السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 91

سَتَجِدُونَ ءَاخَرِينَ يُرِيدُونَ أَن يَأۡمَنُوكُمۡ وَيَأۡمَنُواْ قَوۡمَهُمۡ كُلَّ مَا رُدُّوٓاْ إِلَى ٱلۡفِتۡنَةِ أُرۡكِسُواْ فِيهَاۚ فَإِن لَّمۡ يَعۡتَزِلُوكُمۡ وَيُلۡقُوٓاْ إِلَيۡكُمُ ٱلسَّلَمَ وَيَكُفُّوٓاْ أَيۡدِيَهُمۡ فَخُذُوهُمۡ وَٱقۡتُلُوهُمۡ حَيۡثُ ثَقِفۡتُمُوهُمۡۚ وَأُوْلَـٰٓئِكُمۡ جَعَلۡنَا لَكُمۡ عَلَيۡهِمۡ سُلۡطَٰنٗا مُّبِينٗا

Za ku sami wasu mutanen suna qoqarin su sami amincewarku, kuma su sami amincewar mutanensu, amma duk sa’adda aka kira su zuwa kafirci sai su auka cikinsa. To idan ba su rabu da ku ba, kuma ba su neme ku da zaman lafiya ba, kuma ba su kame hannayensu ba, to ku kama su, kuma ku kashe su a duk inda kuka same su. Waxannan kuwa Mun sanya muku bayyananniyar hujja a kansu



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 92

وَمَا كَانَ لِمُؤۡمِنٍ أَن يَقۡتُلَ مُؤۡمِنًا إِلَّا خَطَـٔٗاۚ وَمَن قَتَلَ مُؤۡمِنًا خَطَـٔٗا فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖ وَدِيَةٞ مُّسَلَّمَةٌ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَصَّدَّقُواْۚ فَإِن كَانَ مِن قَوۡمٍ عَدُوّٖ لَّكُمۡ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖۖ وَإِن كَانَ مِن قَوۡمِۭ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُم مِّيثَٰقٞ فَدِيَةٞ مُّسَلَّمَةٌ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ وَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖۖ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ شَهۡرَيۡنِ مُتَتَابِعَيۡنِ تَوۡبَةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma bai dace ga mumini ya kashe wani mumini ba, sai bisa kuskure. Wanda ya kashe mumini bisa ga kuskure, to zai ‘yanta bawa ko baiwa mumina da kuma diyya wadda za a miqa wa iyalinsa, sai fa idan sun yafe. Amma idan wanda aka kashe yana cikin mutanen da suke maqiyanku, alhalin kuma shi mumini ne, to za ku ‘yanta bawa ko baiwa mumina; idan kuwa ya kasance yana cikin mutanen da kuke da yarjejeniyar zaman lafiya da su, to za a bayar da diyya wadda za a miqa wa iyalinsa, sannan za ku ‘yanta bawa ko baiwa mumina; wanda kuwa bai sami ikon haka ba, to sai ya yi azumin wata biyu a jere[1] don tuba zuwa ga Allah. Allah kuwa Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima


1- Watau sai dai idan akwai wani uzuri na rashin lafiya, ko na shari’a kamar shigowar Ramadana ko a ranar salla.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 93

وَمَن يَقۡتُلۡ مُؤۡمِنٗا مُّتَعَمِّدٗا فَجَزَآؤُهُۥ جَهَنَّمُ خَٰلِدٗا فِيهَا وَغَضِبَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِ وَلَعَنَهُۥ وَأَعَدَّ لَهُۥ عَذَابًا عَظِيمٗا

Duk kuwa wanda ya kashe mumini da gangan, to sakamakonsa wutar Jahannama ce, yana mai dawwama a cikinta, kuma Allah Ya yi fushi da shi, kuma Ya la’ance shi, kuma Ya yi masa tanadin azaba mai girma



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 94

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِذَا ضَرَبۡتُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَتَبَيَّنُواْ وَلَا تَقُولُواْ لِمَنۡ أَلۡقَىٰٓ إِلَيۡكُمُ ٱلسَّلَٰمَ لَسۡتَ مُؤۡمِنٗا تَبۡتَغُونَ عَرَضَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا فَعِندَ ٱللَّهِ مَغَانِمُ كَثِيرَةٞۚ كَذَٰلِكَ كُنتُم مِّن قَبۡلُ فَمَنَّ ٱللَّهُ عَلَيۡكُمۡ فَتَبَيَّنُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka fita yaqi don xaukaka kalmar Allah, to ku riqa bincike, kuma kada ku ce ma wanda ya yi muku sallama: “Kai ba mumini ba ne,”[1] don kawai kuna neman wani jin daxi na rayuwar duniya, to a wurin Allah ne ganimomi masu yawa suke. Kamar haka ku ma a da kuka kasance[2], sai Allah Ya yi muku baiwa, don haka ku riqa bincike. Lalle Allah Ya kasance Mai cikakken sanin abin da kuke aikatawa ne


1- Watau su xauke shi kawai a matsayin wanda yake qoqarin kare kansa amma ba da gaske yake ba.


