السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 91

مَا ٱتَّخَذَ ٱللَّهُ مِن وَلَدٖ وَمَا كَانَ مَعَهُۥ مِنۡ إِلَٰهٍۚ إِذٗا لَّذَهَبَ كُلُّ إِلَٰهِۭ بِمَا خَلَقَ وَلَعَلَا بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖۚ سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ

Allah bai riqi wani xa ba, kuma babu wani abin bauta tare da Shi. (Da ko haka ta faru) to da kowanne abin bauta ya kevanta da abin da ya halitta, da kuma wani ya yi rinjaye a kan wani. Allah Ya tsarkaka daga abin da suke sifanta (Shi da shi)



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 92

عَٰلِمِ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ فَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Shi ne Masanin voye da sarari, to Ya xaukaka daga abin da suke shirka (da Shi)



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 93

قُل رَّبِّ إِمَّا تُرِيَنِّي مَا يُوعَدُونَ

Ka ce: “Ubangijina, idan Ka nuna min abin da ake yi musu alqawari da shi (na azaba)



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 94

رَبِّ فَلَا تَجۡعَلۡنِي فِي ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“Ubangijina, kada Ka sanya ni cikin mutane azzalumai.”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 95

وَإِنَّا عَلَىٰٓ أَن نُّرِيَكَ مَا نَعِدُهُمۡ لَقَٰدِرُونَ

Mu kuma lalle Masu iko ne a kan Mu nuna maka abin da Muke musu alkawari



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 96

ٱدۡفَعۡ بِٱلَّتِي هِيَ أَحۡسَنُ ٱلسَّيِّئَةَۚ نَحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَا يَصِفُونَ

Ka ingije mummunan abu da wanda ya fi kyau. Mu ne Muka fi sanin abin da suke siffata (ka da shi)



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 97

وَقُل رَّبِّ أَعُوذُ بِكَ مِنۡ هَمَزَٰتِ ٱلشَّيَٰطِينِ

Kuma ka ce: “Ubangijina, ina neman tsarinka daga waswasin shaixanu



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 98

وَأَعُوذُ بِكَ رَبِّ أَن يَحۡضُرُونِ

“Ina kuma neman tsarinka Ubangijina kar su zo min.”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 99

حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَ أَحَدَهُمُ ٱلۡمَوۡتُ قَالَ رَبِّ ٱرۡجِعُونِ

Har sai idan da mutuwa ta zo wa xayansu zai ce: “Ubangijina, Ku mai da ni (duniya) mana



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 100

لَعَلِّيٓ أَعۡمَلُ صَٰلِحٗا فِيمَا تَرَكۡتُۚ كَلَّآۚ إِنَّهَا كَلِمَةٌ هُوَ قَآئِلُهَاۖ وَمِن وَرَآئِهِم بَرۡزَخٌ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ

“Don in yi aiki na gari game da abin da na bari (a rayuwata).” Ina! Lalle wannan kalma ce da yake faxin ta (da bakinsa). A gabansu kuwa akwai shamaki har zuwa ranar tashinsu



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 101

فَإِذَا نُفِخَ فِي ٱلصُّورِ فَلَآ أَنسَابَ بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ وَلَا يَتَسَآءَلُونَ

Sannan idan aka busa qaho to fa babu wata dangantaka (mai amfani) a tsakaninsu a wannan ranar, kuma ba za su tambayi juna ba



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 102

فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

To waxanda ma’aunansu suka yi nauyi waxannan su ne masu babban rabo



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 103

وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فِي جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ

Waxanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waxannan su ne waxanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 104

تَلۡفَحُ وُجُوهَهُمُ ٱلنَّارُ وَهُمۡ فِيهَا كَٰلِحُونَ

(Wutar) tana qona fuskokinsu alhali kuwa suna ciccije haqoransu a cikinta



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 105

أَلَمۡ تَكُنۡ ءَايَٰتِي تُتۡلَىٰ عَلَيۡكُمۡ فَكُنتُم بِهَا تُكَذِّبُونَ

Yanzu ayoyina ba su zamanto ana karanta muku su ba, sai ya zamana kuna qaryata su?



