السورة: Suratul Qamar

الآية : 31

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ فَكَانُواْ كَهَشِيمِ ٱلۡمُحۡتَظِرِ

Lalle Mun aika musu da tsawa guda xaya, sai suka zamo kamar duddugar ciyawa a garken makiyayi



السورة: Suratul Qamar

الآية : 32

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



السورة: Suratul Qamar

الآية : 33

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطِۭ بِٱلنُّذُرِ

Mutanen Luxu sun qaryata gargaxi



السورة: Suratul Qamar

الآية : 34

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٖۖ نَّجَّيۡنَٰهُم بِسَحَرٖ

Lalle Mun aika musu da iska cike da duwatsu (ta hallaka su), sai dai iyalin Luxu kaxai Muka tserar da su a lokacin asuba



السورة: Suratul Qamar

الآية : 35

نِّعۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَاۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي مَن شَكَرَ

(Wannan) ni’ima ce daga wurinmu. Kamar haka Muke saka wa wanda ya yi godiya



السورة: Suratul Qamar

الآية : 36

وَلَقَدۡ أَنذَرَهُم بَطۡشَتَنَا فَتَمَارَوۡاْ بِٱلنُّذُرِ

Kuma haqiqa ya tsoratar da su irin damqarmu, sai suka yi jayayya da gargaxin (da ya yi musu)



السورة: Suratul Qamar

الآية : 37

وَلَقَدۡ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيۡفِهِۦ فَطَمَسۡنَآ أَعۡيُنَهُمۡ فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ

Haqiqa kuma sun nemi baqinsa[1] da lalata, sai Muka shafe idanuwansu, (Muka ce da su): “Sai ku xanxani azabata da gargaxina.


1- Su ne mala’iku da suka zo masa a siffar mutane matasa kyawawa.


السورة: Suratul Qamar

الآية : 38

وَلَقَدۡ صَبَّحَهُم بُكۡرَةً عَذَابٞ مُّسۡتَقِرّٞ

Haqiqa kuma azaba matabbaciya ta yi musu sammako da asuba.



السورة: Suratul Qamar

الآية : 39

فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ

Saboda haka ku xanxani azabata da gargaxina.”



السورة: Suratul Qamar

الآية : 40

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



السورة: Suratul Qamar

الآية : 41

وَلَقَدۡ جَآءَ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ ٱلنُّذُرُ

Kuma haqiqa gargaxi ya zo wa mutanen Fir’auna



السورة: Suratul Qamar

الآية : 42

كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذۡنَٰهُمۡ أَخۡذَ عَزِيزٖ مُّقۡتَدِرٍ

Suka qaryata ayoyinmu dukkaninsu, sai Muka kama su irin kamu na Mabuwayi, Mai iko



السورة: Suratul Qamar

الآية : 43

أَكُفَّارُكُمۡ خَيۡرٞ مِّنۡ أُوْلَـٰٓئِكُمۡ أَمۡ لَكُم بَرَآءَةٞ فِي ٱلزُّبُرِ

Yanzu kafiranku (ku mutanen Makka) su ne suka fi waxancan alheri, ko kuwa kuna da wata hanya ta kuvuta ne a cikin littattafan da aka saukar?



السورة: Suratul Qamar

الآية : 44

أَمۡ يَقُولُونَ نَحۡنُ جَمِيعٞ مُّنتَصِرٞ

A’a, suna dai cewa ne: “Mu jama’a ce wadda za ta ci nasara.”



السورة: Suratul Qamar

الآية : 45

سَيُهۡزَمُ ٱلۡجَمۡعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ

To ba da daxewa ba za a karya jama’ar tasu[1], su kuma su ba da baya


1- Haka kuwa ya faru a yaqin Badar lokacin da aka karya lagon kafiran Makka, aka kashe manyansu da dama.


السورة: Suratul Qamar

الآية : 46

بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوۡعِدُهُمۡ وَٱلسَّاعَةُ أَدۡهَىٰ وَأَمَرُّ

A’a, alqiyama ita ce lokacin yi musu azaba, alqiyama kuwa ita ta fi bala’i, ta kuma fi xaci



السورة: Suratul Qamar

الآية : 47

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٖ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin vata da azabar wuta



السورة: Suratul Qamar

الآية : 48

يَوۡمَ يُسۡحَبُونَ فِي ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ ذُوقُواْ مَسَّ سَقَرَ

Ranar da za a ja su cikin wuta a kan fuskokinsu (a ce da su): “Ku xanxani azabar wutar Saqara.”



السورة: Suratul Qamar

الآية : 49

إِنَّا كُلَّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَٰهُ بِقَدَرٖ

Lalle Mu, kowane abu Mun halitta shi da qaddara



السورة: Suratul Qamar

الآية : 50

وَمَآ أَمۡرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٞ كَلَمۡحِۭ بِٱلۡبَصَرِ

Kuma al’amarinmu bai zamanto ba face kalma xaya kamar qiftawar ido



السورة: Suratul Qamar

الآية : 51

وَلَقَدۡ أَهۡلَكۡنَآ أَشۡيَاعَكُمۡ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun hallakar da ire-irenku[1], to ko akwai mai wa’azantuwa?


1- Watau kafirai irinsu masu taurin kai.


السورة: Suratul Qamar

الآية : 52

وَكُلُّ شَيۡءٖ فَعَلُوهُ فِي ٱلزُّبُرِ

Kuma kowane abu da suka aikata yana cikin littattafai



السورة: Suratul Qamar

الآية : 53

وَكُلُّ صَغِيرٖ وَكَبِيرٖ مُّسۡتَطَرٌ

Kowane qaramin abu da babba kuma suna nan a rubuce



السورة: Suratul Qamar

الآية : 54

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَنَهَرٖ

Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da qoramu



السورة: Suratul Qamar

الآية : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko