : 58

وَإِذۡ قُلۡنَا ٱدۡخُلُواْ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةَ فَكُلُواْ مِنۡهَا حَيۡثُ شِئۡتُمۡ رَغَدٗا وَٱدۡخُلُواْ ٱلۡبَابَ سُجَّدٗا وَقُولُواْ حِطَّةٞ نَّغۡفِرۡ لَكُمۡ خَطَٰيَٰكُمۡۚ وَسَنَزِيدُ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka ce: “Ku shiga wannan alqaryar ku ci daga (kayan marmarinta ta) inda kuka ga dama cikin yalwa, kuma ku shiga qofar garin a duqe, kuma ku ce: “(Allah Ka) kankare mana laifuffukanmu”, za Mu gafarta muku laifuffukanku. Kuma za Mu qara wa masu kyautatawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 59

فَبَدَّلَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ قَوۡلًا غَيۡرَ ٱلَّذِي قِيلَ لَهُمۡ فَأَنزَلۡنَا عَلَى ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

Sai waxanda suka yi zalunci suka canza maganar da aka faxa musu, sai Muka saukar da wata azaba daga sama a kan waxanda suka yi zalunci saboda abin da suke aikatawa na fasiqanci



السورة: Suratul Baqara

الآية : 60

۞وَإِذِ ٱسۡتَسۡقَىٰ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ فَقُلۡنَا ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡحَجَرَۖ فَٱنفَجَرَتۡ مِنۡهُ ٱثۡنَتَا عَشۡرَةَ عَيۡنٗاۖ قَدۡ عَلِمَ كُلُّ أُنَاسٖ مَّشۡرَبَهُمۡۖ كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ مِن رِّزۡقِ ٱللَّهِ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Musa ya roqa wa mutanensa ruwan sha, sai Muka ce: “Ka bugi dutse da sandarka”, sai idanuwan marmaron ruwa goma sha biyu suka vuvvugo daga cikinsa. Haqiqa kowaxanne mutane sun san mashayarsu. (Muka ce): “Ku ci kuma ku sha daga arzikin Allah, kuma kada ku yaxa varna a bayan qasa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 61

وَإِذۡ قُلۡتُمۡ يَٰمُوسَىٰ لَن نَّصۡبِرَ عَلَىٰ طَعَامٖ وَٰحِدٖ فَٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُخۡرِجۡ لَنَا مِمَّا تُنۢبِتُ ٱلۡأَرۡضُ مِنۢ بَقۡلِهَا وَقِثَّآئِهَا وَفُومِهَا وَعَدَسِهَا وَبَصَلِهَاۖ قَالَ أَتَسۡتَبۡدِلُونَ ٱلَّذِي هُوَ أَدۡنَىٰ بِٱلَّذِي هُوَ خَيۡرٌۚ ٱهۡبِطُواْ مِصۡرٗا فَإِنَّ لَكُم مَّا سَأَلۡتُمۡۗ وَضُرِبَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلذِّلَّةُ وَٱلۡمَسۡكَنَةُ وَبَآءُو بِغَضَبٖ مِّنَ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ كَانُواْ يَكۡفُرُونَ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَيَقۡتُلُونَ ٱلنَّبِيِّـۧنَ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّۚ ذَٰلِكَ بِمَا عَصَواْ وَّكَانُواْ يَعۡتَدُونَ

Kuma ku tuna lokacin da kuka ce: “Ya Musa, ba za mu iya haquri a kan abinci iri xaya ba, don haka ka roqa mana Ubangijinka Ya fitar mana (wani abincin) daga abin da qasa take tsirarwa, daga mabunqusanta da gurjinta da alkamarta da wakenta da albasarta.” Sai ya ce, “Yanzu kwa nemi musanya qasqantaccen abu da wanda yake shi ne mafifici? To ku sauka kowane gari, domin za ku samu abin da kuka roqa (a cikinsa).” Don haka sai aka sanya musu qasqanci da talauci, kuma suka koma da fushin Allah. Hakan ya faru gare su ne saboda sun kasance suna kafirce wa ayoyin Allah, kuma suna kashe annabawa ba tare da wani haqqi ba. Hakan ya faru saboda savon da suka yi da kuma ta’addancin da suka riqa yi



