السورة: Suratul Baqara

الآية : 24

فَإِن لَّمۡ تَفۡعَلُواْ وَلَن تَفۡعَلُواْ فَٱتَّقُواْ ٱلنَّارَ ٱلَّتِي وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُۖ أُعِدَّتۡ لِلۡكَٰفِرِينَ

To idan har ba ku aikata hakan ba, kuma ba za ku tava iyawa ba, to ku kiyayi wata wuta wadda mutane ne da duwatsu makamashinta; an kuwa tanade ta domin kafirai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 25

وَبَشِّرِ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أَنَّ لَهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۖ كُلَّمَا رُزِقُواْ مِنۡهَا مِن ثَمَرَةٖ رِّزۡقٗا قَالُواْ هَٰذَا ٱلَّذِي رُزِقۡنَا مِن قَبۡلُۖ وَأُتُواْ بِهِۦ مُتَشَٰبِهٗاۖ وَلَهُمۡ فِيهَآ أَزۡوَٰجٞ مُّطَهَّرَةٞۖ وَهُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Kuma ka yi albishir ga waxanda suka yi imani kuma suka aikata ayyuka na qwarai cewa suna da wasu gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Duk sa’adda aka arzuta su da ’ya’yan itatuwa daga gare su sai su ce: “Wannan shi ne irin abin da aka arzuta mu da shi xazu.” An kawo musu shi yana mai kama da juna, kuma suna da wasu mata tsarkaka a cikinsu, kuma su masu zama ne a cikinsu dindindin



السورة: Suratul Baqara

الآية : 26

۞إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَسۡتَحۡيِۦٓ أَن يَضۡرِبَ مَثَلٗا مَّا بَعُوضَةٗ فَمَا فَوۡقَهَاۚ فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ فَيَعۡلَمُونَ أَنَّهُ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّهِمۡۖ وَأَمَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَيَقُولُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۘ يُضِلُّ بِهِۦ كَثِيرٗا وَيَهۡدِي بِهِۦ كَثِيرٗاۚ وَمَا يُضِلُّ بِهِۦٓ إِلَّا ٱلۡفَٰسِقِينَ

Lalle Allah ba Ya jin kunyar buga kowanne irin misali komai qanqantarsa, sauro da abin da ya fi shi. To amma waxanda suka yi imani suna sanin cewa, lalle shi (wannan misali) gaskiya ne daga Ubangijinsu. Amma waxanda suka kafirta sai su riqa cewa: “Me Allah Yake nufi da wannan misalin?” Yana kuwa vatar da mutane da yawa da shi, kuma Ya shiryar da mutane da yawa da shi, kuma ba kowa Yake vatarwa da shi ba sai fasiqai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 27

ٱلَّذِينَ يَنقُضُونَ عَهۡدَ ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مِيثَٰقِهِۦ وَيَقۡطَعُونَ مَآ أَمَرَ ٱللَّهُ بِهِۦٓ أَن يُوصَلَ وَيُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Waxanda suke warware alqawarin Allah bayan qulla shi, kuma suke yanke abin da Allah Ya yi umarni a sadar da shi, kuma suke varna a bayan qasa. Waxannan su ne cikakkun hasararru



السورة: Suratul Baqara

الآية : 28

كَيۡفَ تَكۡفُرُونَ بِٱللَّهِ وَكُنتُمۡ أَمۡوَٰتٗا فَأَحۡيَٰكُمۡۖ ثُمَّ يُمِيتُكُمۡ ثُمَّ يُحۡيِيكُمۡ ثُمَّ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Ta yaya kuke kafirce wa Allah alhalin a da kun kasance matattu, sannan Ya raya ku, sannan zai kuma mayar da ku matattu sannan Ya raya ku (a karo na biyu) sannan zuwa gare Shi ake mayar da ku?



