السورة: Suratul Qiyama

الآية : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Ina rantsuwa da ranar alqiyama



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 2

وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ

Ina kuma rantsuwa da rai mai yawan zargin (kansa)[1]


1- Watau a kan gazawarsa wajen ayyukan alheri ko a kan aikata laifuka.


السورة: Suratul Qiyama

الآية : 3

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ

Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 4

بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ

E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 5

بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ

Ba haka ba ne, mutum yana nufi ne kawai ya gurvata gabansa (da savon Allah)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 6

يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ

Yana tambaya yaushe ne ranar alqiyamar?



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 7

فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ

To lokacin da gani ya ruxe



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 8

وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ

Wata kuma ya yi duhu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 9

وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ

Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 10

يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ

A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 11

كَلَّا لَا وَزَرَ

Faufau, babu mafaka



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 12

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ

Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 13

يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ

Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 14

بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ

A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 15

وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ

Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 16

لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ

(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 17

إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ

Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 18

فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ

Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 19

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ

Sannan kuma bayaninsa yana kanmu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 20

كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ

Haba, ku dai kawai kuna son duniya ne



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 21

وَتَذَرُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Kuna kuma barin lahira



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 22

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاضِرَةٌ

Wasu fuskokin a wannan rana a ni’imce suke



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 23

إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٞ

Suna masu kallon Ubangijinsu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 24

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذِۭ بَاسِرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a wannan rana a xaxxaure suke



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 25

تَظُنُّ أَن يُفۡعَلَ بِهَا فَاقِرَةٞ

Suna tabbatar da cewa, za a saukar musu da wani bala’i



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 26

كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِيَ

Ku saurara, yayin da rai ya iso a karankarama[1]


1- Watau ya zo qasusuwan qirji a lokacin gargarar mutuwa.


السورة: Suratul Qiyama

الآية : 27

وَقِيلَ مَنۡۜ رَاقٖ

Aka kuma ce: “Wane ne mai tawaida[1]?”


1- Watau masu jinya su riqa tambayar junansu cewa, wane ne zai yi masa ruqya ko zai zamu sauqi?


السورة: Suratul Qiyama

الآية : 28

وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلۡفِرَاقُ

Ya kuma tabbata cewar (wannan) shi ne rabuwarsa (da duniya)



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 29

وَٱلۡتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ

Kuma tsananin bala’i ya haxu



السورة: Suratul Qiyama

الآية : 30

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمَسَاقُ

To zuwa Ubangijinka ne (za a) kora ka a wannan ranar