السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 91

إِنَّمَا يُرِيدُ ٱلشَّيۡطَٰنُ أَن يُوقِعَ بَيۡنَكُمُ ٱلۡعَدَٰوَةَ وَٱلۡبَغۡضَآءَ فِي ٱلۡخَمۡرِ وَٱلۡمَيۡسِرِ وَيَصُدَّكُمۡ عَن ذِكۡرِ ٱللَّهِ وَعَنِ ٱلصَّلَوٰةِۖ فَهَلۡ أَنتُم مُّنتَهُونَ

Abin da kawai Shaixan yake nufi shi ne, ya jefa gaba da qiyayya a tsakankaninku, ta hanyar giya da caca, kuma ya hana muku ambaton Allah da yin salla. Shin ko kun hanu?



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 92

وَأَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُواْ ٱلرَّسُولَ وَٱحۡذَرُواْۚ فَإِن تَوَلَّيۡتُمۡ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَا عَلَىٰ رَسُولِنَا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

Kuma ku bi Allah, kuma ku bi wannan Manzon, kuma ku yi hattara. Idan kuka juya baya, to ku sani abin da kawai yake kan Manzonmu shi ne isar da saqo filla-filla



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 93

لَيۡسَ عَلَى ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ جُنَاحٞ فِيمَا طَعِمُوٓاْ إِذَا مَا ٱتَّقَواْ وَّءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ ثُمَّ ٱتَّقَواْ وَّءَامَنُواْ ثُمَّ ٱتَّقَواْ وَّأَحۡسَنُواْۚ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Babu wani laifi a kan waxanda suka yi imani, kuma suka yi aiki nagari cikin abin da suka tava sha (na giya a baya), in dai sun yi taqawa, kuma sun yi imani, kuma sun aikata aiki nagari, sannan suka yi taqawa da imani, sannan suka yi taqawa kuma suka kyautata. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 94

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَيَبۡلُوَنَّكُمُ ٱللَّهُ بِشَيۡءٖ مِّنَ ٱلصَّيۡدِ تَنَالُهُۥٓ أَيۡدِيكُمۡ وَرِمَاحُكُمۡ لِيَعۡلَمَ ٱللَّهُ مَن يَخَافُهُۥ بِٱلۡغَيۡبِۚ فَمَنِ ٱعۡتَدَىٰ بَعۡدَ ذَٰلِكَ فَلَهُۥ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, lalle Allah zai jarrabe ku da wani abu na farauta, wanda hannayenku da masunku za su kai gare shi, don Allah Ya bayyana wanda yake jin tsoron Sa alhalin bai gan Shi ba. Don haka duk wanda ya qetare iyaka bayan haka, to lalle yana da azaba mai raxaxi



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 95

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَقۡتُلُواْ ٱلصَّيۡدَ وَأَنتُمۡ حُرُمٞۚ وَمَن قَتَلَهُۥ مِنكُم مُّتَعَمِّدٗا فَجَزَآءٞ مِّثۡلُ مَا قَتَلَ مِنَ ٱلنَّعَمِ يَحۡكُمُ بِهِۦ ذَوَا عَدۡلٖ مِّنكُمۡ هَدۡيَۢا بَٰلِغَ ٱلۡكَعۡبَةِ أَوۡ كَفَّـٰرَةٞ طَعَامُ مَسَٰكِينَ أَوۡ عَدۡلُ ذَٰلِكَ صِيَامٗا لِّيَذُوقَ وَبَالَ أَمۡرِهِۦۗ عَفَا ٱللَّهُ عَمَّا سَلَفَۚ وَمَنۡ عَادَ فَيَنتَقِمُ ٱللَّهُ مِنۡهُۚ وَٱللَّهُ عَزِيزٞ ذُو ٱنتِقَامٍ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku kashe abin farauta alhali kuna cikin Harami[1]. Duk kuwa wanda ya kashe shi daga cikinku da gangan, to sakamakonsa shi ne (ya bayar) da kwatankwacin abin da ya kashe cikin dabbobin gida; waxanda za su yi hukunci da wannan su ne mutum biyu adalai a cikinku, a matsayin hadaya wadda za ta isa Ka’aba, ko kuma ya yi kaffarar ciyar da miskinai, ko kuma ya yi azumi na kwatankwacin haka, don ya xanxani kuxar lamarinsa. Allah Ya yi afuwa dangane da abin da ya wuce. Duk kuwa wanda ya sake komawa, to Allah zai yi masa uquba. Kuma Allah Mabuwayi ne, Ma’abocin uquba


