السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 1

وَٱلنَّـٰزِعَٰتِ غَرۡقٗا

Na rantse da (mala’iku) masu cizgar (ran kafiri) mummunar cizga



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 2

وَٱلنَّـٰشِطَٰتِ نَشۡطٗا

Da kuma (mala’iku) masu zare (ran mumini) sassauqar zarewa



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 3

وَٱلسَّـٰبِحَٰتِ سَبۡحٗا

Da kuma (mala’iku) masu ninqaya (a sama don sauko da umarni) ninqaya mai tsananin sauri



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 4

فَٱلسَّـٰبِقَٰتِ سَبۡقٗا

Sannan da (mala’iku) masu matuqar rigegeniya (don zartar da umarnin Allah)



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 5

فَٱلۡمُدَبِّرَٰتِ أَمۡرٗا

Sannan da (mala’iku) masu tsara al’amura



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 6

يَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ

Ranar da mai girgizawa za ta yi girgiza (watau busar qaho ta farko)



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 7

تَتۡبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ

Mai bin ta kuma za ta biyo ta (watau busa ta biyu)



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 8

قُلُوبٞ يَوۡمَئِذٖ وَاجِفَةٌ

Wasu zukata a wannan ranar a tsorace suke



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 9

أَبۡصَٰرُهَا خَٰشِعَةٞ

Idanuwansu kuma a qasqance suke



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 10

يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرۡدُودُونَ فِي ٱلۡحَافِرَةِ

(A duniya) suna cewa: “Yanzu zai yiwu a dawo da mu a raye (bayan mutuwa)?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 11

أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمٗا نَّخِرَةٗ

“Yanzu ko bayan mun zama qasusuwa rududdugaggu?”



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 12

قَالُواْ تِلۡكَ إِذٗا كَرَّةٌ خَاسِرَةٞ

Suka ce: “Idan ko ya yiwu, to wannan komawa ce mai cike da asara.”



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 13

فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ

To lalle ita kawai tsawa ce guda xaya tal!



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 14

فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ

Sai ga su a bayan qasa[1]


1- Watau kowa da kowa ya fito da rai.


السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 15

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

Shin labarin Musa ya zo maka?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 16

إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى

Lokacin da Ubangijinsa Ya kirawo shi a kwari mai tsarki, (watau) Xuwa?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 17

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

(Aka ce da shi): Ka tafi zuwa ga Fir’auna, haqiqa shi ya yi xagawa



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 18

فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

Sai ka ce: “Shin zai yiwu gare ka kuwa ka tsarkaka?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 19

وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ

“In kuma shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka, sai ka ji tsoron Sa?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 20

فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ

Sai ya nuna masa babbar aya[1]


1- Watau ya nuna masa hannun mai haske kamar fitila da kuma sandarsa mai rikixa ta zama macijiya.


السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 21

فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

Sai ya qaryata ya kuma kangare



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 22

ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ

Sannan ya ba da baya yana ta gaggawa



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 23

فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

Sai ya tattara (jama’arsa) sai ya yi shela



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 24

فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Sai ya ce, “Ni ne ubangijinku mafi girma!”



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 25

فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ

Saboda haka Allah Ya kama shi da azabar lahira (watau Jahannama) da ta duniya (watau nutse wa a ruwa)



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 26

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga wanda yake tsoron (Allah)



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 27

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 28

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]


1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.


السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta