السورة: Suratul An’am

الآية : 61

وَهُوَ ٱلۡقَاهِرُ فَوۡقَ عِبَادِهِۦۖ وَيُرۡسِلُ عَلَيۡكُمۡ حَفَظَةً حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ تَوَفَّتۡهُ رُسُلُنَا وَهُمۡ لَا يُفَرِّطُونَ

“Kuma Shi ne wanda Yake da iko a kan bayinsa, kuma Yana aiko muku masu tsaro, har zuwa lokacin da mutuwa za ta zo wa xayanku, sai manzanninmu su karvi ransa, kuma su ba sa yin sakaci



السورة: Suratul An’am

الآية : 62

ثُمَّ رُدُّوٓاْ إِلَى ٱللَّهِ مَوۡلَىٰهُمُ ٱلۡحَقِّۚ أَلَا لَهُ ٱلۡحُكۡمُ وَهُوَ أَسۡرَعُ ٱلۡحَٰسِبِينَ

“Sannan sai a mayar da su zuwa ga Allah Majivincin lamarinsu na gaskiya. Ku saurara, dukkan hukunci nasa ne, kuma Shi ne Mafi gaggawar masu hisabi.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 63

قُلۡ مَن يُنَجِّيكُم مِّن ظُلُمَٰتِ ٱلۡبَرِّ وَٱلۡبَحۡرِ تَدۡعُونَهُۥ تَضَرُّعٗا وَخُفۡيَةٗ لَّئِنۡ أَنجَىٰنَا مِنۡ هَٰذِهِۦ لَنَكُونَنَّ مِنَ ٱلشَّـٰكِرِينَ

Ka ce: “Wane ne yake tserar da ku daga cikin duffai na tudu da na kogi, kuna roqon sa a fili da a voye (cewa): “Tabbas, in da zai tserar da mu daga wannan, to lalle za mu kasance cikin masu godiya.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 64

قُلِ ٱللَّهُ يُنَجِّيكُم مِّنۡهَا وَمِن كُلِّ كَرۡبٖ ثُمَّ أَنتُمۡ تُشۡرِكُونَ

Ka ce: “Allah ne zai tserar da ku daga cikinsa (tsoron), da ma duk wani baqin ciki, sannan sai ga ku kuna yin shirka.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 65

قُلۡ هُوَ ٱلۡقَادِرُ عَلَىٰٓ أَن يَبۡعَثَ عَلَيۡكُمۡ عَذَابٗا مِّن فَوۡقِكُمۡ أَوۡ مِن تَحۡتِ أَرۡجُلِكُمۡ أَوۡ يَلۡبِسَكُمۡ شِيَعٗا وَيُذِيقَ بَعۡضَكُم بَأۡسَ بَعۡضٍۗ ٱنظُرۡ كَيۡفَ نُصَرِّفُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّهُمۡ يَفۡقَهُونَ

Ka ce: “Shi ne Mai cikakken ikon Ya aiko muku da azaba ta samanku ko ta qarqashin qafafuwanku ko Ya mayar da ku qungiyoyi daban-daban, kuma Ya xanxana wa sashinku azabar sashi.” Duba ka ga yadda Muke bayyana ayoyi, don su fahimta



السورة: Suratul An’am

الآية : 66

وَكَذَّبَ بِهِۦ قَوۡمُكَ وَهُوَ ٱلۡحَقُّۚ قُل لَّسۡتُ عَلَيۡكُم بِوَكِيلٖ

Kuma mutanenka sun qaryata shi (Alqur’ani) alhali shi ne gaskiya. Ka ce: “Ni ba wakili ne a kanku ba



السورة: Suratul An’am

الآية : 67

لِّكُلِّ نَبَإٖ مُّسۡتَقَرّٞۚ وَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَ

“Kowane labari yana da lokaci ne na musamman. Kuma da sannu za ku sani.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 68

وَإِذَا رَأَيۡتَ ٱلَّذِينَ يَخُوضُونَ فِيٓ ءَايَٰتِنَا فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ يَخُوضُواْ فِي حَدِيثٍ غَيۡرِهِۦۚ وَإِمَّا يُنسِيَنَّكَ ٱلشَّيۡطَٰنُ فَلَا تَقۡعُدۡ بَعۡدَ ٱلذِّكۡرَىٰ مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma idan ka ga waxanda suke kutsawa cikin ayoyinmu (suna izgili), to ka rabu da su, har sai sun canja wani zancen da ba wancan ba. Amma in da Shaixan zai mantar da kai kuwa, to bayan ka tuna kar ka sake zama tare da azzalumai



السورة: Suratul An’am

الآية : 69

وَمَا عَلَى ٱلَّذِينَ يَتَّقُونَ مِنۡ حِسَابِهِم مِّن شَيۡءٖ وَلَٰكِن ذِكۡرَىٰ لَعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ

Kuma babu wani laifi a kan waxanda suke tsoron haxuwarsu da Allah (don sun zauna da su), sai dai kuma (dole su yi) musu wa’azi don su tsorata



السورة: Suratul An’am

الآية : 70

وَذَرِ ٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ دِينَهُمۡ لَعِبٗا وَلَهۡوٗا وَغَرَّتۡهُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَاۚ وَذَكِّرۡ بِهِۦٓ أَن تُبۡسَلَ نَفۡسُۢ بِمَا كَسَبَتۡ لَيۡسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ وَلِيّٞ وَلَا شَفِيعٞ وَإِن تَعۡدِلۡ كُلَّ عَدۡلٖ لَّا يُؤۡخَذۡ مِنۡهَآۗ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ أُبۡسِلُواْ بِمَا كَسَبُواْۖ لَهُمۡ شَرَابٞ مِّنۡ حَمِيمٖ وَعَذَابٌ أَلِيمُۢ بِمَا كَانُواْ يَكۡفُرُونَ

Ka rabu da waxanda suka xauki addininsu wasa da sharholiya, rayuwarsu ta duniya kuma ta ruxe su. Ka kuma yi gargaxi da shi (Alqur’ani), saboda kada a jarrabi rai da abin da ya aikata wanda ba ya da wani mataimaki ko mai ceto ban da Allah, ko da kuwa (ran) ya ba da kowace irin fansa ba za a karva ba daga gare shi. Waxancan su ne waxanda aka kange (don yi musu azaba) saboda abin da suka aikata; suna da abin sha na tafasasshen ruwa da kuma azaba mai raxaxi saboda abin da suka zamanto suna kafircewa (da shi)



السورة: Suratul An’am

الآية : 71

قُلۡ أَنَدۡعُواْ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَا يَنفَعُنَا وَلَا يَضُرُّنَا وَنُرَدُّ عَلَىٰٓ أَعۡقَابِنَا بَعۡدَ إِذۡ هَدَىٰنَا ٱللَّهُ كَٱلَّذِي ٱسۡتَهۡوَتۡهُ ٱلشَّيَٰطِينُ فِي ٱلۡأَرۡضِ حَيۡرَانَ لَهُۥٓ أَصۡحَٰبٞ يَدۡعُونَهُۥٓ إِلَى ٱلۡهُدَى ٱئۡتِنَاۗ قُلۡ إِنَّ هُدَى ٱللَّهِ هُوَ ٱلۡهُدَىٰۖ وَأُمِرۡنَا لِنُسۡلِمَ لِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka ce: “Shin yanzu ma riqa bauta wa wani wanda ba Allah ba, abin da ba zai amfane mu ba, kuma ba zai cutar da mu ba, mu koma gidan jiya (kafirai) bayan kuwa Allah Ya shiryar da mu, (mu koma) kamar wanda shaixanu suka vatar da shi yana ta ximuwa a bayan qasa, ga shi da wasu abokai suna kiran sa zuwa ga shiriya, (suna cewa): “Ka zo (mu bi tafarkin shiriya)[1].” Ka ce: “Lalle shiriyar Allah fa ita kaxai ce shiriya; kuma mu an umarce mu da mu miqa wuya ne kaxai ga Ubangijin talikai


1- Misali ne na wanda ya saki Musulunci ya kama shirka ko vata, ya zama kamar mutumin da aljanu suka xauke shi suka tafi da shi suka jefar da shi a qurgurmin daji. Don haka ya yi nisan da ba zai ji kira ba, balle ya gane hanyar dawowa.


السورة: Suratul An’am

الآية : 72

وَأَنۡ أَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَٱتَّقُوهُۚ وَهُوَ ٱلَّذِيٓ إِلَيۡهِ تُحۡشَرُونَ

“Kuma ku tsayar da salla kuma ku kiyaye dokokinsa. Kuma Shi ne Wanda za a tara ku zuwa gare Shi



السورة: Suratul An’am

الآية : 73

وَهُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۖ وَيَوۡمَ يَقُولُ كُن فَيَكُونُۚ قَوۡلُهُ ٱلۡحَقُّۚ وَلَهُ ٱلۡمُلۡكُ يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِۚ عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡخَبِيرُ

“Kuma Shi ne Wanda ya halicci sammai da qasa da gaskiya; kuma (ku tuna) ranar da zai ce da abu: ‘Kasance!’ Nan take sai ya kasance. Maganarsa gaskiya ce. Kuma Shi ne Yake da cikakken mulki a ranar da za a busa qaho Masanin gaibu da sarari, kuma Shi ne Mai hikima, Mai cikakken sani.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 74