السورة: Suratul Baqara

الآية : 29

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ لَكُم مَّا فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰٓ إِلَى ٱلسَّمَآءِ فَسَوَّىٰهُنَّ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖۚ وَهُوَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Shi ne wanda Ya halitta muku abin da yake cikin qasa gaba xaya, sannan Ya nufi sama Ya daidaita su sammai bakwai, kuma Shi Masanin komai ne



السورة: Suratul Baqara

الآية : 30

وَإِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي جَاعِلٞ فِي ٱلۡأَرۡضِ خَلِيفَةٗۖ قَالُوٓاْ أَتَجۡعَلُ فِيهَا مَن يُفۡسِدُ فِيهَا وَيَسۡفِكُ ٱلدِّمَآءَ وَنَحۡنُ نُسَبِّحُ بِحَمۡدِكَ وَنُقَدِّسُ لَكَۖ قَالَ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

Kuma ka tuna sa’adda Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle ni zan sanya wani halifa[1] a bayan qasa.” Suka ce: “Yanzu za Ka sanya mata wanda zai yi varna a cikinta kuma ya zubar da jini, alhali ga mu muna tasbihi tare da gode Maka, kuma muna tsarkake Ka?” (Allah) Ya ce: “Ni fa tabbas Na san abin da ku ba ku sani ba.”


1- Halifa, shi ne Annabi Adamu () da zuriyarsa, waxanda za su riqa maye gurbin juna a bayan qasa.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 31

وَعَلَّمَ ءَادَمَ ٱلۡأَسۡمَآءَ كُلَّهَا ثُمَّ عَرَضَهُمۡ عَلَى ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ فَقَالَ أَنۢبِـُٔونِي بِأَسۡمَآءِ هَـٰٓؤُلَآءِ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Kuma sai (Allah) Ya koya wa Adamu dukkan sunaye (na abubuwa) sannan Ya kawo su gaban mala’iku, sai Ya ce: “Ku faxa min sunayen waxannan abubuwan in kun zamanto masu gaskiya.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 32

قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ لَا عِلۡمَ لَنَآ إِلَّا مَا عَلَّمۡتَنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَلِيمُ ٱلۡحَكِيمُ

Sai suka ce: “Tsarki ya tabbata a gare Ka, ba mu da wani ilimi sai wanda Ka sanar da mu. Lalle Kai ne cikakken Masani, Mai hikima.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 33

قَالَ يَـٰٓـَٔادَمُ أَنۢبِئۡهُم بِأَسۡمَآئِهِمۡۖ فَلَمَّآ أَنۢبَأَهُم بِأَسۡمَآئِهِمۡ قَالَ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ غَيۡبَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَأَعۡلَمُ مَا تُبۡدُونَ وَمَا كُنتُمۡ تَكۡتُمُونَ

Ya ce: “Ya Adamu faxa musu sunayensu.” Yayin da ya faxa musu sunayensu, sai (Allah) Ya ce: “Ba Na faxa muku cewa, lalle Ni ne Nake sane da gaibin sammai da qasa ba, kuma Nake sane da abin da kuke bayyanawa da kuma abin da kuke voyewa ba?”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 34

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ وَٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce wa mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu.” Sai duk suka yi sujjada[1], in ban da Iblis, sai shi ya qi, ya kuma yi girman kai, kuma ya tabbata cikin kafirai


1- Mala’iku sun yi wa Adamu () sujjada ne don biyayya ga umarnin Allah. Ba ya halatta a Musulunci wani ya yi wa wani sujjada ba Allah ba.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 35

وَقُلۡنَا يَـٰٓـَٔادَمُ ٱسۡكُنۡ أَنتَ وَزَوۡجُكَ ٱلۡجَنَّةَ وَكُلَا مِنۡهَا رَغَدًا حَيۡثُ شِئۡتُمَا وَلَا تَقۡرَبَا هَٰذِهِ ٱلشَّجَرَةَ فَتَكُونَا مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma Muka ce: “Ya kai Adamu, ka zauna gidan Aljanna kai da matarka, kuma ku ci (kayan marmarinta) cikin yalwa a duk inda kuka ga dama, kada kuma ku kuskura ku kusanci wannan bishiyar, sai ku kasance daga cikin azzalumai.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 36