السورة: Suratul Baqara

الآية : 62

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱلَّذِينَ هَادُواْ وَٱلنَّصَٰرَىٰ وَٱلصَّـٰبِـِٔينَ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا فَلَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Lalle waxanda suka yi imani da Yahudawa da Nasara da Sabi’awa[1], duk wanda ya yi imani da Allah da ranar Lahira kuma ya yi aiki na qwarai, to suna da ladansu a wurin Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba


1- Waxanda suka yi imani, su ne al’ummar Annabi Muhammadu (). Yahudawa, ana nufin mabiya Annabi Musa () kafin a shafe addininsa, ko kafin su gurvata shi. Nasara, ana nufin mabiya Annabi Isa () kafin a shafe addininsa ko kafin su gurvata shi. Sabi’awa, wasu qungiyoyi ne, daga cikinsu akwai masu aqidar kaxaita Allah da haramta duk wata alfasha da zalunci, duk da kasancewarsu ba bisa wani addini suke ba, to amma ba sa aikata shirka.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 63

وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَكُمۡ وَرَفَعۡنَا فَوۡقَكُمُ ٱلطُّورَ خُذُواْ مَآ ءَاتَيۡنَٰكُم بِقُوَّةٖ وَٱذۡكُرُواْ مَا فِيهِ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka xauki alqawari mai qarfi daga gare ku, kuma Muka xaga dusten Xuri a kanku (Muka ce): “Ku karvi abin da Muka ba ku da qarfi (Attaura), kuma ku tuna abin da yake cikinsa, don ku yi taqawa.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 64

ثُمَّ تَوَلَّيۡتُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَۖ فَلَوۡلَا فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ وَرَحۡمَتُهُۥ لَكُنتُم مِّنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Sannan bayan haka sai kuka juya da baya, to ba domin falalar Allah da rahamarsa a gare ku ba, lalle da kun kasance daga cikin asararru



السورة: Suratul Baqara

الآية : 65

وَلَقَدۡ عَلِمۡتُمُ ٱلَّذِينَ ٱعۡتَدَوۡاْ مِنكُمۡ فِي ٱلسَّبۡتِ فَقُلۡنَا لَهُمۡ كُونُواْ قِرَدَةً خَٰسِـِٔينَ

Kuma haqiqa kun san waxanda suka yi shisshigi daga cikinku game da ranar Assabar, sai Muka ce da su: “Ku zama birrai kuna qasqantattu.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 66

فَجَعَلۡنَٰهَا نَكَٰلٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهَا وَمَا خَلۡفَهَا وَمَوۡعِظَةٗ لِّلۡمُتَّقِينَ

Sai Muka sanya ta (wannan uqubar) ta zama izina ga (al’ummomin) da suke zamanin faruwarta da kuma (garuruwan) da suke daura da su, kuma don ta zama wa’azi ga masu taqawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 67

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦٓ إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُكُمۡ أَن تَذۡبَحُواْ بَقَرَةٗۖ قَالُوٓاْ أَتَتَّخِذُنَا هُزُوٗاۖ قَالَ أَعُوذُ بِٱللَّهِ أَنۡ أَكُونَ مِنَ ٱلۡجَٰهِلِينَ

Kuma ku tuna lokacin da Musa ya ce wa mutanensa: “Allah Yana umartar ku da ku yanka saniya”, sai suka ce: “Yanzu ka riqa yi mana izgili?” Sai ya ce: “Ina neman Allah Ya kiyaye ni da in zama cikin jahilai!”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 68

قَالُواْ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا هِيَۚ قَالَ إِنَّهُۥ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٞ لَّا فَارِضٞ وَلَا بِكۡرٌ عَوَانُۢ بَيۡنَ ذَٰلِكَۖ فَٱفۡعَلُواْ مَا تُؤۡمَرُونَ

Sai suka ce: “Ka roqa mana Ubangijinka Ya yi mana bayanin yaya take?” Sai ya ce: “Lalle Shi Yana cewa, lalle ita saniya ce, ba tsohuwa ba kuma ba budurwa ba, tana tsakatsakin haka.” Don haka ku aikata abin da ake umartar ku



