السورة: Suratul Anbiya

الآية : 61

قَالُواْ فَأۡتُواْ بِهِۦ عَلَىٰٓ أَعۡيُنِ ٱلنَّاسِ لَعَلَّهُمۡ يَشۡهَدُونَ

Suka ce: “(Ku je) ku zo da shi kan idon mutane don su shaidi (abin da ya aikata).”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 62

قَالُوٓاْ ءَأَنتَ فَعَلۡتَ هَٰذَا بِـَٔالِهَتِنَا يَـٰٓإِبۡرَٰهِيمُ

(Da aka kawo shi sai) suka ce: “Yanzu kai ka aikata wannan (irin aiki) ga ababen bautarmu, ya Ibrahimu?”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 63

قَالَ بَلۡ فَعَلَهُۥ كَبِيرُهُمۡ هَٰذَا فَسۡـَٔلُوهُمۡ إِن كَانُواْ يَنطِقُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “A’a, wannan babban nasu (shi) ya aikata shi, sai ku tambaye su idan ya zamana suna magana.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 64

فَرَجَعُوٓاْ إِلَىٰٓ أَنفُسِهِمۡ فَقَالُوٓاْ إِنَّكُمۡ أَنتُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Sai suka koma ga (zargin) kawunansu sannan suka ce: “Lallai ku dai ne azzalumai.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 65

ثُمَّ نُكِسُواْ عَلَىٰ رُءُوسِهِمۡ لَقَدۡ عَلِمۡتَ مَا هَـٰٓؤُلَآءِ يَنطِقُونَ

Sannan aka juyo da kawunansu (zuwa kafirci) suka ce (da Ibrahimu): “Mun rantse haqiqa ka san cewa su waxannan ba sa magana.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 66

قَالَ أَفَتَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَا يَنفَعُكُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَا يَضُرُّكُمۡ

Ya ce: “To yanzu kwa riqa bauta wa wani ba Allah ba, wanda ba zai amfana muku komai ba kuma ba zai cuce ku ba?



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 67

أُفّٖ لَّكُمۡ وَلِمَا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

“Tir da ku, da kuma abin da kuke bauta wa wanda ba Allah ba. To yanzu ba kwa hankalta ba?”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 68

قَالُواْ حَرِّقُوهُ وَٱنصُرُوٓاْ ءَالِهَتَكُمۡ إِن كُنتُمۡ فَٰعِلِينَ

Sai suka ce: “Ku qone shi ku kuma taimaki allolinku in kun kasance masu aikata hakan.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 69

قُلۡنَا يَٰنَارُ كُونِي بَرۡدٗا وَسَلَٰمًا عَلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ

(Da suka jefa shi cikin wutar sai) Muka ce: “Ke wuta, ki zama sassanya da kuma aminci ga Ibrahimu!”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 70

وَأَرَادُواْ بِهِۦ كَيۡدٗا فَجَعَلۡنَٰهُمُ ٱلۡأَخۡسَرِينَ

Suka yi nufin shirya masa makirci sai Muka mayar da su tavavvu



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 71

وَنَجَّيۡنَٰهُ وَلُوطًا إِلَى ٱلۡأَرۡضِ ٱلَّتِي بَٰرَكۡنَا فِيهَا لِلۡعَٰلَمِينَ

Muka kuma tserar da shi, shi da Luxu zuwa ga qasar da Muka yi albarka a cikinta ga talikai (watau Sham)



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 72

وَوَهَبۡنَا لَهُۥٓ إِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ نَافِلَةٗۖ وَكُلّٗا جَعَلۡنَا صَٰلِحِينَ

Muka kuma ba shi Is’haqa da kuma Ya’aqubu qari (wato jika). Dukkanninsu kuma Mun sanya su salihai



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 73

وَجَعَلۡنَٰهُمۡ أَئِمَّةٗ يَهۡدُونَ بِأَمۡرِنَا وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡهِمۡ فِعۡلَ ٱلۡخَيۡرَٰتِ وَإِقَامَ ٱلصَّلَوٰةِ وَإِيتَآءَ ٱلزَّكَوٰةِۖ وَكَانُواْ لَنَا عَٰبِدِينَ

Muka kuma sanya su shugabanni masu shiryarwa da umarninmu, Muka kuma yi musu wahayi na aikata alheri da tsai da salla da ba da zakka, sun kuwa zamanto masu bauta mana ne



