السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 151

وَلَا تُطِيعُوٓاْ أَمۡرَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

“Kada kuma ku bi umarnin mavarnata



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 152

ٱلَّذِينَ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ

“Waxanda suke varna a bayan qasa, kuma ba sa gyara.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 153

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Lalle kai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 154

مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا فَأۡتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, to ka zo mana da aya idan ka kasance daga masu gaskiya.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 155

قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٞ لَّهَا شِرۡبٞ وَلَكُمۡ شِرۡبُ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ

(Salihu) ya ce: “Wannan taguwa ce[1], tana da (ranar) shanta ku ma kuna da rana sananniya ta shanku


1- Watau a matsayin mu’ujiza ga Annabi Salihu ().


السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 156

وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَظِيمٖ

“Kada kuwa ku shafe ta da mugun abu, sai azabar wani yini mai girma ta kama ku.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 157

فَعَقَرُوهَا فَأَصۡبَحُواْ نَٰدِمِينَ

Sai suka soke ta, sai kuwa suka wayi gari suna masu nadama



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 158

فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai azaba ta kama su. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 159

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 160

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen Luxu sun qaryata manzanni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 161

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Luxu ya ce da su: “Yanzu ba kwa kiyaye dokokin Allah ba?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 162

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 163

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 164

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 165

أَتَأۡتُونَ ٱلذُّكۡرَانَ مِنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Yanzu kwa riqa zaike wa maza daga halittu?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 166

وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمۡ رَبُّكُم مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٌ عَادُونَ

“Kuma ku bar abin da Ubangijinku Ya halitta na matanku dominku? A’a, ku dai mutane ne masu qetare iyaka.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 167

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُخۡرَجِينَ

Suka ce: “Tabbas Luxu idan ba ka bar (faxar abin da kake faxa ba) haqiqa za ka kasance daga korarru (daga garin nan).”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 168

قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلۡقَالِينَ

(Luxu) ya ce: “Lalle ni ina cikin masu qyamar aikin nan naku



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 169

رَبِّ نَجِّنِي وَأَهۡلِي مِمَّا يَعۡمَلُونَ

“Ya Ubangijina, Ka tserar da ni da iyalina daga (sakamakon) abin da suke aikatawa.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 170

فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Sai Muka tserar da shi da iyalinsa gaba xaya



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 171

إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai fa wata tsohuwa (watau matarsa) da ta (kasance tana) cikin hallakakku



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 172

ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka hallaka sauran



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 173

وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلۡمُنذَرِينَ

Muka kuma saukar musu da ruwa na azaba; to ruwan azabar waxanda aka yi wa gargaxi ya munana



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 174

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; yawancinsu kuwa ba su zamanto muminai ba



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 175

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangiijnka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 176

كَذَّبَ أَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen kurmi sun qaryata manzanni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 177

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ شُعَيۡبٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da Shu’aibu ya ce da su: “Yanzu ba kwa kiyaye dokokin (Allah) ba?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 178

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 179

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 180

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai