السورة: Suratut Tauba

الآية : 31

ٱتَّخَذُوٓاْ أَحۡبَارَهُمۡ وَرُهۡبَٰنَهُمۡ أَرۡبَابٗا مِّن دُونِ ٱللَّهِ وَٱلۡمَسِيحَ ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُوٓاْ إِلَٰهٗا وَٰحِدٗاۖ لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ سُبۡحَٰنَهُۥ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Sun xauki malamansu da masu ibadarsu da kuma Almasihu xan Maryamu iyayen giji maimakon Allah[1], alhali kuwa ba abin da aka umarce su sai su bauta wa Abin bauta Xaya, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Ya tsarkaka daga abin da suke tara Shi da shi


1- Watau suna yi wa malamansu da masu bauta a cikinsu makauniyar biyayya, suna haramta musu halal, su kuma halatta musu haram. Nasara sun xauki Annabi Isa () abin bauta ba Allah ba.


السورة: Suratut Tauba

الآية : 32

يُرِيدُونَ أَن يُطۡفِـُٔواْ نُورَ ٱللَّهِ بِأَفۡوَٰهِهِمۡ وَيَأۡبَى ٱللَّهُ إِلَّآ أَن يُتِمَّ نُورَهُۥ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡكَٰفِرُونَ

Suna nufi ne su dushashe hasken Allah da bakunansu, Allah kuwa ba zai qyale ba har sai Ya cika haskensa ko da kuwa kafirai sun qi



السورة: Suratut Tauba

الآية : 33

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَرۡسَلَ رَسُولَهُۥ بِٱلۡهُدَىٰ وَدِينِ ٱلۡحَقِّ لِيُظۡهِرَهُۥ عَلَى ٱلدِّينِ كُلِّهِۦ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡمُشۡرِكُونَ

Shi ne wanda Ya aiko Manzonsa da shiriya da kuma addini na gaskiya don Ya xora shi a kan dukkanin addinai, ko da kuwa mushrikai sun qi



السورة: Suratut Tauba

الآية : 34

۞يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِنَّ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلۡأَحۡبَارِ وَٱلرُّهۡبَانِ لَيَأۡكُلُونَ أَمۡوَٰلَ ٱلنَّاسِ بِٱلۡبَٰطِلِ وَيَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِۗ وَٱلَّذِينَ يَكۡنِزُونَ ٱلذَّهَبَ وَٱلۡفِضَّةَ وَلَا يُنفِقُونَهَا فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَبَشِّرۡهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٖ

Ya ku waxanda suka yi imani, lalle da yawa daga malaman (Yahudawa) da masu ibada (Nasara) tabbas suna cin dukiyoyin mutane ta hanyar cuta, suna kuma toshe hanyar Allah. Waxanda kuma suke voye zinariya da azurfa ba sa ciyar da ita saboda Allah[1], to ka yi musu albishir da wata azaba mai raxaxi


1- Watau ba sa fitar da zakka daga dukiyarsu.


السورة: Suratut Tauba

الآية : 35

يَوۡمَ يُحۡمَىٰ عَلَيۡهَا فِي نَارِ جَهَنَّمَ فَتُكۡوَىٰ بِهَا جِبَاهُهُمۡ وَجُنُوبُهُمۡ وَظُهُورُهُمۡۖ هَٰذَا مَا كَنَزۡتُمۡ لِأَنفُسِكُمۡ فَذُوقُواْ مَا كُنتُمۡ تَكۡنِزُونَ

Ranar da za a narkar da su (zinariya da azurfa) cikin wutar Jahannama sannan a yi wa fuskokinsu da kuyavunsu da bayansu lalas da su, (a ce da su): “Wannan shi ne abin da kuka taskace wa kanku, sai ku xanxani abin da kuka kasance kuna taskacewa.”



السورة: Suratut Tauba

الآية : 36

إِنَّ عِدَّةَ ٱلشُّهُورِ عِندَ ٱللَّهِ ٱثۡنَا عَشَرَ شَهۡرٗا فِي كِتَٰبِ ٱللَّهِ يَوۡمَ خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ مِنۡهَآ أَرۡبَعَةٌ حُرُمٞۚ ذَٰلِكَ ٱلدِّينُ ٱلۡقَيِّمُۚ فَلَا تَظۡلِمُواْ فِيهِنَّ أَنفُسَكُمۡۚ وَقَٰتِلُواْ ٱلۡمُشۡرِكِينَ كَآفَّةٗ كَمَا يُقَٰتِلُونَكُمۡ كَآفَّةٗۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلۡمُتَّقِينَ

Lalle adadin watanni a wurin Allah wata goma sha biyu ne a cikin littafin Allah, tun ranar da Ya halicci sammai da qasa, daga cikinsu akwai (wata) huxu masu alfarma[1]. Wannan shi ne addini madaidaici. To kada ku zalunci kanku a cikinsu[2], kuma ku yaqi mushrikai gaba xaya kamar yadda suke yaqar ku gaba xaya. Ku kuma sani cewa Allah Yana tare da masu taqawa


1- Su ne watan Zulqi’ida da Zulhijja da Al-Muharram da Rajab.


2- Watau ta hanyar shiga yaqi da wasu ko aikata miyagun laifuka.


السورة: Suratut Tauba

الآية : 37

إِنَّمَا ٱلنَّسِيٓءُ زِيَادَةٞ فِي ٱلۡكُفۡرِۖ يُضَلُّ بِهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُحِلُّونَهُۥ عَامٗا وَيُحَرِّمُونَهُۥ عَامٗا لِّيُوَاطِـُٔواْ عِدَّةَ مَا حَرَّمَ ٱللَّهُ فَيُحِلُّواْ مَا حَرَّمَ ٱللَّهُۚ زُيِّنَ لَهُمۡ سُوٓءُ أَعۡمَٰلِهِمۡۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Lalle jinkiri[1] ba wani abu ba ne ban da qari cikin kafirci, wanda da shi (jinkirin) ake vatar da waxanda suka kafirta, suna halatta shi a wata shekarar, su kuma haramta shi a wata, wai don su daidaita adadin abin da Allah Ya haramta, sai su halatta abin da Allah Ya haramta. An qawata musu munanan ayyukansu. Allah kuwa ba Ya shiryar da mutane kafirai


1- Wata mummunar al’ada ce ta Larabawa a jahiiyya, sukan jinkirta watan Muharram su musanya shi da Safar, domin su halatta wa kansu yin yaqi a cikinsa.


السورة: Suratut Tauba

الآية : 38

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَا لَكُمۡ إِذَا قِيلَ لَكُمُ ٱنفِرُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ٱثَّاقَلۡتُمۡ إِلَى ٱلۡأَرۡضِۚ أَرَضِيتُم بِٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا مِنَ ٱلۡأٓخِرَةِۚ فَمَا مَتَٰعُ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا فِي ٱلۡأٓخِرَةِ إِلَّا قَلِيلٌ

Ya ku waxanda suka yi imani, me ya same ku ne idan aka ce da ku ku fita yaqi saboda Allah sai ku yi nauyin jiki? Yanzu kun zavi rayuwar duniya a kan ta lahira? Ai jin daxin rayuwar duniya abu ne qanqani dangane da na lahira



السورة: Suratut Tauba

الآية : 39

إِلَّا تَنفِرُواْ يُعَذِّبۡكُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا وَيَسۡتَبۡدِلۡ قَوۡمًا غَيۡرَكُمۡ وَلَا تَضُرُّوهُ شَيۡـٔٗاۗ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Idan ba za ku fita (yaqi ba to (Allah) zai azabtar da ku da azaba mai raxaxi, Ya kuma canja wasu mutanen daban, ba kuwa za ku cutar da Shi da komai ba. Allah kuwa Mai iko ne a kan komai



السورة: Suratut Tauba

الآية : 40

إِلَّا تَنصُرُوهُ فَقَدۡ نَصَرَهُ ٱللَّهُ إِذۡ أَخۡرَجَهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ثَانِيَ ٱثۡنَيۡنِ إِذۡ هُمَا فِي ٱلۡغَارِ إِذۡ يَقُولُ لِصَٰحِبِهِۦ لَا تَحۡزَنۡ إِنَّ ٱللَّهَ مَعَنَاۖ فَأَنزَلَ ٱللَّهُ سَكِينَتَهُۥ عَلَيۡهِ وَأَيَّدَهُۥ بِجُنُودٖ لَّمۡ تَرَوۡهَا وَجَعَلَ كَلِمَةَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلسُّفۡلَىٰۗ وَكَلِمَةُ ٱللَّهِ هِيَ ٱلۡعُلۡيَاۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٌ

Idan ba ku taimake shi ba (watau Manzon Allah) to haqiqa Allah Ya taimake shi lokacin da kafirai suka fitar da shi (daga Makka), alhalin suna su biyu, lokacin da suke a cikin kogo, yayin da yake ce wa abokinsa (Abubakar): “Kada ka damu, lalle Allah yana tare da mu,” sai Allah Ya saukar masa da nutsuwarsa Ya kuma qarfafe shi da runduna wadda ba ku gan ta ba, Ya kuma sanya kalmar waxanda suka kafirta ta zama qaskantacciya. Kalmar Allah kuwa ita ce maxaukakiya. Allah kuma Mabuwayi ne, Mai hikima



السورة: Suratut Tauba

الآية : 41

ٱنفِرُواْ خِفَافٗا وَثِقَالٗا وَجَٰهِدُواْ بِأَمۡوَٰلِكُمۡ وَأَنفُسِكُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Ku fita yaqi kuna da kuzari ko ba ku da shi, ku kuma yi yaqi da dukiyoyinku da kawunanku saboda Allah. Wannan ya fi alheri a gare ku, in kun kasance kun san (haka)



السورة: Suratut Tauba

الآية : 42

لَوۡ كَانَ عَرَضٗا قَرِيبٗا وَسَفَرٗا قَاصِدٗا لَّٱتَّبَعُوكَ وَلَٰكِنۢ بَعُدَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلشُّقَّةُۚ وَسَيَحۡلِفُونَ بِٱللَّهِ لَوِ ٱسۡتَطَعۡنَا لَخَرَجۡنَا مَعَكُمۡ يُهۡلِكُونَ أَنفُسَهُمۡ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ إِنَّهُمۡ لَكَٰذِبُونَ

Da (abin da za su samu) amfani ne na kusa, ko tafiya gajeriya, to lalle da sun bi ka, sai dai kuma tafiyar ta yi musu tsawo; kuma za su zo suna rantsuwa da Allah cewa: “Da mun sami hali da lalle mun fita tare da ku[1]”, suna hallaka kansu ne kawai, Allah kuwa Yana sane da cewa lalle su tabbas maqaryata ne


1- Watau zuwa yaqin Tabuka.


السورة: Suratut Tauba

الآية : 43

عَفَا ٱللَّهُ عَنكَ لِمَ أَذِنتَ لَهُمۡ حَتَّىٰ يَتَبَيَّنَ لَكَ ٱلَّذِينَ صَدَقُواْ وَتَعۡلَمَ ٱلۡكَٰذِبِينَ

Allah Ya yafe maka; don me ka yi musu izini? Ai har sai ka gane musu gaskiya ka kuma san maqaryata



السورة: Suratut Tauba

الآية : 44

لَا يَسۡتَـٔۡذِنُكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ أَن يُجَٰهِدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلۡمُتَّقِينَ

Waxanda suka yi imani da Allah da ranar lahira ba sa neman izininka don kada su yi yaqi da dukiyoyinsu da kawunansu. Allah kuwa yana sane da masu taqawa



السورة: Suratut Tauba

الآية : 45

إِنَّمَا يَسۡتَـٔۡذِنُكَ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَٱرۡتَابَتۡ قُلُوبُهُمۡ فَهُمۡ فِي رَيۡبِهِمۡ يَتَرَدَّدُونَ

Waxanda kawai suke neman izininka su ne waxanda ba sa imani da Allah da ranar lahira, zukatansu kuma suka yi kokwanto, saboda haka suke ta dawurwuri a cikin kokwantonsu



السورة: Suratut Tauba

الآية : 46

۞وَلَوۡ أَرَادُواْ ٱلۡخُرُوجَ لَأَعَدُّواْ لَهُۥ عُدَّةٗ وَلَٰكِن كَرِهَ ٱللَّهُ ٱنۢبِعَاثَهُمۡ فَثَبَّطَهُمۡ وَقِيلَ ٱقۡعُدُواْ مَعَ ٱلۡقَٰعِدِينَ

Da kuwa sun yi niyyar fita to da sun yi masa tanadi, sai dai kuma Allah Ya qi zaburar da su, sai Ya dankwafar da su, aka kuma ce (da su): “Ku zauna tare da mazauna (gida)[1].”


1- Watau mata da yara da marasa lafiya da masu lalura waxanda ba za su iya fita yaqi ba.