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 74

وَلُوطًا ءَاتَيۡنَٰهُ حُكۡمٗا وَعِلۡمٗا وَنَجَّيۡنَٰهُ مِنَ ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلَّتِي كَانَت تَّعۡمَلُ ٱلۡخَبَـٰٓئِثَۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمَ سَوۡءٖ فَٰسِقِينَ

Luxu kuma Muka ba shi hukunci da ilimi, Muka kuma tserar da shi daga alqaryar nan da (mutanenta) suka zamanto suna aikata munanan ayyuka. Lallai su sun kasance mutanen banza ne fasiqai



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 75

وَأَدۡخَلۡنَٰهُ فِي رَحۡمَتِنَآۖ إِنَّهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Muka kuma shigar da shi cikin rahamarmu; lallai shi yana daga (cikin) mutane na gari



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 76

وَنُوحًا إِذۡ نَادَىٰ مِن قَبۡلُ فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

(Ka tuna) lokacin da Nuhu ya roqi Ubangijinsa tun a da can[1], sannan Muka amsa masa (roqonsa) Muka tserar da shi da iyalinsa daga baqin ciki mai girma


1- Duba Suratu Nuh, aya ta 26-28.


السورة: Suratul Anbiya

الآية : 77

وَنَصَرۡنَٰهُ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَآۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمَ سَوۡءٖ فَأَغۡرَقۡنَٰهُمۡ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma taimake shi bisa mutanen da suka qaryata ayoyinmu. Lalle su sun kasance mutanen banza, sai Muka nutsar da su gaba xaya



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 78

وَدَاوُۥدَ وَسُلَيۡمَٰنَ إِذۡ يَحۡكُمَانِ فِي ٱلۡحَرۡثِ إِذۡ نَفَشَتۡ فِيهِ غَنَمُ ٱلۡقَوۡمِ وَكُنَّا لِحُكۡمِهِمۡ شَٰهِدِينَ

(Ka tuna) kuma Dawuda da Sulaimanu lokacin da suke yin hukunci a kan amfanin gona lokacin da dabbobin wasu mutane suka cinye shi da daddare, Mun kuwa zamanto Muna sane da irin hukuncin nasu



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 79

فَفَهَّمۡنَٰهَا سُلَيۡمَٰنَۚ وَكُلًّا ءَاتَيۡنَا حُكۡمٗا وَعِلۡمٗاۚ وَسَخَّرۡنَا مَعَ دَاوُۥدَ ٱلۡجِبَالَ يُسَبِّحۡنَ وَٱلطَّيۡرَۚ وَكُنَّا فَٰعِلِينَ

Sai Muka ganar da Sulaimanu shi (hukuncin)[1]. Kuma dukkaninsu Mun ba su annabta da ilimi. Muka kuma hore wa Dawuda duwatsu da tsuntsaye, suna tasbihi tare da shi. Mun kuwa kasance Masu aikata (haka)


1- Da farko Annabi Dawud () ya yi hukunci da cewa, manomin zai karvi dabbobin a madadin amfanin gonarsa da suka cinye. Amma sai Sulaiman () ya sake hukunci da cewa, manomin zai riqe dabbobin yana amfanuwa da su har zuwa lokacin da masu dabbobin za su sake noma musu gonarsa ta dawo kamar farko sai su karvi dabbobinsu.


السورة: Suratul Anbiya

الآية : 80

وَعَلَّمۡنَٰهُ صَنۡعَةَ لَبُوسٖ لَّكُمۡ لِتُحۡصِنَكُم مِّنۢ بَأۡسِكُمۡۖ فَهَلۡ أَنتُمۡ شَٰكِرُونَ

Muka kuma koya masa yadda ake qera silke dominku don ya kare ku lokacin yaqinku; to shin ku masu godiya ne?



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 81

وَلِسُلَيۡمَٰنَ ٱلرِّيحَ عَاصِفَةٗ تَجۡرِي بِأَمۡرِهِۦٓ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ ٱلَّتِي بَٰرَكۡنَا فِيهَاۚ وَكُنَّا بِكُلِّ شَيۡءٍ عَٰلِمِينَ

Sulaimanu kuwa (Muka hore masa) iska mai qarfi tana gudu da umarninsa zuwa qasar da Muka yi albarka a cikinta, (watau Sham). Mun kuwa kasance Masana ga kowanne abu



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 82

وَمِنَ ٱلشَّيَٰطِينِ مَن يَغُوصُونَ لَهُۥ وَيَعۡمَلُونَ عَمَلٗا دُونَ ذَٰلِكَۖ وَكُنَّا لَهُمۡ حَٰفِظِينَ

