السورة: Suratu Sad

الآية : 31

إِذۡ عُرِضَ عَلَيۡهِ بِٱلۡعَشِيِّ ٱلصَّـٰفِنَٰتُ ٱلۡجِيَادُ

(Ka tuna) lokacin da aka jera masa ingarmun dawakai masu tsayawa da qafa uku da yamma



السورة: Suratu Sad

الآية : 32

فَقَالَ إِنِّيٓ أَحۡبَبۡتُ حُبَّ ٱلۡخَيۡرِ عَن ذِكۡرِ رَبِّي حَتَّىٰ تَوَارَتۡ بِٱلۡحِجَابِ

Sai ya ce: “Lalle ni na fifita son dukiya (watau dawakai) a kan ambaton Ubangijina (watau sallar La’asar) har sai da (rana) ta faxi.”



السورة: Suratu Sad

الآية : 33

رُدُّوهَا عَلَيَّۖ فَطَفِقَ مَسۡحَۢا بِٱلسُّوقِ وَٱلۡأَعۡنَاقِ

(Ya ce): “Ku dawo min da su;” sai ya riqa saran su ta qafafu da wuyoyi



السورة: Suratu Sad

الآية : 34

وَلَقَدۡ فَتَنَّا سُلَيۡمَٰنَ وَأَلۡقَيۡنَا عَلَىٰ كُرۡسِيِّهِۦ جَسَدٗا ثُمَّ أَنَابَ

Kuma haqiqa Mun jarrabi Sulaimanu Muka xora wani jiki a kan gadonsa na mulki[1], sannan ya koma (kan mulkinsa)


1- Wannan wata jarrrabawa ce da Allah ya yi wa Annabi Sulaimanu () game da mulkinsa, lokacin da ya xora wani jiki a kan kujerarsa ta mulki. Mafi yawan malamai sun ce wani shaixani ne Allah ya ba shi ikon hayewa kujerarsa.


السورة: Suratu Sad

الآية : 35

قَالَ رَبِّ ٱغۡفِرۡ لِي وَهَبۡ لِي مُلۡكٗا لَّا يَنۢبَغِي لِأَحَدٖ مِّنۢ بَعۡدِيٓۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡوَهَّابُ

Ya ce: “Ya Ubangijina, Ka gafarta min, Ka kuma ba ni wani mulki wanda bai kamaci wani ba a bayana ya sami irinsa; lalle Kai Kai ne Mai yawan kyauta.”



السورة: Suratu Sad

الآية : 36

فَسَخَّرۡنَا لَهُ ٱلرِّيحَ تَجۡرِي بِأَمۡرِهِۦ رُخَآءً حَيۡثُ أَصَابَ

Sai Muka hore masa iska tana tafiya da umarninsa a natse duk inda ya fuskanta



السورة: Suratu Sad

الآية : 37

وَٱلشَّيَٰطِينَ كُلَّ بَنَّآءٖ وَغَوَّاصٖ

Da kuma shaixanu masu yin kowane irin gini da kuma masu yin nutso (a ruwa)



السورة: Suratu Sad

الآية : 38

وَءَاخَرِينَ مُقَرَّنِينَ فِي ٱلۡأَصۡفَادِ

Wasu kuma an xaxxaure su cikin maruruwa



السورة: Suratu Sad

الآية : 39

هَٰذَا عَطَآؤُنَا فَٱمۡنُنۡ أَوۡ أَمۡسِكۡ بِغَيۡرِ حِسَابٖ

Wannan kyautarmu ce, to ka yi kyauta ko ka hana ba da wani bincike ba



السورة: Suratu Sad

الآية : 40

وَإِنَّ لَهُۥ عِندَنَا لَزُلۡفَىٰ وَحُسۡنَ مَـَٔابٖ

Lalle kuma shi tabbas yana da kusanci a wurinmu, da kuma kyakkyawar makoma



السورة: Suratu Sad

الآية : 41

وَٱذۡكُرۡ عَبۡدَنَآ أَيُّوبَ إِذۡ نَادَىٰ رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَسَّنِيَ ٱلشَّيۡطَٰنُ بِنُصۡبٖ وَعَذَابٍ

Ka kuma tuna bawanmu Ayyuba lokacin da ya kira Ubangijinsa (yana cewa): “Lalle ni Shaixan ya shafe ni da wata wahala da azaba.”