۞وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِيمُ لِأَبِيهِ ءَازَرَ أَتَتَّخِذُ أَصۡنَامًا ءَالِهَةً إِنِّيٓ أَرَىٰكَ وَقَوۡمَكَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Kuma (ka tuna) lokacin da Ibrahimu ya ce da babansa Azaru: “Yanzu ka riqi gumaka a matsayin alloli? Lalle ni ina ganin ka kai da mutanenka, kuna cikin vata mabayyani.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 75

وَكَذَٰلِكَ نُرِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ مَلَكُوتَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلِيَكُونَ مِنَ ٱلۡمُوقِنِينَ

Kuma kamar haka ne Muke nuna wa Ibrahimu halittun sammai da qasa, domin ya kasance cikin masu sakankancewa



السورة: Suratul An’am

الآية : 76

فَلَمَّا جَنَّ عَلَيۡهِ ٱلَّيۡلُ رَءَا كَوۡكَبٗاۖ قَالَ هَٰذَا رَبِّيۖ فَلَمَّآ أَفَلَ قَالَ لَآ أُحِبُّ ٱلۡأٓفِلِينَ

To yayin da dare ya lulluve shi, ya ga tauraro, sai ya ce; “Wannan shi ne ubangijina;”[1] sannan yayin da ya vace, sai ya ce: “Ni fa ba na son abubuwa masu gushewa.”


1- Daga wannan ayar zuwa aya ta 79 Allah () ya koya wa Annabi Ibrahim () hanyar da zai yi wa mutanensa wa’azi cikin hikima da laluma don jan hankalinsu su fahimci abubuwan da suke bauta wa ba ababen bauta ne na gaskiya ba.


السورة: Suratul An’am

الآية : 77

فَلَمَّا رَءَا ٱلۡقَمَرَ بَازِغٗا قَالَ هَٰذَا رَبِّيۖ فَلَمَّآ أَفَلَ قَالَ لَئِن لَّمۡ يَهۡدِنِي رَبِّي لَأَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلضَّآلِّينَ

Sa’annan yayin da ya ga wata ya fito, sai ya ce; “Wannan shi ne ubangijina;” sannan yayin da ya gushe, sai ya ce: “Lalle idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haqiqa zan kasance daga cikin mutane vatattu.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 78

فَلَمَّا رَءَا ٱلشَّمۡسَ بَازِغَةٗ قَالَ هَٰذَا رَبِّي هَٰذَآ أَكۡبَرُۖ فَلَمَّآ أَفَلَتۡ قَالَ يَٰقَوۡمِ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تُشۡرِكُونَ

Sannan yayin da ya ga rana ta hudo, sai ya ce: “Wannan shi ne ubangijina, wannan shi ya fi girma;” sannan yayin da ta vace, sai ya ce: “Ya ku mutanena, haqiqa ni ba ruwana da abin da kuke haxa Allah da shi



السورة: Suratul An’am

الآية : 79

إِنِّي وَجَّهۡتُ وَجۡهِيَ لِلَّذِي فَطَرَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ حَنِيفٗاۖ وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

“Lalle ni kam na juyar da fuskata ga Wanda Ya halicci sammai da qasa, ina mai kauce wa varna kuma ni ba na cikin masu yin shirka.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 80

وَحَآجَّهُۥ قَوۡمُهُۥۚ قَالَ أَتُحَـٰٓجُّوٓنِّي فِي ٱللَّهِ وَقَدۡ هَدَىٰنِۚ وَلَآ أَخَافُ مَا تُشۡرِكُونَ بِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَشَآءَ رَبِّي شَيۡـٔٗاۚ وَسِعَ رَبِّي كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمًاۚ أَفَلَا تَتَذَكَّرُونَ

Kuma mutanensa sun yi jayayya da shi; (sai) ya ce: “Shin yanzu kwa riqa jayayya da ni game da (kaxaitakar) Allah, alhalin kuwa Ya shiryar da ni? Kuma ba na jin tsoron abin da kuke sanya wa Allah kishiya da shi, sai abin da Ubangijina Ya ga dama. Kuma ilimin Ubangijina ya yalwaci komai. Shin ba za ku wa’azantu ba?



السورة: Suratul An’am

الآية : 81

وَكَيۡفَ أَخَافُ مَآ أَشۡرَكۡتُمۡ وَلَا تَخَافُونَ أَنَّكُمۡ أَشۡرَكۡتُم بِٱللَّهِ مَا لَمۡ يُنَزِّلۡ بِهِۦ عَلَيۡكُمۡ سُلۡطَٰنٗاۚ فَأَيُّ ٱلۡفَرِيقَيۡنِ أَحَقُّ بِٱلۡأَمۡنِۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

“To ta qaqa kuwa zan ji tsoron abin da kuka tara da (Allah), alhali ku kuma ba kwa jin tsoron kun sanya wa Allah kishiya, abin da kuwa bai saukar muku da wata hujja a kai ba? To wane vangare ne cikin vangarori biyu, ya fi dacewa da samun aminci; in har kun kasance kun sani?



