السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 91

وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِلۡغَاوِينَ

Kuma aka bayyanar da (wutar) Jahima ga vatattu



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 92

وَقِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ

Aka kuma ce da su: “Ina abubuwan da kuka kasance kuna bauta wa?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 93

مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلۡ يَنصُرُونَكُمۡ أَوۡ يَنتَصِرُونَ

“Waxanda ba Allah ba? Shin za su taimake ku, ko za su taimaki kansu?”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 94

فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ

Sai aka kikkifa su cikinta (wutar) su da vatattu



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 95

وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ

Da kuma rundunar Iblis gaba xaya



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 96

قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ

Sai suka ce, alhali suna jayayya da juna a cikinta:



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 97

تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ

“Mun rantse da Allah tabbas mun kasance (a duniya) cikin vata bayyananne



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 98

إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Lokacin da muke daidaita ku da Ubangijin talikai[1]


1- Watau wajen soyayya da bauta.


السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 99

وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ

“Ba kuwa waxanda suka vatar da mu sai manyan masu laifuka



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 100

فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ

“To a (yau) ba mu da wasu masu ceto



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 101

وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٖ

“Ba kuma wani aboki na qut-da-qut



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 102

فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةٗ فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“To ina ma da za mu samu damar komawa, sai mu zamanto daga muminai!”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 103

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu, ba su zamanto muminai ba



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 104

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangijinka tabbas Shi ne Mabuwayi Mai jin qai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 105

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen Nuhu sun qaryata mazanni[1]


1- Domin qaryata Annabi Nuhu () daidai yake da qaryata dukkan manzannin Allah, domin saqo iri xaya suke xauke da shi.


السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 106

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Nuhu ya ce da su: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokin Allah ba?



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 107

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce a gare ku



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 108

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 109

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Ba na kuma tambayar ku wani lada a game da shi (isar da manzancin). Ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 110

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 111

۞قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ

Suka ce: “Yanzu ma yi imani da kai alhali qasqantattu ne mabiyanka?”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 112

قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Ya ce: “Ba ni da sani game da abin da suka zamanto suna aikatawa



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 113

إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ

“Hisabinsu kawai yana wajen Ubangijina ne; da za ku gane



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 114

وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Ni kuma ba mai korar muminai ba ne



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 115

إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ

“Ni kawai mai gargaxi ne mai bayyanawa.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 116

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ

Suka ce: “Ya Nuhu, mun rantse idan ba ka daina (faxar abin da kake faxa) ba, tabbas za ka zamanto daga cikin jefaffu!”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 117

قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun qaryata ni



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 118

فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

“Ka yi hukunci tsakanina da su, kuma Ka tserar da ni tare da muminan da suke tare da ni.”



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 119

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ

Sai Muka tserar da shi da waxanda suke tare da shi a cikin jirgin ruwan da ke maqare (da mutane da dabbobi)



السورة: Suratus Shu’ara

الآية : 120

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ

Sannan bayan haka Muka nutsar da sauran