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 106

قَالُواْ رَبَّنَا غَلَبَتۡ عَلَيۡنَا شِقۡوَتُنَا وَكُنَّا قَوۡمٗا ضَآلِّينَ

Suka ce: “Ya Ubangijinmu, tsiyarmu ce ta rinjaye mu, mun kuma zamo mutane vatattu



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 107

رَبَّنَآ أَخۡرِجۡنَا مِنۡهَا فَإِنۡ عُدۡنَا فَإِنَّا ظَٰلِمُونَ

“Ya Ubangijinmu, Ka fitar da mu daga cikinta, to idan muka sake, to lalle mu azzalumai ne.”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 108

قَالَ ٱخۡسَـُٔواْ فِيهَا وَلَا تُكَلِّمُونِ

Ya ce: “Ku yi min shiru, kada kuwa ku qara yi min magana a cikinta



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 109

إِنَّهُۥ كَانَ فَرِيقٞ مِّنۡ عِبَادِي يَقُولُونَ رَبَّنَآ ءَامَنَّا فَٱغۡفِرۡ لَنَا وَٱرۡحَمۡنَا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰحِمِينَ

“Lalle yadda lamarin yake, wata qungiya daga bayina sun kasance suna cewa: “Ya Ubangijinmu, mun yi imani, sai Ka gafarta mana, kuma Ka ji qan mu, Kai ne kuwa Fiyayyen masu jin qai



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 110

فَٱتَّخَذۡتُمُوهُمۡ سِخۡرِيًّا حَتَّىٰٓ أَنسَوۡكُمۡ ذِكۡرِي وَكُنتُم مِّنۡهُمۡ تَضۡحَكُونَ

“Sai kuka xauke su ababen yi wa izgili, har suka mantar da ku ambatona kuka kuma kasance kuna yi musu dariya



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 111

إِنِّي جَزَيۡتُهُمُ ٱلۡيَوۡمَ بِمَا صَبَرُوٓاْ أَنَّهُمۡ هُمُ ٱلۡفَآئِزُونَ

“Lalle Ni Na saka musu a yau saboda haqurinsu. Lalle kuma su ne marabauta.”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 112

قَٰلَ كَمۡ لَبِثۡتُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ عَدَدَ سِنِينَ

Ya ce: “Zaman shekara nawa kuka yi a bayan qasa?”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 113

قَالُواْ لَبِثۡنَا يَوۡمًا أَوۡ بَعۡضَ يَوۡمٖ فَسۡـَٔلِ ٱلۡعَآدِّينَ

Suka ce: “Mun zauna ne yini xaya ko rabin yini, sai Ka tambayi (mala’iku) masu lissafin (kwanaki)



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 114

قَٰلَ إِن لَّبِثۡتُمۡ إِلَّا قَلِيلٗاۖ لَّوۡ أَنَّكُمۡ كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Ya ce: “Ai ba ku zauna ba sai xan lokaci qanqani (dangane da zaman lahira), da a ce kun kasance kun san da haka.”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 115

أَفَحَسِبۡتُمۡ أَنَّمَا خَلَقۡنَٰكُمۡ عَبَثٗا وَأَنَّكُمۡ إِلَيۡنَا لَا تُرۡجَعُونَ

(Allah Ya ce da su): “Ko kuna tsammani ne cewa Mun halicce ku ne ba manufa kuma ku ba za a dawo da ku gare Mu ba?”



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 116

فَتَعَٰلَى ٱللَّهُ ٱلۡمَلِكُ ٱلۡحَقُّۖ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ رَبُّ ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡكَرِيمِ

To Allah Sarki na gaskiya Ya xaukaka; babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi, (Shi ne) Ubangijin Al’arshi mai girma



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 117

وَمَن يَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ لَا بُرۡهَٰنَ لَهُۥ بِهِۦ فَإِنَّمَا حِسَابُهُۥ عِندَ رَبِّهِۦٓۚ إِنَّهُۥ لَا يُفۡلِحُ ٱلۡكَٰفِرُونَ

Duk wanda ya bauta wa wani abin bauta tare da Allah ba da wata hujja ba game da (wannan bautar), to sakamakonsa wajen Ubangijinsa kawai yake. Lalle su dai kafirai ba za su rabauta ba



السورة: Suratul Mu’uminun

الآية : 118

وَقُل رَّبِّ ٱغۡفِرۡ وَٱرۡحَمۡ وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰحِمِينَ

Kuma ka ce: “Ya Ubangijina Ka gafarta (mana) kuma Ka ji qan mu, Kai ne kuwa Fiyayyen masu jin qai.”