2- Watau suna voye imaninsu daga mutanensu mushirikai har Allah ya ba su ikon bayyana addininsu.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 95

لَّا يَسۡتَوِي ٱلۡقَٰعِدُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ غَيۡرُ أُوْلِي ٱلضَّرَرِ وَٱلۡمُجَٰهِدُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۚ فَضَّلَ ٱللَّهُ ٱلۡمُجَٰهِدِينَ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡ عَلَى ٱلۡقَٰعِدِينَ دَرَجَةٗۚ وَكُلّٗا وَعَدَ ٱللَّهُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ وَفَضَّلَ ٱللَّهُ ٱلۡمُجَٰهِدِينَ عَلَى ٱلۡقَٰعِدِينَ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Waxanda suka zauna a gida daga cikin muminai ba su fita yaqi ba, in dai ba masu larura ba, ba za su yi daidai da masu jihadi don xaukaka kalmar Allah da dukiyoyinsu da kawunansu ba. Allah Ya fifita darajar masu jihadi da dukiyoyinsu da kawunansu a kan waxanda suka zauna a gida. Kuma dukkansu Allah Ya yi masu alqawarin Aljanna. Kuma Allah Ya fifita masu jihadi a kan waxanda suka zauna a gida, da lada mai girma



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 96

دَرَجَٰتٖ مِّنۡهُ وَمَغۡفِرَةٗ وَرَحۡمَةٗۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمًا

Wasu darajoji masu yawa daga gare Shi da gafara da kuma jin qai. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 97

إِنَّ ٱلَّذِينَ تَوَفَّىٰهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ ظَالِمِيٓ أَنفُسِهِمۡ قَالُواْ فِيمَ كُنتُمۡۖ قَالُواْ كُنَّا مُسۡتَضۡعَفِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ قَالُوٓاْ أَلَمۡ تَكُنۡ أَرۡضُ ٱللَّهِ وَٰسِعَةٗ فَتُهَاجِرُواْ فِيهَاۚ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ وَسَآءَتۡ مَصِيرًا

Lalle waxanda mala’iku suke karvar rayukansu suna masu zaluntar kawunansu[1], (mala’ikun) za su ce (da su): “Cikin wane hali kuka kasance?” Sai su ce: “Mu mun kasance masu rauni a bayan qasa.” Sai su ce: “Ashe qasar Allah ba mai yalwa ba ce, ta yadda za ku sami damar yin hijira a cikinta?” To waxannan, makomarsu ita ce wutar Jahannama, kuma wannan makoma ta munana


1- Watau sun qi yin hijira zuwa cikin ‘yan’uwansu Musulmi, sun ci gaba da zama a qasar kafirci, tare da cewa suna da ikon yin hijirar.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 98

إِلَّا ٱلۡمُسۡتَضۡعَفِينَ مِنَ ٱلرِّجَالِ وَٱلنِّسَآءِ وَٱلۡوِلۡدَٰنِ لَا يَسۡتَطِيعُونَ حِيلَةٗ وَلَا يَهۡتَدُونَ سَبِيلٗا

Sai dai waxanda suke raunana cikin maza da mata da yara qanana waxanda ba su da wata dabara, kuma ba za su gane wata hanya (ta hijira) ba[1]


1- Watau ba su da wata hanya da za su kuvutar da kansu daga hannun mushirikai.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 99

فَأُوْلَـٰٓئِكَ عَسَى ٱللَّهُ أَن يَعۡفُوَ عَنۡهُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَفُوًّا غَفُورٗا

To waxannan mai yiwuwa ne Allah Ya yi musu afuwa, Allah kuma Ya kasance Mai afuwa ne, Mai yawan gafara



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 100

۞وَمَن يُهَاجِرۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ يَجِدۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُرَٰغَمٗا كَثِيرٗا وَسَعَةٗۚ وَمَن يَخۡرُجۡ مِنۢ بَيۡتِهِۦ مُهَاجِرًا إِلَى ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ ثُمَّ يُدۡرِكۡهُ ٱلۡمَوۡتُ فَقَدۡ وَقَعَ أَجۡرُهُۥ عَلَى ٱللَّهِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma duk wanda ya yi hijira saboda Allah, zai samu wuraren hijira masu yawa da yalwa a bayan qasa. Kuma duk wanda ya fita daga gidansa, yana mai hijira zuwa ga Allah da Manzonsa, sannan mutuwa ta riske shi, to haqiqa ladansa ya tabbata a wajen Allah. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 101

