السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 12

فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ

A cikinta akwai marmaro mai gudana



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 13

فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ

A cikinta akwai gadaje maxaukaka



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 14

وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ

Da kofuna a ajijjiye



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 15

وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ

Da matasan kai a jejjere



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 16

وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ

Da dardumai a shisshimfixe



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ

Da kuma sama yadda aka xaga ta?



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 19

وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ

Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 20

وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ

Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 21

فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ

To ka yi wa’azi, lalle kai mai wa’azi ne kawai



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 22

لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ

Kai ba mai tilasta su ba ne



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

Sai dai wanda ya ba da baya ya kuma kafirce



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ

To Allah zai azabtar da shi azaba mafi girma[1]


1- Watau wutar Jahannama inda zai dawwama a cikinta har abada.


السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 25

إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ

Lalle zuwa gare Mu ne makomarsu take



السورة: Suratul Ghashiya

الآية : 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم

Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake



السورة: Suratul Fajr

الآية : 1

وَٱلۡفَجۡرِ

Na rantse da alfijir



السورة: Suratul Fajr

الآية : 2

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ

Da kuma darare goma[1]


1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.


السورة: Suratul Fajr

الآية : 3

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ

Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]


1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.


2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.


السورة: Suratul Fajr

الآية : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ

Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)



السورة: Suratul Fajr

الآية : 5

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ

Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?


1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.


السورة: Suratul Fajr

الآية : 6

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?



السورة: Suratul Fajr

الآية : 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ

(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo



السورة: Suratul Fajr

الآية : 8

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)



السورة: Suratul Fajr

الآية : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura



السورة: Suratul Fajr

الآية : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



السورة: Suratul Fajr

الآية : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



السورة: Suratul Fajr

الآية : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



السورة: Suratul Fajr

الآية : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani



السورة: Suratul Fajr

الآية : 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ

Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]


1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.


السورة: Suratul Fajr

الآية : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”