1- Watau kuna sanye da haramin hajji ko na umara.


السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 96

أُحِلَّ لَكُمۡ صَيۡدُ ٱلۡبَحۡرِ وَطَعَامُهُۥ مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِلسَّيَّارَةِۖ وَحُرِّمَ عَلَيۡكُمۡ صَيۡدُ ٱلۡبَرِّ مَا دُمۡتُمۡ حُرُمٗاۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ ٱلَّذِيٓ إِلَيۡهِ تُحۡشَرُونَ

An halatta muku yin farautar naman ruwa da abincin cikinsa[1], don jin daxi a gare ku da kuma matafiya; amma an haramta muku farautar naman daji matuqar kuna cikin Harami. Kuma ku kiyaye dokokin Allah Wanda zuwa gare Shi za a tattara ku


1- Watau abin da kogi ya yi ambaliyar sa an halatta wa waxanda suke cikin haramin hajji ko umara farautar sa da cin sa.


السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 97

۞جَعَلَ ٱللَّهُ ٱلۡكَعۡبَةَ ٱلۡبَيۡتَ ٱلۡحَرَامَ قِيَٰمٗا لِّلنَّاسِ وَٱلشَّهۡرَ ٱلۡحَرَامَ وَٱلۡهَدۡيَ وَٱلۡقَلَـٰٓئِدَۚ ذَٰلِكَ لِتَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَأَنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٌ

Allah Ya sanya Ka’aba xaki ne mai alfarma, wuri mai matuqar amfani ga mutane, haka watanni masu alfarma, da dabbar hadaya da dabbar hadaya mai rataye. Wannan kuwa don ku sani cewa, lalle Allah Ya san abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa, kuma lalle Allah Masanin komai ne



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 98

ٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ وَأَنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ku sani lalle Allah Mai tsananin uquba ne, kuma lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 99

مَّا عَلَى ٱلرَّسُولِ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُۗ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تُبۡدُونَ وَمَا تَكۡتُمُونَ

Babu abin da yake kan Manzo sai isarwa. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke bayyanawa da abin da kuke voyewa



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 100

قُل لَّا يَسۡتَوِي ٱلۡخَبِيثُ وَٱلطَّيِّبُ وَلَوۡ أَعۡجَبَكَ كَثۡرَةُ ٱلۡخَبِيثِۚ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ يَـٰٓأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ

Ka ce: “Mummuna da kyakkyawa ba za su tava zama daidai ba, ko da kuwa yawan mummunan ya burge ka.” Don haka ku kiyaye dokokin Allah, ya ku ma’abota hankali, don ku sami rabauta



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 101

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَسۡـَٔلُواْ عَنۡ أَشۡيَآءَ إِن تُبۡدَ لَكُمۡ تَسُؤۡكُمۡ وَإِن تَسۡـَٔلُواْ عَنۡهَا حِينَ يُنَزَّلُ ٱلۡقُرۡءَانُ تُبۡدَ لَكُمۡ عَفَا ٱللَّهُ عَنۡهَاۗ وَٱللَّهُ غَفُورٌ حَلِيمٞ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku yi tambaya game da waxansu al’amurra, waxanda idan aka bayyana muku su za su dame ku, idan kuwa kuka riqa tambaya game da su yayin da Alqur’ani yake sauka, za a bayyana muku su; Allah Ya yi rangwame game da su. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai haquri



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 102

قَدۡ سَأَلَهَا قَوۡمٞ مِّن قَبۡلِكُمۡ ثُمَّ أَصۡبَحُواْ بِهَا كَٰفِرِينَ

Haqiqa waxansu mutane gabaninku sun yi irin wannan tambayar, sannan suka wayi gari suna kafirce mata



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 103

مَا جَعَلَ ٱللَّهُ مِنۢ بَحِيرَةٖ وَلَا سَآئِبَةٖ وَلَا وَصِيلَةٖ وَلَا حَامٖ وَلَٰكِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يَفۡتَرُونَ عَلَى ٱللَّهِ ٱلۡكَذِبَۖ وَأَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡقِلُونَ

Allah bai sanya wata dabba bahîra ba ko sá’iba ko wasîla ko hám[1] ba, sai dai waxanda suka kafirta suna qirqirar qarya su jingina wa Allah; kuma yawancinsu ba sa hankalta


1- Bahîra da sá’iba da wasîla da hám duk waxannan dabbobi ne da mushirikan Larabawa suke ‘yanta su ga gumakansu, ba a hawan su, ba a xora musu kaya, ba a cin namansu.


السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 104

وَإِذَا قِيلَ لَهُمۡ تَعَالَوۡاْ إِلَىٰ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ وَإِلَى ٱلرَّسُولِ قَالُواْ حَسۡبُنَا مَا وَجَدۡنَا عَلَيۡهِ ءَابَآءَنَآۚ أَوَلَوۡ كَانَ ءَابَآؤُهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ شَيۡـٔٗا وَلَا يَهۡتَدُونَ

Kuma idan aka ce da su: “Ku taho zuwa ga abin da Allah Ya saukar da kuma zuwa ga Manzo,” sai su ce: “Abin da muka sami iyayenmu a kai ya ishe mu.” Yanzu ko da iyayen nasu sun kasance ba su san komai ba, kuma ba sa shiryuwa?



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 105

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ عَلَيۡكُمۡ أَنفُسَكُمۡۖ لَا يَضُرُّكُم مَّن ضَلَّ إِذَا ٱهۡتَدَيۡتُمۡۚ إِلَى ٱللَّهِ مَرۡجِعُكُمۡ جَمِيعٗا فَيُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi ta kanku; wanda ya vata, ba zai cutar da ku ba idan har ku kun shiryu. Zuwa ga Allah ne makomarku take gaba xaya, sannan kuma zai ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 106

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ شَهَٰدَةُ بَيۡنِكُمۡ إِذَا حَضَرَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ حِينَ ٱلۡوَصِيَّةِ ٱثۡنَانِ ذَوَا عَدۡلٖ مِّنكُمۡ أَوۡ ءَاخَرَانِ مِنۡ غَيۡرِكُمۡ إِنۡ أَنتُمۡ ضَرَبۡتُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَأَصَٰبَتۡكُم مُّصِيبَةُ ٱلۡمَوۡتِۚ تَحۡبِسُونَهُمَا مِنۢ بَعۡدِ ٱلصَّلَوٰةِ فَيُقۡسِمَانِ بِٱللَّهِ إِنِ ٱرۡتَبۡتُمۡ لَا نَشۡتَرِي بِهِۦ ثَمَنٗا وَلَوۡ كَانَ ذَا قُرۡبَىٰ وَلَا نَكۡتُمُ شَهَٰدَةَ ٱللَّهِ إِنَّآ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡأٓثِمِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, shaidar da take tsakaninku idan alamun mutuwa suka zo wa xaya daga cikinku, yayin da ya so ya yi wasiyya, shi ne a samu mutum biyu masu adalci daga cikinku ko kuma waxansu biyu daga wasunku (kafirai), yayin da kuka yi tafiya a bayan qasa, sai musibar mutuwa ta same ku. Za ku tsayar da su (shaidun) biyun ne bayan an kammala salla, sai su rantse da Allah- idan har kun yi shakka game da su-: “Wallahi, ba za mu musanya shi da wani farashi ba, ko da kuwa ya zamo ma’abocin kusanci ne, kuma ba za mu voye shaidar Allah ba, lalle kuwa idan har muka yi haka, tabbas muna cikin masu laifi.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 107