وَإِذَا ضَرَبۡتُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَلَيۡسَ عَلَيۡكُمۡ جُنَاحٌ أَن تَقۡصُرُواْ مِنَ ٱلصَّلَوٰةِ إِنۡ خِفۡتُمۡ أَن يَفۡتِنَكُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْۚ إِنَّ ٱلۡكَٰفِرِينَ كَانُواْ لَكُمۡ عَدُوّٗا مُّبِينٗا

Kuma idan kun yi tafiya a bayan qasa, to babu laifi a kanku ku yi sallar qasaru[1], in kun ji tsoron kafirai su fitine ku[2]. Lalle kafirai sun kasance maqiya ne, masu bayyana qiyayya a gare ku


1- Watau ku taqaita salloli masu raka’a huxu zuwa raka’a biyu.


2- Ko da yake an ambaci halin tsoron fitinar kafirai, to amma wannan ba sharaxi ba ne, duk wanda yake a halin tafiya yana iya yin sallar qasaru.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 102

وَإِذَا كُنتَ فِيهِمۡ فَأَقَمۡتَ لَهُمُ ٱلصَّلَوٰةَ فَلۡتَقُمۡ طَآئِفَةٞ مِّنۡهُم مَّعَكَ وَلۡيَأۡخُذُوٓاْ أَسۡلِحَتَهُمۡۖ فَإِذَا سَجَدُواْ فَلۡيَكُونُواْ مِن وَرَآئِكُمۡ وَلۡتَأۡتِ طَآئِفَةٌ أُخۡرَىٰ لَمۡ يُصَلُّواْ فَلۡيُصَلُّواْ مَعَكَ وَلۡيَأۡخُذُواْ حِذۡرَهُمۡ وَأَسۡلِحَتَهُمۡۗ وَدَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَوۡ تَغۡفُلُونَ عَنۡ أَسۡلِحَتِكُمۡ وَأَمۡتِعَتِكُمۡ فَيَمِيلُونَ عَلَيۡكُم مَّيۡلَةٗ وَٰحِدَةٗۚ وَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ إِن كَانَ بِكُمۡ أَذٗى مِّن مَّطَرٍ أَوۡ كُنتُم مَّرۡضَىٰٓ أَن تَضَعُوٓاْ أَسۡلِحَتَكُمۡۖ وَخُذُواْ حِذۡرَكُمۡۗ إِنَّ ٱللَّهَ أَعَدَّ لِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابٗا مُّهِينٗا

Kuma idan ka kasance a cikinsu, sai ka yi musu limancin salla[1], to sai wata qungiya su tsaya tare da kai, kuma su riqe makamansu, to yayin da suka yi sujada (wato salla), sai su koma bayanku, sai xaya qungiyar wadda ba su yi salla ba, su zo su yi salla tare da kai, kuma su ma su yi taka-tsantsan, su kuma riqe makamansu. Kafirai kuwa suna burin ina ma za ku gafala ku ajiye makamanku da kayayyakin guzurinku, sai su far muku gaba xaya. Kuma idan akwai wata cuta tare da ku saboda ruwan sama ko kun kasance marasa lafiya, to babu laifi a gare ku ku ajiye makamanku, amma fa ku yi taka-tsantsan. Lalle Allah Ya yi wa kafirai tanadin wata azaba mai wulaqantarwa


1- Watau yadda zai yi wa sahabbansa limancin salla a lokacin da ake cikin halin yaqi.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 103

فَإِذَا قَضَيۡتُمُ ٱلصَّلَوٰةَ فَٱذۡكُرُواْ ٱللَّهَ قِيَٰمٗا وَقُعُودٗا وَعَلَىٰ جُنُوبِكُمۡۚ فَإِذَا ٱطۡمَأۡنَنتُمۡ فَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَۚ إِنَّ ٱلصَّلَوٰةَ كَانَتۡ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ كِتَٰبٗا مَّوۡقُوتٗا

To idan kun kammala salla, to sai ku ambaci Allah a tsaye ko a zaune ko kuma a kwance. To idan kuka samu nutsuwa sai ku tsayar da salla (a yadda take). Lalle salla ta kasance wata farilla ce mai qayyadajjen lokaci a kan muminai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 104