Akwai kuma wasu aljannu da suke nutso don fito masa (da lu’u-lu’u) suna kuma yin wani aikin ban da wannan (kamar gine-gine); Mun zamanto kuma Masu kula da su))



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 83

۞وَأَيُّوبَ إِذۡ نَادَىٰ رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَسَّنِيَ ٱلضُّرُّ وَأَنتَ أَرۡحَمُ ٱلرَّـٰحِمِينَ

Kuma (ka tuna) Ayyuba lokacin da ya roqi Ubangijinsa (yana cewa): “Lallai cuta ta same ni, Kai ne kuwa Mafi jin qan masu jin qai!”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 84

فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ فَكَشَفۡنَا مَا بِهِۦ مِن ضُرّٖۖ وَءَاتَيۡنَٰهُ أَهۡلَهُۥ وَمِثۡلَهُم مَّعَهُمۡ رَحۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَا وَذِكۡرَىٰ لِلۡعَٰبِدِينَ

Sai Muka amsa masa (roqonsa) sannan Muka yaye cutar da take tare da shi, Muka kuma ba shi (madadin) iyalinsa (da ya rasa) da kuma kwatankwacinsu tare da su don jin qai daga gare Mu da kuma wa’azi ga masu bauta (ga Allah)



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 85

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَإِدۡرِيسَ وَذَا ٱلۡكِفۡلِۖ كُلّٞ مِّنَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

(Ka tuna) kuma Isma’ila da Idrisa da kuma Zulkifli; dukkansu suna cikin masu haquri



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 86

وَأَدۡخَلۡنَٰهُمۡ فِي رَحۡمَتِنَآۖ إِنَّهُم مِّنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Muka kuma shigar da su cikin rahamarmu; lalle su suna daga bayi na gari



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 87

وَذَا ٱلنُّونِ إِذ ذَّهَبَ مُغَٰضِبٗا فَظَنَّ أَن لَّن نَّقۡدِرَ عَلَيۡهِ فَنَادَىٰ فِي ٱلظُّلُمَٰتِ أَن لَّآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنتَ سُبۡحَٰنَكَ إِنِّي كُنتُ مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma (ka tuna) ma’abocin kifi (wato Yunusa) lokacin da ya tafi yana cike da fushi[1], sannan ya zaci cewa ba za Mu quntata masa ba, sai ya kira (Mu) a cikin duffai[2] yana cewa: “Ba wani abin bauta da gaskiya sai Kai (ya Allah), tsarki ya tabbata a gare Ka, lallai ni na kasance cikin azzalumai!”


1- Watau saboda mutanensa sun kafe a kan kafirci sun qi yin imani.


2- Watau duhun dare da duhun kogi da duhun cikin kifi.


السورة: Suratul Anbiya

الآية : 88

فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ وَنَجَّيۡنَٰهُ مِنَ ٱلۡغَمِّۚ وَكَذَٰلِكَ نُـۨجِي ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Sai Muka amsa masa Muka kuma tserar da shi daga baqin ciki. Kamar haka kuwa Muke tserar da muminai



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 89

وَزَكَرِيَّآ إِذۡ نَادَىٰ رَبَّهُۥ رَبِّ لَا تَذَرۡنِي فَرۡدٗا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡوَٰرِثِينَ

(Ka tuna) kuma Zakariya’u lokacin da ya roqi Ubangijinsa (cewa): “Ya Ubangijina, kada Ka bar ni ni kaxai (ba magaji), Kai ne kuwa Fiyayyen magada.”



السورة: Suratul Anbiya

الآية : 90

فَٱسۡتَجَبۡنَا لَهُۥ وَوَهَبۡنَا لَهُۥ يَحۡيَىٰ وَأَصۡلَحۡنَا لَهُۥ زَوۡجَهُۥٓۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ يُسَٰرِعُونَ فِي ٱلۡخَيۡرَٰتِ وَيَدۡعُونَنَا رَغَبٗا وَرَهَبٗاۖ وَكَانُواْ لَنَا خَٰشِعِينَ

Sai Muka amsa masa Muka ba shi Yahya, Muka kuma gyara masa (mahaifar) matarsa. Lallai su sun kasance suna gaggawa wajen yin alherai, suna kuma roqon Mu suna masu kwaxayin (rahamarmu) masu kuma tsoron (azabarmu), sun kuma zamanto masu qasqantar da kai gare Mu