فَإِنۡ عُثِرَ عَلَىٰٓ أَنَّهُمَا ٱسۡتَحَقَّآ إِثۡمٗا فَـَٔاخَرَانِ يَقُومَانِ مَقَامَهُمَا مِنَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَحَقَّ عَلَيۡهِمُ ٱلۡأَوۡلَيَٰنِ فَيُقۡسِمَانِ بِٱللَّهِ لَشَهَٰدَتُنَآ أَحَقُّ مِن شَهَٰدَتِهِمَا وَمَا ٱعۡتَدَيۡنَآ إِنَّآ إِذٗا لَّمِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Amma idan an gano cewa su biyun sun yi laifi, sai a nemi mutum biyu su tsaya su yi shaida a madadin waxancan daga cikin waxanda suka cancanta su ci gadonsa, sai su rantse da Allah: “Wallahi, shaidarmu ta fi shaidarsu, kuma wallahi ba mu qetare iyaka ba, lalle kuwa idan mun yi haka, tabbas da mun zama cikin azzalumai.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 108

ذَٰلِكَ أَدۡنَىٰٓ أَن يَأۡتُواْ بِٱلشَّهَٰدَةِ عَلَىٰ وَجۡهِهَآ أَوۡ يَخَافُوٓاْ أَن تُرَدَّ أَيۡمَٰنُۢ بَعۡدَ أَيۡمَٰنِهِمۡۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱسۡمَعُواْۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡفَٰسِقِينَ

Yin haka shi ne ya fi kusa da su kawo shaida kamar yadda take, ko su ji tsoron a mayar da wannan shaidar bayan rantsuwarsu. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku saurari (umarninsa), kuma Allah ba Ya shiryar da mutanen da suke fasiqai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 109

۞يَوۡمَ يَجۡمَعُ ٱللَّهُ ٱلرُّسُلَ فَيَقُولُ مَاذَآ أُجِبۡتُمۡۖ قَالُواْ لَا عِلۡمَ لَنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ عَلَّـٰمُ ٱلۡغُيُوبِ

(Ka tuna) ranar da Allah zai tara manzanni, sannan Ya ce: “Da me aka ba ku amsa?” sai su ce: “Ba mu da wata masaniya; lalle Kai ne kaxai Masanin abubuwan da suke voye.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 110

إِذۡ قَالَ ٱللَّهُ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ٱذۡكُرۡ نِعۡمَتِي عَلَيۡكَ وَعَلَىٰ وَٰلِدَتِكَ إِذۡ أَيَّدتُّكَ بِرُوحِ ٱلۡقُدُسِ تُكَلِّمُ ٱلنَّاسَ فِي ٱلۡمَهۡدِ وَكَهۡلٗاۖ وَإِذۡ عَلَّمۡتُكَ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَٱلتَّوۡرَىٰةَ وَٱلۡإِنجِيلَۖ وَإِذۡ تَخۡلُقُ مِنَ ٱلطِّينِ كَهَيۡـَٔةِ ٱلطَّيۡرِ بِإِذۡنِي فَتَنفُخُ فِيهَا فَتَكُونُ طَيۡرَۢا بِإِذۡنِيۖ وَتُبۡرِئُ ٱلۡأَكۡمَهَ وَٱلۡأَبۡرَصَ بِإِذۡنِيۖ وَإِذۡ تُخۡرِجُ ٱلۡمَوۡتَىٰ بِإِذۡنِيۖ وَإِذۡ كَفَفۡتُ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ عَنكَ إِذۡ جِئۡتَهُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡهُمۡ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٞ

(Ka tuna) lokacin da Allah zai ce: “Ya kai Isa xan Maryamu, ka tuna ni’imata da Na yi maka kai da mahaifiyarka, yayin da Na qarfafe ka da Ruhi mai tsarki, kana yi wa mutane magana lokacin kana cikin zanin goyo, da kuma lokacin da kake dattijo, kuma ka tuna lokacin da Na koyar da kai rubutu da hikima da Attaura da Linjila. Kuma ka tuna lokacin da kake qirqirar (wani abu) kamar tsuntsu da tavo da izinina, sai ka yi busa a cikinsa, sai ya zamo tsuntsu da izinina; kuma kake warkar da wanda aka haifa da makanta da mai albaras da izinina; kuma ka tuna lokacin da kake fito da matattu (daga cikin qaburburansu) da izinina; kuma ka tuna lokacin da Na kare ka (daga cutar) Bani Isra’ila yayin da ka zo musu da hujjoji bayyanannu, sai waxanda suka kafirta daga cikinsu suka ce: “Ai wannan ba komai ba ne face sihiri mabayyani.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 111

وَإِذۡ أَوۡحَيۡتُ إِلَى ٱلۡحَوَارِيِّـۧنَ أَنۡ ءَامِنُواْ بِي وَبِرَسُولِي قَالُوٓاْ ءَامَنَّا وَٱشۡهَدۡ بِأَنَّنَا مُسۡلِمُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Na yi wahayi zuwa ga Hawariyyawa: “Ku yi imani da Ni da Manzona,” sai suka ce: “Mun yi imani, kuma Ka shaida cewa, mu Musulmai ne.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 112

إِذۡ قَالَ ٱلۡحَوَارِيُّونَ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ هَلۡ يَسۡتَطِيعُ رَبُّكَ أَن يُنَزِّلَ عَلَيۡنَا مَآئِدَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِۖ قَالَ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Lokacin da Hawariyyawa suka ce: “Ya Isa xan Maryamu, shin Ubangijinka Yana iya saukar mana da kavaki daga sama?” Ya ce: “Ku kiyayi Allah, idan har kun kasance muminai.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 113

قَالُواْ نُرِيدُ أَن نَّأۡكُلَ مِنۡهَا وَتَطۡمَئِنَّ قُلُوبُنَا وَنَعۡلَمَ أَن قَدۡ صَدَقۡتَنَا وَنَكُونَ عَلَيۡهَا مِنَ ٱلشَّـٰهِدِينَ

Suka ce: “Mu muna nufin mu ci daga gare shi, kuma zukatanmu su sami nutsuwa, sannan mu haqiqance cewa, lalle ka faxa mana gaskiya, kuma mu zamo masu ba da shaida a kansa.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 114

قَالَ عِيسَى ٱبۡنُ مَرۡيَمَ ٱللَّهُمَّ رَبَّنَآ أَنزِلۡ عَلَيۡنَا مَآئِدَةٗ مِّنَ ٱلسَّمَآءِ تَكُونُ لَنَا عِيدٗا لِّأَوَّلِنَا وَءَاخِرِنَا وَءَايَةٗ مِّنكَۖ وَٱرۡزُقۡنَا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ

Isa xan Maryamu ya ce: “Ya Allah Ubangijinmu, Ka saukar mana da kavaki daga sama, wanda zai zame mana wani Idi, ga na farkonmu da na qarshenmu, kuma ya zamo wata aya daga gare Ka; kuma Ka arzuta mu, lalle Kai ne Fiyayyen masu arzutawa.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 115

