السورة: Suratu Muhammad

الآية : 31

وَلَنَبۡلُوَنَّكُمۡ حَتَّىٰ نَعۡلَمَ ٱلۡمُجَٰهِدِينَ مِنكُمۡ وَٱلصَّـٰبِرِينَ وَنَبۡلُوَاْ أَخۡبَارَكُمۡ

Kuma tabbas za Mu jarraba ku har sai Mun bayyana masu jihadi daga cikinku, da masu haquri, kuma za Mu bayyana halayenku



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 32

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَصَدُّواْ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ وَشَآقُّواْ ٱلرَّسُولَ مِنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمُ ٱلۡهُدَىٰ لَن يَضُرُّواْ ٱللَّهَ شَيۡـٔٗا وَسَيُحۡبِطُ أَعۡمَٰلَهُمۡ

Lalle waxanda suka kafirta suka kuma toshe hanyar Allah, kuma suka sava wa Manzo bayan shiriya ta bayyana a gare su, to ba za su tava cutar Allah da komai ba, kuma zai lalata ayyukansu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 33

۞يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُواْ ٱلرَّسُولَ وَلَا تُبۡطِلُوٓاْ أَعۡمَٰلَكُمۡ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku bi Allah, kuma ku bi Manzonsa, kada kuma ku vata ayyukanku[1]


1- Watau ta hanyar aikata kafirci ko munafurci ko riya.


السورة: Suratu Muhammad

الآية : 34

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَصَدُّواْ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ ثُمَّ مَاتُواْ وَهُمۡ كُفَّارٞ فَلَن يَغۡفِرَ ٱللَّهُ لَهُمۡ

Lalle waxanda suka kafirta suka kuma toshe hanyar Allah, sannan suka mutu a halin suna kafirai, to Allah ba zai tava gafarta musu ba



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 35

فَلَا تَهِنُواْ وَتَدۡعُوٓاْ إِلَى ٱلسَّلۡمِ وَأَنتُمُ ٱلۡأَعۡلَوۡنَ وَٱللَّهُ مَعَكُمۡ وَلَن يَتِرَكُمۡ أَعۡمَٰلَكُمۡ

To kada ku raunana, kuma kada ku kirawo su zuwa sulhu[1], alhali ku ne a sama, Allah kuwa Yana tare da ku, kuma ba zai tauye muku ayyukanku ba


1- Watau gabanin su kafiran su nuna suna son sulhu.


السورة: Suratu Muhammad

الآية : 36

إِنَّمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَا لَعِبٞ وَلَهۡوٞۚ وَإِن تُؤۡمِنُواْ وَتَتَّقُواْ يُؤۡتِكُمۡ أُجُورَكُمۡ وَلَا يَسۡـَٔلۡكُمۡ أَمۡوَٰلَكُمۡ

Rayuwar duniya wasa ce da sharholiya kawai. Idan kuwa kuka yi imani kuka kiyaye dokokin Allah, to zai ba ku ladanku, ba kuma zai tambaye ku ku ba da dukiyoyinku (duka) ba



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 37

إِن يَسۡـَٔلۡكُمُوهَا فَيُحۡفِكُمۡ تَبۡخَلُواْ وَيُخۡرِجۡ أَضۡغَٰنَكُمۡ

Don ko idan da zai tambaye ku ita (dukiyar gaba xaya) Ya kuma nace muku, to da sai ku yi rowa, Ya kuma fito da qulle-qullen zukatanku



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 38

هَـٰٓأَنتُمۡ هَـٰٓؤُلَآءِ تُدۡعَوۡنَ لِتُنفِقُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَمِنكُم مَّن يَبۡخَلُۖ وَمَن يَبۡخَلۡ فَإِنَّمَا يَبۡخَلُ عَن نَّفۡسِهِۦۚ وَٱللَّهُ ٱلۡغَنِيُّ وَأَنتُمُ ٱلۡفُقَرَآءُۚ وَإِن تَتَوَلَّوۡاْ يَسۡتَبۡدِلۡ قَوۡمًا غَيۡرَكُمۡ ثُمَّ لَا يَكُونُوٓاْ أَمۡثَٰلَكُم

To ga ku fa ku xin nan ana kiran ku don ku ciyar a hanyar Allah, to daga cikinku akwai masu yin rowa; wanda kuwa duk ya yi rowa, lalle ya yi wa kansa rowa ne. Allah kuma Mawadaci ne, ku ne mabuqata. Idan kuwa kuka ba da baya to zai canja wasu mutanen ba ku ba, sannan ba za su zama kamar ku ba