وَلَا تَهِنُواْ فِي ٱبۡتِغَآءِ ٱلۡقَوۡمِۖ إِن تَكُونُواْ تَأۡلَمُونَ فَإِنَّهُمۡ يَأۡلَمُونَ كَمَا تَأۡلَمُونَۖ وَتَرۡجُونَ مِنَ ٱللَّهِ مَا لَا يَرۡجُونَۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمًا

Kuma kada ku yi rauni wajen neman mutanen; in kun kasance kuna jin raxaxi, to ai su ma (kafirai) suna jin raxaxi kamar yadda kuke jin raxaxi; kuma kuna fatan wani lada a wurin Allah, wanda su ba sa fatan irinsa. Allah kuwa Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai yawan hikima



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 105

إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ لِتَحۡكُمَ بَيۡنَ ٱلنَّاسِ بِمَآ أَرَىٰكَ ٱللَّهُۚ وَلَا تَكُن لِّلۡخَآئِنِينَ خَصِيمٗا

Lalle Mu Mun saukar maka da Littafi da gaskiya domin ka yi hukunci a tsakanin mutane da abin da Allah Ya sanar da kai, kuma kada ka zamo mai ba da kariya ga maha’inta



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 106

وَٱسۡتَغۡفِرِ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma ka roqi gafarar Allah, lalle Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 107

وَلَا تُجَٰدِلۡ عَنِ ٱلَّذِينَ يَخۡتَانُونَ أَنفُسَهُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُحِبُّ مَن كَانَ خَوَّانًا أَثِيمٗا

Kuma kada ka kare waxanda suke ha’intar kawunansu. Lalle Allah ba Ya son duk wanda ya kasance mai yawan ha’inci ne, mai yawan savo



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 108

يَسۡتَخۡفُونَ مِنَ ٱلنَّاسِ وَلَا يَسۡتَخۡفُونَ مِنَ ٱللَّهِ وَهُوَ مَعَهُمۡ إِذۡ يُبَيِّتُونَ مَا لَا يَرۡضَىٰ مِنَ ٱلۡقَوۡلِۚ وَكَانَ ٱللَّهُ بِمَا يَعۡمَلُونَ مُحِيطًا

Suna voye wa mutane (laifinsu), amma ba sa voye wa Allah, alhali kuwa Yana tare da su yayin da suke kwana suna qulle-qullen maganar da bai yarda da ita ba. Kuma lalle Allah Ya kasance Mai kewayewa ne ga abin da suke aikatawa



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 109

هَـٰٓأَنتُمۡ هَـٰٓؤُلَآءِ جَٰدَلۡتُمۡ عَنۡهُمۡ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا فَمَن يُجَٰدِلُ ٱللَّهَ عَنۡهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ أَم مَّن يَكُونُ عَلَيۡهِمۡ وَكِيلٗا

Sai ga shi ku waxannan kun ba su kariya a rayuwar duniya, to wane ne zai ba su kariya a gaban Allah a ranar alqiyama, ko kuwa wane ne zai zama wakilinsu?



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 110

وَمَن يَعۡمَلۡ سُوٓءًا أَوۡ يَظۡلِمۡ نَفۡسَهُۥ ثُمَّ يَسۡتَغۡفِرِ ٱللَّهَ يَجِدِ ٱللَّهَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma duk wanda ya aikata mummunan aiki ko ya zalunci kansa, sannan ya nemi gafarar Allah, to zai sami Allah Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 111

وَمَن يَكۡسِبۡ إِثۡمٗا فَإِنَّمَا يَكۡسِبُهُۥ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma duk wanda ya aikata wani laifi, to kansa ya yi wa. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 112

وَمَن يَكۡسِبۡ خَطِيٓـَٔةً أَوۡ إِثۡمٗا ثُمَّ يَرۡمِ بِهِۦ بَرِيٓـٔٗا فَقَدِ ٱحۡتَمَلَ بُهۡتَٰنٗا وَإِثۡمٗا مُّبِينٗا

Kuma duk wanda ya aikata wani qaramin laifi, ko wani babban zunubi, sannan ya xora shi a kan wanda bai ji ba bai gani ba, to haqiqa ya xaukar wa kansa babban laifin qage da kuma wani zunubi mabayyani



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 113

وَلَوۡلَا فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكَ وَرَحۡمَتُهُۥ لَهَمَّت طَّآئِفَةٞ مِّنۡهُمۡ أَن يُضِلُّوكَ وَمَا يُضِلُّونَ إِلَّآ أَنفُسَهُمۡۖ وَمَا يَضُرُّونَكَ مِن شَيۡءٖۚ وَأَنزَلَ ٱللَّهُ عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَعَلَّمَكَ مَا لَمۡ تَكُن تَعۡلَمُۚ وَكَانَ فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكَ عَظِيمٗا