قَالَ ٱللَّهُ إِنِّي مُنَزِّلُهَا عَلَيۡكُمۡۖ فَمَن يَكۡفُرۡ بَعۡدُ مِنكُمۡ فَإِنِّيٓ أُعَذِّبُهُۥ عَذَابٗا لَّآ أُعَذِّبُهُۥٓ أَحَدٗا مِّنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Allah Ya ce: “Lalle Ni Mai saukar muku da shi (kavakin) ne; amma duk wanda ya kafirta daga baya cikinku, to lalle Ni zan yi masa wata irin azaba wadda ba zan tava azabtar da wani daga cikin halittu irinta ba.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 116

وَإِذۡ قَالَ ٱللَّهُ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ءَأَنتَ قُلۡتَ لِلنَّاسِ ٱتَّخِذُونِي وَأُمِّيَ إِلَٰهَيۡنِ مِن دُونِ ٱللَّهِۖ قَالَ سُبۡحَٰنَكَ مَا يَكُونُ لِيٓ أَنۡ أَقُولَ مَا لَيۡسَ لِي بِحَقٍّۚ إِن كُنتُ قُلۡتُهُۥ فَقَدۡ عَلِمۡتَهُۥۚ تَعۡلَمُ مَا فِي نَفۡسِي وَلَآ أَعۡلَمُ مَا فِي نَفۡسِكَۚ إِنَّكَ أَنتَ عَلَّـٰمُ ٱلۡغُيُوبِ

Kuma (ka tuna) lokacin da Allah zai ce: “Ya kai Isa xan Maryamu, shin kai ne ka ce da mutane: ‘Ku riqe ni, ni da mahaifiyata a matsayin alloli biyu ban da Allah?’” Sai ya ce: “Tsarki ya tabbata gare Ka, bai dace ba a gare ni in faxi wani abu wanda ba ni da haqqin (faxar sa). Idan har na faxe shi, to haqiqa Ka riga Ka sani, Ka san abin da yake cikin raina, amma ni ban san abin da yake ranka ba. Lalle Kai ne Masanin abubuwan da suke voye



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 117

مَا قُلۡتُ لَهُمۡ إِلَّا مَآ أَمَرۡتَنِي بِهِۦٓ أَنِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ رَبِّي وَرَبَّكُمۡۚ وَكُنتُ عَلَيۡهِمۡ شَهِيدٗا مَّا دُمۡتُ فِيهِمۡۖ فَلَمَّا تَوَفَّيۡتَنِي كُنتَ أَنتَ ٱلرَّقِيبَ عَلَيۡهِمۡۚ وَأَنتَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

“Ban faxa musu komai ba sai abin da Ka umarce ni da shi, cewa: ‘Ku bauta wa Allah Ubangijina, kuma Ubangijinku.’ Kuma na kasance mai sa ido a kansu lokacin da nake cikinsu. Amma yayin da Ka karvi rayuwata, Ka zama Kai ne Mai kula da su. Kuma lalle Kai Mai kula ne a kan komai



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 118

إِن تُعَذِّبۡهُمۡ فَإِنَّهُمۡ عِبَادُكَۖ وَإِن تَغۡفِرۡ لَهُمۡ فَإِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Idan har Ka azabtar da su, haqiqa su bayinka ne; idan kuwa Ka yafe musu, to lalle Kai Mabuwayi ne, Mai hikima.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 119

قَالَ ٱللَّهُ هَٰذَا يَوۡمُ يَنفَعُ ٱلصَّـٰدِقِينَ صِدۡقُهُمۡۚ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ رَّضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Allah zai ce: “Wannan ita ce rana wadda gaskiya za ta amfani masu ita. Suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, za su dawwama a cikinsu har abada. Allah Ya yarda da su, su kuma sun yarda da Shi. Wannan shi ne rabo mai girma.”



السورة: Suratul Ma’ida

الآية : 120

لِلَّهِ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا فِيهِنَّۚ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرُۢ

Mulkin sammai da qasa da abin da yake cikinsu na Allah ne. Kuma Shi Mai iko ne a kan komai