السورة: Suratul Baqara

الآية : 69

قَالُواْ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا لَوۡنُهَاۚ قَالَ إِنَّهُۥ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٞ صَفۡرَآءُ فَاقِعٞ لَّوۡنُهَا تَسُرُّ ٱلنَّـٰظِرِينَ

Sai suka ce: “Ka roqa mana Ubangijinka Ya bayyana mana mene ne launinta?” Sai ya ce, “Lalle Shi Yana cewa, lalle ita saniya ce mai launin fatsi-fatsi mai tsananin cizawa, tana faranta wa masu kallon ta rai.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 70

قَالُواْ ٱدۡعُ لَنَا رَبَّكَ يُبَيِّن لَّنَا مَا هِيَ إِنَّ ٱلۡبَقَرَ تَشَٰبَهَ عَلَيۡنَا وَإِنَّآ إِن شَآءَ ٱللَّهُ لَمُهۡتَدُونَ

Sai suka ce: “Ka roqa mana Ubangijinka Ya bayyana mana yaya take, lalle shanu sun rikitar da mu, kuma lalle mu, insha Allahu masu shiryuwa ne.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 71

قَالَ إِنَّهُۥ يَقُولُ إِنَّهَا بَقَرَةٞ لَّا ذَلُولٞ تُثِيرُ ٱلۡأَرۡضَ وَلَا تَسۡقِي ٱلۡحَرۡثَ مُسَلَّمَةٞ لَّا شِيَةَ فِيهَاۚ قَالُواْ ٱلۡـَٰٔنَ جِئۡتَ بِٱلۡحَقِّۚ فَذَبَحُوهَا وَمَا كَادُواْ يَفۡعَلُونَ

Ya ce: “Lalle Shi Yana cewa, ita saniya ce wadda ba horarriya ba ce da take noma kasa, kuma ba ta shayar da shuka; lafiyayya ce, babu dabbare-dabbare a jikinta”. Sai suka ce: “Yanzu ne ka zo da gaskiya”. Sai suka yanka ta, kamar dai ba za su aikata ba



السورة: Suratul Baqara

الآية : 72

وَإِذۡ قَتَلۡتُمۡ نَفۡسٗا فَٱدَّـٰرَٰٔتُمۡ فِيهَاۖ وَٱللَّهُ مُخۡرِجٞ مَّا كُنتُمۡ تَكۡتُمُونَ

Kuma ku tuna lokacin da kuka kashe wani mutum, kuma kuka riqa tura wa juna (laifin kisan), Allah kuma Mai bayyanar da abin da kuka kasance kuna voyewa ne



السورة: Suratul Baqara

الآية : 73

فَقُلۡنَا ٱضۡرِبُوهُ بِبَعۡضِهَاۚ كَذَٰلِكَ يُحۡيِ ٱللَّهُ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَيُرِيكُمۡ ءَايَٰتِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Sai Muka ce: “Ku doke shi (mataccen) da wani sashinta (saniyar).”[1] Kamar haka ne Allah Yake raya matattu, Yake kuma nuna muku ayoyinsa don ku hankalta


1- Sai Allah ya sake raya shi, ya tashi ya faxa musu sunan wanda ya kashe shi.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 74

ثُمَّ قَسَتۡ قُلُوبُكُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ فَهِيَ كَٱلۡحِجَارَةِ أَوۡ أَشَدُّ قَسۡوَةٗۚ وَإِنَّ مِنَ ٱلۡحِجَارَةِ لَمَا يَتَفَجَّرُ مِنۡهُ ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ وَإِنَّ مِنۡهَا لَمَا يَشَّقَّقُ فَيَخۡرُجُ مِنۡهُ ٱلۡمَآءُۚ وَإِنَّ مِنۡهَا لَمَا يَهۡبِطُ مِنۡ خَشۡيَةِ ٱللَّهِۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ

Sannan sai zukatanku suka qeqashe bayan haka, suka zama kamar dutse ko ma fiye da dutse qeqashewa. Kuma lalle daga cikin duwatsu akwai waxanda qoramu suke vuvvugowa daga cikinsu; akwai kuma waxanda suke tsattsagewa ruwa ya fito daga cikinsu; akwai kuma waxanda suke faxowa saboda tsoron Allah. Allah ba marafkani ne ba game da abin da kuke aikatawa