السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 91

قَالُواْ تَٱللَّهِ لَقَدۡ ءَاثَرَكَ ٱللَّهُ عَلَيۡنَا وَإِن كُنَّا لَخَٰطِـِٔينَ

Suka ce: “Wallahi haqiqa Allah Ya fifita ka a kanmu, mu kuma lalle mun tabbata masu kuskure!”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 92

قَالَ لَا تَثۡرِيبَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡيَوۡمَۖ يَغۡفِرُ ٱللَّهُ لَكُمۡۖ وَهُوَ أَرۡحَمُ ٱلرَّـٰحِمِينَ

Ya ce: “A yau babu wani zargi a kanku; Allah zai yafe muku, Shi ne Mafificin masu rahama



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 93

ٱذۡهَبُواْ بِقَمِيصِي هَٰذَا فَأَلۡقُوهُ عَلَىٰ وَجۡهِ أَبِي يَأۡتِ بَصِيرٗا وَأۡتُونِي بِأَهۡلِكُمۡ أَجۡمَعِينَ

“Ku tafi da rigata wannan sannan ku jefa ta a fuskar babana, zai dawo mai gani, ku kuma zo min da iyalanku gaba xaya.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 94

وَلَمَّا فَصَلَتِ ٱلۡعِيرُ قَالَ أَبُوهُمۡ إِنِّي لَأَجِدُ رِيحَ يُوسُفَۖ لَوۡلَآ أَن تُفَنِّدُونِ

Lokacin da ayarin ya baro (Masar) sai babansu ya ce: “Lalle ina jin qanshin Yusufu; ba don dai kada ku ce na susuce ba!”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 95

قَالُواْ تَٱللَّهِ إِنَّكَ لَفِي ضَلَٰلِكَ ٱلۡقَدِيمِ

Suka ce: “Wallahi mun tabbata ba shakka (har yanzu) kana nan cikin daxaxxiyar rikicewar nan taka!”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 96

فَلَمَّآ أَن جَآءَ ٱلۡبَشِيرُ أَلۡقَىٰهُ عَلَىٰ وَجۡهِهِۦ فَٱرۡتَدَّ بَصِيرٗاۖ قَالَ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ مِنَ ٱللَّهِ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

To lokacin da mai albishir ya zo masa sai ya jefa ta (rigar) a fuskarsa, sai ya dawo yana gani. Ya ce: “Ban gaya muku ba cewa lalle ni na san abin da ku ba ku sani ba game da Allah?”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 97

قَالُواْ يَـٰٓأَبَانَا ٱسۡتَغۡفِرۡ لَنَا ذُنُوبَنَآ إِنَّا كُنَّا خَٰطِـِٔينَ

Suka ce: “Ya babanmu, ka nema mana gafarar zunubanmu, lalle mun zamanto masu kuskure!”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 98

قَالَ سَوۡفَ أَسۡتَغۡفِرُ لَكُمۡ رَبِّيٓۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Ya ce: “Ba da daxewa ba zan nema muku gafarar Ubangijina; lalle Shi ne Mai yawan gafara, Mai jin qai.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 99

فَلَمَّا دَخَلُواْ عَلَىٰ يُوسُفَ ءَاوَىٰٓ إِلَيۡهِ أَبَوَيۡهِ وَقَالَ ٱدۡخُلُواْ مِصۡرَ إِن شَآءَ ٱللَّهُ ءَامِنِينَ

Lokacin da suka shiga wurin Yusufu sai ya jawo iyayensa ya kuma ce: “Ku shigo Masar in Allah Ya ga dama kuna amintattu.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 100

وَرَفَعَ أَبَوَيۡهِ عَلَى ٱلۡعَرۡشِ وَخَرُّواْ لَهُۥ سُجَّدٗاۖ وَقَالَ يَـٰٓأَبَتِ هَٰذَا تَأۡوِيلُ رُءۡيَٰيَ مِن قَبۡلُ قَدۡ جَعَلَهَا رَبِّي حَقّٗاۖ وَقَدۡ أَحۡسَنَ بِيٓ إِذۡ أَخۡرَجَنِي مِنَ ٱلسِّجۡنِ وَجَآءَ بِكُم مِّنَ ٱلۡبَدۡوِ مِنۢ بَعۡدِ أَن نَّزَغَ ٱلشَّيۡطَٰنُ بَيۡنِي وَبَيۡنَ إِخۡوَتِيٓۚ إِنَّ رَبِّي لَطِيفٞ لِّمَا يَشَآءُۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡعَلِيمُ ٱلۡحَكِيمُ

Ya kuma xora mahaifansa a kan gadon mulki, suka kuma faxi suna masu gaisuwa a gare shi, ya kuma ce: “Ya babanmu, wannan shi ne fassarar mafarkina na tun tuni. Lalle Ubangijina Ya mai da shi gaskiya; haqiqa kuma Ya kyautata min lokacin da Ya fitar da ni daga kurkuku, Ya kuma zo da ku daga qauye bayan Shaixan ya shiga tsakanina da ‘yan’uwana. Lalle Ubangijina Mai tausasawa ne ga wanda Ya ga dama. Lalle Shi ne Masani, Mai hikima