فَأَزَلَّهُمَا ٱلشَّيۡطَٰنُ عَنۡهَا فَأَخۡرَجَهُمَا مِمَّا كَانَا فِيهِۖ وَقُلۡنَا ٱهۡبِطُواْ بَعۡضُكُمۡ لِبَعۡضٍ عَدُوّٞۖ وَلَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُسۡتَقَرّٞ وَمَتَٰعٌ إِلَىٰ حِينٖ

Sai Shaixan ya zamar da su[1] game da ita (bishiyar), sai ya fitar da su daga ni’imar da suke ciki. Sai Muka ce: “Ku sauko qasa sashinku yana mai gaba da sashi; kuma kuna da mazauni a bayan qasa da wani jin daxi zuwa wani xan lokaci.”


1- Ta hanyar yi musu waswasi, kamar yadda ya zo a Suratul A’raf, aya ta 20, da Xaha, aya ta 120.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 37

فَتَلَقَّىٰٓ ءَادَمُ مِن رَّبِّهِۦ كَلِمَٰتٖ فَتَابَ عَلَيۡهِۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Sai Adamu ya karvi wasu kalmomi daga Ubangijinsa (na neman gafara), sai Ya yafe masa; lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba kuma Mai yawan jin qai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 38

قُلۡنَا ٱهۡبِطُواْ مِنۡهَا جَمِيعٗاۖ فَإِمَّا يَأۡتِيَنَّكُم مِّنِّي هُدٗى فَمَن تَبِعَ هُدَايَ فَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Muka ce: “Dukkanku ku sauko daga cikinta, sannan idan wata shiriyata ta zo muku, to waxanda suka bi shiriyata, babu wani tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



السورة: Suratul Baqara

الآية : 39

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَكَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَآ أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Kuma waxanda suka kafirta suka kuma qaryata ayoyinmu, waxannan su ne ‘yan wuta, su masu dawwama ne a cikinta



السورة: Suratul Baqara

الآية : 40

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَوۡفُواْ بِعَهۡدِيٓ أُوفِ بِعَهۡدِكُمۡ وَإِيَّـٰيَ فَٱرۡهَبُونِ

Ya ku ‘ya’yan Isra’ila, ku tuna ni’imata da Na yi muku, kuma ku cika alqawarina zan cika muku alkawarinku, kuma ku tsorace Ni Ni kaxai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 41

وَءَامِنُواْ بِمَآ أَنزَلۡتُ مُصَدِّقٗا لِّمَا مَعَكُمۡ وَلَا تَكُونُوٓاْ أَوَّلَ كَافِرِۭ بِهِۦۖ وَلَا تَشۡتَرُواْ بِـَٔايَٰتِي ثَمَنٗا قَلِيلٗا وَإِيَّـٰيَ فَٱتَّقُونِ

Kuma ku yi imani da abin da Na saukar yana mai gaskata abin da yake tare da ku (na wahayi), kada kuma ku zama farkon (jinsinku) da zai kafirce masa, kuma kada ku sayar da ayoyina da xan kuxi kaxan, kuma ku kiyaye dokokina



السورة: Suratul Baqara

الآية : 42

وَلَا تَلۡبِسُواْ ٱلۡحَقَّ بِٱلۡبَٰطِلِ وَتَكۡتُمُواْ ٱلۡحَقَّ وَأَنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kada kuma ku gauraya gaskiya da qarya, kuma ku voye gaskiya, alhalin kuna sane



السورة: Suratul Baqara

الآية : 43

وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱرۡكَعُواْ مَعَ ٱلرَّـٰكِعِينَ

Kuma ku tsayar da salla, ku kuma ba da zakka, kuma ku yi ruku’i tare da masu ruku’i



السورة: Suratul Baqara

الآية : 44

۞أَتَأۡمُرُونَ ٱلنَّاسَ بِٱلۡبِرِّ وَتَنسَوۡنَ أَنفُسَكُمۡ وَأَنتُمۡ تَتۡلُونَ ٱلۡكِتَٰبَۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Shin yanzu kwa riqa umartar mutane da ayyukan alheri ku kuma kuna mantawa da kawunanku, alhalin kuna karanta Littafi? Ashe ba za ku hankalta ba?