Ba don falalar Allah da rahamarsa a kanka ba kuwa, lalle da waxansu jama’a daga cikinsu sun yi niyyar su vatar da kai, ba kuwa kowa za su iya vatarwa ba sai dai kawunansu; kuma ba za su cuce ka da komai ba. Kuma Allah Ya saukar maka da Littafi da hikima, kuma Ya sanar da kai abin da a da ba ka sani ba. Kuma falalar Allah mai girma ce gare ka



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 114

۞لَّا خَيۡرَ فِي كَثِيرٖ مِّن نَّجۡوَىٰهُمۡ إِلَّا مَنۡ أَمَرَ بِصَدَقَةٍ أَوۡ مَعۡرُوفٍ أَوۡ إِصۡلَٰحِۭ بَيۡنَ ٱلنَّاسِۚ وَمَن يَفۡعَلۡ ذَٰلِكَ ٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِ ٱللَّهِ فَسَوۡفَ نُؤۡتِيهِ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Babu wani alheri a cikin yawancin ganawarsu, sai fa wanda ya yi umarni da yin sadaka, ko wani aiki nagari ko kuma sulhuntawa tsakanin mutane. Wanda ya aikata haka don neman yardar Allah, to za Mu ba shi lada mai girma



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 115

وَمَن يُشَاقِقِ ٱلرَّسُولَ مِنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُ ٱلۡهُدَىٰ وَيَتَّبِعۡ غَيۡرَ سَبِيلِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ نُوَلِّهِۦ مَا تَوَلَّىٰ وَنُصۡلِهِۦ جَهَنَّمَۖ وَسَآءَتۡ مَصِيرًا

Kuma duk wanda yake sava wa wannan Manzo bayan shiriya ta bayyana a gare shi, yake kuma bin tafarkin da ba na muminai ba, to za Mu bar shi da abin da ya xaukar wa kansa, sannan Mu shigar da shi wutar Jahannama; makoma kuwa ta munana



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 116

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَغۡفِرُ أَن يُشۡرَكَ بِهِۦ وَيَغۡفِرُ مَا دُونَ ذَٰلِكَ لِمَن يَشَآءُۚ وَمَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدۡ ضَلَّ ضَلَٰلَۢا بَعِيدًا

Lalle Allah ba Ya gafartawa a yi masa shirka, Yana kuwa gafarta abin da bai kai shirka ba ga wanda Ya ga dama. Duk wanda ya yi wa Allah shirka, to haqiqa ya vata manisanciyar vata



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 117

إِن يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦٓ إِلَّآ إِنَٰثٗا وَإِن يَدۡعُونَ إِلَّا شَيۡطَٰنٗا مَّرِيدٗا

Ba waxanda suke bauta wa, baya ga Allah, sai wasu gumaka masu sunan mata, kuma babu wanda suke bauta wa sai Shaixan mai taurin kai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 118

لَّعَنَهُ ٱللَّهُۘ وَقَالَ لَأَتَّخِذَنَّ مِنۡ عِبَادِكَ نَصِيبٗا مَّفۡرُوضٗا

Allah Ya la’ance shi. Sai kuma ya ce: “Tabbas sai na samu wani kaso qayyadajje daga bayinka



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 119

وَلَأُضِلَّنَّهُمۡ وَلَأُمَنِّيَنَّهُمۡ وَلَأٓمُرَنَّهُمۡ فَلَيُبَتِّكُنَّ ءَاذَانَ ٱلۡأَنۡعَٰمِ وَلَأٓمُرَنَّهُمۡ فَلَيُغَيِّرُنَّ خَلۡقَ ٱللَّهِۚ وَمَن يَتَّخِذِ ٱلشَّيۡطَٰنَ وَلِيّٗا مِّن دُونِ ٱللَّهِ فَقَدۡ خَسِرَ خُسۡرَانٗا مُّبِينٗا

“Kuma lalle sai na vatar da su, kuma lalle sai na sa musu dogon buri, kuma lalle zan umarce su, sai sun riqa gutsuttsure kunnuwan dabbobin gida, kuma lalle zan umarce su, sai sun canja halittar Allah.” Duk wanda kuwa ya riqi Shaixan a matsayin masoyi ba Allah ba, to haqiqa ya yi hasara bayyananniyar hasara



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 120

يَعِدُهُمۡ وَيُمَنِّيهِمۡۖ وَمَا يَعِدُهُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ إِلَّا غُرُورًا

Yana yi musu alqawari kuma yana sa musu dogon buri; kuma babu abin da Shaixan yake yi musu alqawari da shi sai ruxi kawai