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 101

۞رَبِّ قَدۡ ءَاتَيۡتَنِي مِنَ ٱلۡمُلۡكِ وَعَلَّمۡتَنِي مِن تَأۡوِيلِ ٱلۡأَحَادِيثِۚ فَاطِرَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ أَنتَ وَلِيِّۦ فِي ٱلدُّنۡيَا وَٱلۡأٓخِرَةِۖ تَوَفَّنِي مُسۡلِمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّـٰلِحِينَ

“Ya Ubangijina, haqiqa Ka ba ni wani abu na mulki, Ka kuma sanar da ni wani abu daga fassarar mafarki; Ya Mahaliccin sammai da qasa, Kai ne Majivincina a duniya da lahira; ka karvi raina ina Musulmi, Ka kuma haxa ni da (mutane) salihai.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 102

ذَٰلِكَ مِنۡ أَنۢبَآءِ ٱلۡغَيۡبِ نُوحِيهِ إِلَيۡكَۖ وَمَا كُنتَ لَدَيۡهِمۡ إِذۡ أَجۡمَعُوٓاْ أَمۡرَهُمۡ وَهُمۡ يَمۡكُرُونَ

Wannan yana daga labaran gaibu da Muke yi maka wahayinsa; ba ka kuma tare da su lokacin da suka haxa al’amarinsu suna qulle-qullen makirci



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 103

وَمَآ أَكۡثَرُ ٱلنَّاسِ وَلَوۡ حَرَصۡتَ بِمُؤۡمِنِينَ

Yawancin mutane ba za su yi imani ba, komai kwaxayinka (ga hakan)



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 104

وَمَا تَسۡـَٔلُهُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۚ إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ

Kuma ba ka tambayar su lada a kansa (wato Alqur’ani). Shi ba wani abu ne daban ba in ban da gargaxi ga talikai



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 105

وَكَأَيِّن مِّنۡ ءَايَةٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ يَمُرُّونَ عَلَيۡهَا وَهُمۡ عَنۡهَا مُعۡرِضُونَ

Kuma ayoyi nawa ne a sammai da qasa waxanda (kafirai) suke wucewa ta wajensu, amma suna bijire musu?



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 106

وَمَا يُؤۡمِنُ أَكۡثَرُهُم بِٱللَّهِ إِلَّا وَهُم مُّشۡرِكُونَ

Yawancinsu kuma ba sa yin imani da Allah sai (an same su) suna masu shirka (da Shi)



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 107

أَفَأَمِنُوٓاْ أَن تَأۡتِيَهُمۡ غَٰشِيَةٞ مِّنۡ عَذَابِ ٱللَّهِ أَوۡ تَأۡتِيَهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Yanzu sun amince ne wata azabar Allah mai lulluvewa ta zo musu, ko kuwa alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, alhalin su ba su sani ba?



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 108

قُلۡ هَٰذِهِۦ سَبِيلِيٓ أَدۡعُوٓاْ إِلَى ٱللَّهِۚ عَلَىٰ بَصِيرَةٍ أَنَا۠ وَمَنِ ٱتَّبَعَنِيۖ وَسُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

Ka ce: “Wannan ce hanyata, ina yin kira zuwa ga Allah, bisa hujja, ni da wanda ya bi ni. Tsarki kuma ya tabbata ga Allah, ni kuwa ba na cikin masu shirka.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 109

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ إِلَّا رِجَالٗا نُّوحِيٓ إِلَيۡهِم مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡقُرَىٰٓۗ أَفَلَمۡ يَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَيَنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۗ وَلَدَارُ ٱلۡأٓخِرَةِ خَيۡرٞ لِّلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Ba Mu kuma aiko (manzanni) a gabaninka ba sai maza ‘yan birni waxanda Muke yi wa wahayi. Me ya sa (kafirai) ba za su yi tafiya ba a bayan qasa don su ga yadda qarshen waxanda suka rigaye su ya kasance? Lalle kuwa gidan lahira shi ya fi ga waxanda suke kiyaye dokokin (Allah). Shin ba za ku hankalta ba?



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 110

حَتَّىٰٓ إِذَا ٱسۡتَيۡـَٔسَ ٱلرُّسُلُ وَظَنُّوٓاْ أَنَّهُمۡ قَدۡ كُذِبُواْ جَآءَهُمۡ نَصۡرُنَا فَنُجِّيَ مَن نَّشَآءُۖ وَلَا يُرَدُّ بَأۡسُنَا عَنِ ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Har yayin da manzanni suka xebe qauna (da imanin mutanensu), su kuma (kafiran) suka yi zaton an faxa musu qarya ne (game da zuwan azabar Allah) sai taimakonmu ya zo musu, sai Muka tserar da wanda Muka ga dama; ba kuwa za a kawar da azabarmu daga mutane masu laifi ba



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 111

لَقَدۡ كَانَ فِي قَصَصِهِمۡ عِبۡرَةٞ لِّأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِۗ مَا كَانَ حَدِيثٗا يُفۡتَرَىٰ وَلَٰكِن تَصۡدِيقَ ٱلَّذِي بَيۡنَ يَدَيۡهِ وَتَفۡصِيلَ كُلِّ شَيۡءٖ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٗ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Haqiqa akwai izina a cikin labaransu (annabawa) ga ma’abota hankali. (Alqur’ani) bai zamanto zance ne da ake qirqirar sa ba, sai dai zance ne da yake gaskata abin da ya rigaye shi (na littattafai), da kuma bayanin komai; shiriya ne kuma da rahama ga mutanen da suke yin imani