السورة: Suratux Xur

الآية : 31

قُلۡ تَرَبَّصُواْ فَإِنِّي مَعَكُم مِّنَ ٱلۡمُتَرَبِّصِينَ

Ka ce, “To ku saurara, ni ma lalle ina cikin masu sauraron.”



السورة: Suratux Xur

الآية : 32

أَمۡ تَأۡمُرُهُمۡ أَحۡلَٰمُهُم بِهَٰذَآۚ أَمۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ

Ko kuwa hankullansu ne suke umartar su da wannan? A’a, su dai mutane ne masu tsaurin kai



السورة: Suratux Xur

الآية : 33

أَمۡ يَقُولُونَ تَقَوَّلَهُۥۚ بَل لَّا يُؤۡمِنُونَ

Ko kuwa suna cewa: “Ya qago shi?” A’a, su dai ba sa yin imani ne kawai



السورة: Suratux Xur

الآية : 34

فَلۡيَأۡتُواْ بِحَدِيثٖ مِّثۡلِهِۦٓ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ

To su zo da wani zance irinsa idan sun kasance masu gaskiya



السورة: Suratux Xur

الآية : 35

أَمۡ خُلِقُواْ مِنۡ غَيۡرِ شَيۡءٍ أَمۡ هُمُ ٱلۡخَٰلِقُونَ

Ko kuwa an halicce su ne ba da wani mai halitta ba, ko kuwa su ne masu halittar (kansu)?



السورة: Suratux Xur

الآية : 36

أَمۡ خَلَقُواْ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَۚ بَل لَّا يُوقِنُونَ

Ko kuwa su suka halicci sammai da qasa? A’a, ba sa dai sakankancewa ne



السورة: Suratux Xur

الآية : 37

أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَبِّكَ أَمۡ هُمُ ٱلۡمُصَۜيۡطِرُونَ

Ko kuwa taskokin Ubangijinka suna wurinsu ne, ko kuwa su ne masu iko?



السورة: Suratux Xur

الآية : 38

أَمۡ لَهُمۡ سُلَّمٞ يَسۡتَمِعُونَ فِيهِۖ فَلۡيَأۡتِ مُسۡتَمِعُهُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ

Ko kuwa suna da wani tsani ne da suke jiyo (zancen Allah) ta kansa[1]? To mai jiyowar tasu ya zo da wata hujja mabayyaniya


1- Watau cewa su ne masu gaskiya, Annabi () maqaryaci ne?


السورة: Suratux Xur

الآية : 39

أَمۡ لَهُ ٱلۡبَنَٰتُ وَلَكُمُ ٱلۡبَنُونَ

Ko kuwa Shi ne zai zama mai ‘ya’ya mata, ku kuwa ku zamanto da ‘ya’ya maza?



السورة: Suratux Xur

الآية : 40

أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ

Ko kuwa kana tambayar su wani lada ne, saboda haka bashi ya yi musu nauyi?



السورة: Suratux Xur

الآية : 41

أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko kuwa sun san gaibu ne, saboda haka su ne suke rubutawa



السورة: Suratux Xur

الآية : 42

أَمۡ يُرِيدُونَ كَيۡدٗاۖ فَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ هُمُ ٱلۡمَكِيدُونَ

Ko kuwa suna nufin (yi maka) makirci ne? To waxanda suka kafirce su ne waxanda makircinsu zai kama su



السورة: Suratux Xur

الآية : 43

أَمۡ لَهُمۡ إِلَٰهٌ غَيۡرُ ٱللَّهِۚ سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ko kuwa suna da wani abin bauta ne ba Allah ba? Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke tara (Shi da shi)



السورة: Suratux Xur

الآية : 44

وَإِن يَرَوۡاْ كِسۡفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ سَاقِطٗا يَقُولُواْ سَحَابٞ مَّرۡكُومٞ

Da kuwa za su ga wani yanki na azaba mai faxowa daga sama da sai su ce: “Hadari ne haxaxxe.”



السورة: Suratux Xur

الآية : 45

فَذَرۡهُمۡ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي فِيهِ يُصۡعَقُونَ

To ka rabu da su har sai sun haxu da ranarsu wadda za a karvi rayukansu a cikinta



السورة: Suratux Xur

الآية : 46

يَوۡمَ لَا يُغۡنِي عَنۡهُمۡ كَيۡدُهُمۡ شَيۡـٔٗا وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Ranar da makircinsu ba zai maganta musu komai ba, kuma su ba za a taimake su ba



السورة: Suratux Xur

الآية : 47

وَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ عَذَابٗا دُونَ ذَٰلِكَ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Lalle kuma waxanda suka yi zalunci suna da wata azabar daban[1] ban da wannan (ta lahira), sai dai kuma mafi yawansu ba su sani ba


1- Watau a nan duniya ta hanyar kisa a wajen yaqi ko kamu a matsayin ribatattu ko kuma azabar qabari bayan sun mutu.


السورة: Suratux Xur

الآية : 48

وَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ فَإِنَّكَ بِأَعۡيُنِنَاۖ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ حِينَ تَقُومُ

Kuma ka yi haquri da hukuncin Ubangijika, don ko lalle kana qarqashin lurarmu; kuma ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka lokacin da za ka tashi (daga bacci)



السورة: Suratux Xur

الآية : 49

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡهُ وَإِدۡبَٰرَ ٱلنُّجُومِ

Da daddare kuma sai ka tsarkake Shi da kuma lokacin da taurari suka ba da baya