السورة: Suratut Tauba

الآية : 47

لَوۡ خَرَجُواْ فِيكُم مَّا زَادُوكُمۡ إِلَّا خَبَالٗا وَلَأَوۡضَعُواْ خِلَٰلَكُمۡ يَبۡغُونَكُمُ ٱلۡفِتۡنَةَ وَفِيكُمۡ سَمَّـٰعُونَ لَهُمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Da sun fito cikinku xin, to ba abin da za su qare ku da shi sai tavarvarewa, kuma lalle da sun yi ta shige da fice a tsakaninku suna qoqarin haifar muku da fitina, a cikinku kuma akwai masu jiyo musu (wato abokan gaba) magana. Allah kuwa Masanin azzalumai ne



السورة: Suratut Tauba

الآية : 48

لَقَدِ ٱبۡتَغَوُاْ ٱلۡفِتۡنَةَ مِن قَبۡلُ وَقَلَّبُواْ لَكَ ٱلۡأُمُورَ حَتَّىٰ جَآءَ ٱلۡحَقُّ وَظَهَرَ أَمۡرُ ٱللَّهِ وَهُمۡ كَٰرِهُونَ

Haqiqa tun da can sun nemi yaxa fitina, suka hargitsa maka al’amura, har sai da gaskiya ta zo, al’amarin Allah kuma ya bayyana, su kuwa suna masu qin (haka)



السورة: Suratut Tauba

الآية : 49

وَمِنۡهُم مَّن يَقُولُ ٱئۡذَن لِّي وَلَا تَفۡتِنِّيٓۚ أَلَا فِي ٱلۡفِتۡنَةِ سَقَطُواْۗ وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمُحِيطَةُۢ بِٱلۡكَٰفِرِينَ

Daga cikinsu kuma akwai wanda yake cewa: “Ka yi mani izinin (zama), kada ka jefa ni cikin fitina.” Tabbas, ai cikin fitinar suka faxa. Lalle Jahannama kuwa mai kewaye kafirai ce



السورة: Suratut Tauba

الآية : 50

إِن تُصِبۡكَ حَسَنَةٞ تَسُؤۡهُمۡۖ وَإِن تُصِبۡكَ مُصِيبَةٞ يَقُولُواْ قَدۡ أَخَذۡنَآ أَمۡرَنَا مِن قَبۡلُ وَيَتَوَلَّواْ وَّهُمۡ فَرِحُونَ

Idan wani alheri ya same ka sai ya baqanta musu rai; idan kuwa musiba ce ta same ka sai su riqa cewa: “Haqiqa mu da ma tuni mun xauki matakin kauce mata[1],” sai kuma su juya baya suna masu farin ciki


1- Watau da suka qi fita yaqi tare da Manzon Allah ().


السورة: Suratut Tauba

الآية : 51

قُل لَّن يُصِيبَنَآ إِلَّا مَا كَتَبَ ٱللَّهُ لَنَا هُوَ مَوۡلَىٰنَاۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

Ka ce: “Ba abin da zai same mu sai abin da Allah Ya rubuta mana, shi ne Majivincin al’amuranmu; kuma ga Allah kaxai muminai sai su dogara.”



السورة: Suratut Tauba

الآية : 52

قُلۡ هَلۡ تَرَبَّصُونَ بِنَآ إِلَّآ إِحۡدَى ٱلۡحُسۡنَيَيۡنِۖ وَنَحۡنُ نَتَرَبَّصُ بِكُمۡ أَن يُصِيبَكُمُ ٱللَّهُ بِعَذَابٖ مِّنۡ عِندِهِۦٓ أَوۡ بِأَيۡدِينَاۖ فَتَرَبَّصُوٓاْ إِنَّا مَعَكُم مُّتَرَبِّصُونَ

Ka ce: “Shin akwai abin da kuke jira ya same mu in ban da xayan kyawawan abubuwa biyu (wato nasara ko shahada). Mu kuwa muna jiran (mu ga) Allah Ya aukar muku da wata azaba daga wurinsa ko kuwa ta hannunmu? To sai ku jira, lalle mu ma masu jira ne tare da ku.”



السورة: Suratut Tauba

الآية : 53

قُلۡ أَنفِقُواْ طَوۡعًا أَوۡ كَرۡهٗا لَّن يُتَقَبَّلَ مِنكُمۡ إِنَّكُمۡ كُنتُمۡ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ

Ka ce: “Ku ciyar (da dukiyarku) cikin daxin rai ko a bisa dole (duka xai suke), ba za a karva muku ba; don kuwa lalle kun kasance ku mutane ne fasiqai.”



السورة: Suratut Tauba

الآية : 54

وَمَا مَنَعَهُمۡ أَن تُقۡبَلَ مِنۡهُمۡ نَفَقَٰتُهُمۡ إِلَّآ أَنَّهُمۡ كَفَرُواْ بِٱللَّهِ وَبِرَسُولِهِۦ وَلَا يَأۡتُونَ ٱلصَّلَوٰةَ إِلَّا وَهُمۡ كُسَالَىٰ وَلَا يُنفِقُونَ إِلَّا وَهُمۡ كَٰرِهُونَ

Ba kuwa abin da yah ana a karvi ciyarwar tasu sai don sun kafirce wa Allah da Manzonsa, ba sa kuma zuwa salla sai suna cikin kasala, ba sa kuma sa ciyarwa sai aka tilas,



السورة: Suratut Tauba

الآية : 55

فَلَا تُعۡجِبۡكَ أَمۡوَٰلُهُمۡ وَلَآ أَوۡلَٰدُهُمۡۚ إِنَّمَا يُرِيدُ ٱللَّهُ لِيُعَذِّبَهُم بِهَا فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَتَزۡهَقَ أَنفُسُهُمۡ وَهُمۡ كَٰفِرُونَ

To kada dukiyoyinsu da ‘ya’yansu su qayatar da kai. Allah Yana nufin kawai Ya azabta su ne da su a rayuwar duniya, rayukansu kuma su zazzago a halin suna kafirai



السورة: Suratut Tauba

الآية : 56

وَيَحۡلِفُونَ بِٱللَّهِ إِنَّهُمۡ لَمِنكُمۡ وَمَا هُم مِّنكُمۡ وَلَٰكِنَّهُمۡ قَوۡمٞ يَفۡرَقُونَ

Sukan kuma rantse da Allah cewa lalle suna tare da ku, alhali kuwa ba sa tare da ku, kawai dai su wasu mutane ne matsorata



السورة: Suratut Tauba

الآية : 57

لَوۡ يَجِدُونَ مَلۡجَـًٔا أَوۡ مَغَٰرَٰتٍ أَوۡ مُدَّخَلٗا لَّوَلَّوۡاْ إِلَيۡهِ وَهُمۡ يَجۡمَحُونَ

Da za su sami wata mafaka ko wani kogo ko wata mashiga, to da sun juya zuwa gare shi suna gaggawar (shiga)



السورة: Suratut Tauba

الآية : 58

وَمِنۡهُم مَّن يَلۡمِزُكَ فِي ٱلصَّدَقَٰتِ فَإِنۡ أُعۡطُواْ مِنۡهَا رَضُواْ وَإِن لَّمۡ يُعۡطَوۡاْ مِنۡهَآ إِذَا هُمۡ يَسۡخَطُونَ

Daga cikinsu kuma akwai waxanda suke aibata ka game da rabon sadaka; idan an ba su wani abu daga cikinta to sai su gamsu, idan kuwa ba a ba su daga cikinta ba sai ka gan su suna fushi



السورة: Suratut Tauba

الآية : 59

وَلَوۡ أَنَّهُمۡ رَضُواْ مَآ ءَاتَىٰهُمُ ٱللَّهُ وَرَسُولُهُۥ وَقَالُواْ حَسۡبُنَا ٱللَّهُ سَيُؤۡتِينَا ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦ وَرَسُولُهُۥٓ إِنَّآ إِلَى ٱللَّهِ رَٰغِبُونَ

Da kuwa za su yarda da abin da Allah da Manzonsa suka ba su, su kuma ce: “Allah ya ishe mu, kuma Allah zai ba mu daga falalarsa Manzonsa ma (zai ba mu), lalle mu masu kwaxayi ne a wurin Allah kaxai.”



السورة: Suratut Tauba

الآية : 60

۞إِنَّمَا ٱلصَّدَقَٰتُ لِلۡفُقَرَآءِ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱلۡعَٰمِلِينَ عَلَيۡهَا وَٱلۡمُؤَلَّفَةِ قُلُوبُهُمۡ وَفِي ٱلرِّقَابِ وَٱلۡغَٰرِمِينَ وَفِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِۖ فَرِيضَةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

Dukiyoyin zakka na matalauta ne kaxai da miskinai da ma’aikatanta[1] da waxanda ake lallashin zukatansu da kuma game da ‘yanta bayi da waxanda ake bi bashi da kuma wajen jihadi saboda Allah da matafiyi. Farilla ce daga Allah. Allah kuwa Masani ne, Mai hikima


1- Su ne waxanda aka wakilta wajen karvo ta da kula da ita da rarraba wa mabuqata.