السورة: Suratul An’am

الآية : 82

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَلَمۡ يَلۡبِسُوٓاْ إِيمَٰنَهُم بِظُلۡمٍ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱلۡأَمۡنُ وَهُم مُّهۡتَدُونَ

“Waxanda suka yi imani, kuma ba su garwaya imaninsu da zalunci ba, waxannan su suke da aminci, kuma su ne shiryayyu.”



السورة: Suratul An’am

الآية : 83

وَتِلۡكَ حُجَّتُنَآ ءَاتَيۡنَٰهَآ إِبۡرَٰهِيمَ عَلَىٰ قَوۡمِهِۦۚ نَرۡفَعُ دَرَجَٰتٖ مَّن نَّشَآءُۗ إِنَّ رَبَّكَ حَكِيمٌ عَلِيمٞ

Kuma waxancan su ne hujjojinmu da Muka ba wa Ibrahimu su a kan mutanensa. Muna xaukaka darajojin waxanda Muka ga dama. Lalle Ubangijinka Mai hikima ne, Mai yawan sani



السورة: Suratul An’am

الآية : 84

وَوَهَبۡنَا لَهُۥٓ إِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَۚ كُلًّا هَدَيۡنَاۚ وَنُوحًا هَدَيۡنَا مِن قَبۡلُۖ وَمِن ذُرِّيَّتِهِۦ دَاوُۥدَ وَسُلَيۡمَٰنَ وَأَيُّوبَ وَيُوسُفَ وَمُوسَىٰ وَهَٰرُونَۚ وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma Muka ba shi Ishaqa da Ya’aqubu. Kowanne daga cikinsu Mun shiryar da shi, kuma Mun shiryar da Nuhu tun gabaninsu. Kuma daga cikin zurriyarsa akwai Dawudu da Sulaimanu da Ayyuba da Yusufu da Musa da Haruna. Kuma kamar haka ne Muke saka wa masu kyautata (ayyukansu)



السورة: Suratul An’am

الآية : 85

وَزَكَرِيَّا وَيَحۡيَىٰ وَعِيسَىٰ وَإِلۡيَاسَۖ كُلّٞ مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Da Zakariyya da Yahaya da Isa da Iliyasu; kowanne daga cikinsu yana cikin salihan bayi



السورة: Suratul An’am

الآية : 86

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَيُونُسَ وَلُوطٗاۚ وَكُلّٗا فَضَّلۡنَا عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Da Isma’ilu da Alyasa’u da Yunusu da Luxu. Kowanne daga cikinsu kuma Mun fifita shi a kan (sauran) talikai



السورة: Suratul An’am

الآية : 87

وَمِنۡ ءَابَآئِهِمۡ وَذُرِّيَّـٰتِهِمۡ وَإِخۡوَٰنِهِمۡۖ وَٱجۡتَبَيۡنَٰهُمۡ وَهَدَيۡنَٰهُمۡ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Kuma daga cikin iyayensu da zurriyarsu da ‘yan’uwansu; duka Mun zave su, kuma Mun shiryar da su zuwa ga tafarki madaidaici



السورة: Suratul An’am

الآية : 88

ذَٰلِكَ هُدَى ٱللَّهِ يَهۡدِي بِهِۦ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦۚ وَلَوۡ أَشۡرَكُواْ لَحَبِطَ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Wannan ita ce shiriyar Allah wadda da ita ne Yake shiryar da wanda Ya ga dama cikin bayinsa. Kuma da a ce sun yi shirka, to lalle da duk abin da suka kasance suna aikatawa ya rushe



السورة: Suratul An’am

الآية : 89

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ ءَاتَيۡنَٰهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحُكۡمَ وَٱلنُّبُوَّةَۚ فَإِن يَكۡفُرۡ بِهَا هَـٰٓؤُلَآءِ فَقَدۡ وَكَّلۡنَا بِهَا قَوۡمٗا لَّيۡسُواْ بِهَا بِكَٰفِرِينَ

Waxannan su ne waxanda Muka bai wa littattafai da hukunci da annabta. To idan waxancan (mutanen Makka) suka kafirce mata (shiriya), to haqiqa Mun shirya musu waxansu mutane waxanda ba za su kafirce mata ba



السورة: Suratul An’am

الآية : 90

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ هَدَى ٱللَّهُۖ فَبِهُدَىٰهُمُ ٱقۡتَدِهۡۗ قُل لَّآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ أَجۡرًاۖ إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡعَٰلَمِينَ

Waxannan su ne waxanda Allah Ya shiryar; don haka ka yi koyi da irin shiriyarsu. Ka ce: “Ba na roqon ku wani lada game da shi (Alqur’ani); shi ba komai ba ne face tunatarwa ga talikai.”