السورة: Suratul Baqara

الآية : 45

وَٱسۡتَعِينُواْ بِٱلصَّبۡرِ وَٱلصَّلَوٰةِۚ وَإِنَّهَا لَكَبِيرَةٌ إِلَّا عَلَى ٱلۡخَٰشِعِينَ

Kuma ku nemi agaji ta hanyar haquri da kuma salla, kuma lalle ita (salla) babban abu ne sai dai ga masu qasqantar da kai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 46

ٱلَّذِينَ يَظُنُّونَ أَنَّهُم مُّلَٰقُواْ رَبِّهِمۡ وَأَنَّهُمۡ إِلَيۡهِ رَٰجِعُونَ

Waxanda suka tabbatar da cewa, su masu haxuwa ne da Ubangijinsu, kuma su zuwa gare Shi suke komawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 47

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَنِّي فَضَّلۡتُكُمۡ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ya ku ‘ya’yan Isra’ila ku tuna ni’imata da Na yi muku, kuma Ni Na fifita ku a kan sauran mutanen duniya (na zamaninku)



السورة: Suratul Baqara

الآية : 48

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا لَّا تَجۡزِي نَفۡسٌ عَن نَّفۡسٖ شَيۡـٔٗا وَلَا يُقۡبَلُ مِنۡهَا شَفَٰعَةٞ وَلَا يُؤۡخَذُ مِنۡهَا عَدۡلٞ وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Kuma ku kiyayi wata rana da babu wani (mai) rai da zai isar wa da wani (mai) rai komai a cikinta; kuma ba za a karvi wani ceto daga gare shi ba, kuma ba za a karvi wata fansa daga gare shi ba, kuma ba za a taimaka musu ba



السورة: Suratul Baqara

الآية : 49

وَإِذۡ نَجَّيۡنَٰكُم مِّنۡ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ يَسُومُونَكُمۡ سُوٓءَ ٱلۡعَذَابِ يُذَبِّحُونَ أَبۡنَآءَكُمۡ وَيَسۡتَحۡيُونَ نِسَآءَكُمۡۚ وَفِي ذَٰلِكُم بَلَآءٞ مِّن رَّبِّكُمۡ عَظِيمٞ

Kuma ku tuna lokacin da Muka kuvutar da ku daga jama’ar Fir’auna waxanda suke xanxana muku mummunar azaba, suna yanka ‘ya’yanku maza, kuma suna qyale ‘ya’yanku mata. A cikin wannan lamari akwai babbar jarraba daga Ubangijinku



السورة: Suratul Baqara

الآية : 50

وَإِذۡ فَرَقۡنَا بِكُمُ ٱلۡبَحۡرَ فَأَنجَيۡنَٰكُمۡ وَأَغۡرَقۡنَآ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ وَأَنتُمۡ تَنظُرُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka raba muku kogi, sai Muka kuvutar da ku, kuma Muka nutsar da jama’ar Fir’auna, alhalin kuna kallo



السورة: Suratul Baqara

الآية : 51

وَإِذۡ وَٰعَدۡنَا مُوسَىٰٓ أَرۡبَعِينَ لَيۡلَةٗ ثُمَّ ٱتَّخَذۡتُمُ ٱلۡعِجۡلَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَنتُمۡ ظَٰلِمُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka yi wa Musa wa’adin (ganawa da shi) na kwana arba’in, sannan ku kuma kuka kama bautar xan maraqi a bayansa, alhalin kuna masu zaluntar kawunanku



السورة: Suratul Baqara

الآية : 52

ثُمَّ عَفَوۡنَا عَنكُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Sannan sai Muka yi muku afuwa bayan haka, don ku yi godiya



السورة: Suratul Baqara

الآية : 53

وَإِذۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡفُرۡقَانَ لَعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka ba wa Musa Littafin (Attaura) da abin da yake rarrabewa (tsakanin gaskiya da qarya) don ku shiriya