السورة: Suratu Sad

الآية : 42

ٱرۡكُضۡ بِرِجۡلِكَۖ هَٰذَا مُغۡتَسَلُۢ بَارِدٞ وَشَرَابٞ

(Aka ce da shi): “Ka hauri qasa da qafarka; (sai ruwa ya vuvvugo, aka ce da shi): “Wannan ruwan wanka ne mai sanyi da na sha.”



السورة: Suratu Sad

الآية : 43

وَوَهَبۡنَا لَهُۥٓ أَهۡلَهُۥ وَمِثۡلَهُم مَّعَهُمۡ رَحۡمَةٗ مِّنَّا وَذِكۡرَىٰ لِأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Muka kuma yi masa baiwar iyalinsa da kuma (qarin) wasu kamarsu (na `ya`ya da jikoki) don jin qai daga gare Mu da kuma wa’azi ga masu hankula



السورة: Suratu Sad

الآية : 44

وَخُذۡ بِيَدِكَ ضِغۡثٗا فَٱضۡرِب بِّهِۦ وَلَا تَحۡنَثۡۗ إِنَّا وَجَدۡنَٰهُ صَابِرٗاۚ نِّعۡمَ ٱلۡعَبۡدُ إِنَّهُۥٓ أَوَّابٞ

Ka xauki danqi na ciyawa da hannunka ka bugi (matarka da shi)[1], kada ka karya rantsuwarka. Lalle Mun same shi mai haquri. Madalla da wannan bawan; lalle shi mai yawan komawa ne (ga Allah)


1- Yayin da matarsa ta yi masa laifi ya yi rantsuwa cewa, idan ya warke sai ya yi mata bulala xari. Allah () ya umarce shi da ya cika rantsuwarsa ta wannan hanyar.


السورة: Suratu Sad

الآية : 45

وَٱذۡكُرۡ عِبَٰدَنَآ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ أُوْلِي ٱلۡأَيۡدِي وَٱلۡأَبۡصَٰرِ

Ka kuma tuna bayinmu Ibrahimu da Is’haqa da Yaqubu ma’abota qarfi da basira



السورة: Suratu Sad

الآية : 46

إِنَّآ أَخۡلَصۡنَٰهُم بِخَالِصَةٖ ذِكۡرَى ٱلدَّارِ

Lalle Mun kevance su da wata kevantacciyar xabi’a, (ita ce) tuna lahira



السورة: Suratu Sad

الآية : 47

وَإِنَّهُمۡ عِندَنَا لَمِنَ ٱلۡمُصۡطَفَيۡنَ ٱلۡأَخۡيَارِ

Kuma lalle su a wurinmu tabbas suna daga cikin zavavvu nagari



السورة: Suratu Sad

الآية : 48

وَٱذۡكُرۡ إِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَذَا ٱلۡكِفۡلِۖ وَكُلّٞ مِّنَ ٱلۡأَخۡيَارِ

Ka kuma tuna Isma’ila da Alyasa’u da Zulkifli; dukkaninsu kuma suna cikin zavavvu



السورة: Suratu Sad

الآية : 49

هَٰذَا ذِكۡرٞۚ وَإِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ لَحُسۡنَ مَـَٔابٖ

Wannan kyakkyawan ambato ne (a gare su). Kuma lalle masu taqawa tabbas suna da kyakkyawar makoma



السورة: Suratu Sad

الآية : 50

جَنَّـٰتِ عَدۡنٖ مُّفَتَّحَةٗ لَّهُمُ ٱلۡأَبۡوَٰبُ

(Wato) gidajen Aljannar dawwama, alhali qofofi suna buxe saboda su



السورة: Suratu Sad

الآية : 51

مُتَّكِـِٔينَ فِيهَا يَدۡعُونَ فِيهَا بِفَٰكِهَةٖ كَثِيرَةٖ وَشَرَابٖ

Suna kishingixe a cikinsu, suna kiran a kawo musu ababen marmari masu yawa da abin sha a cikinsu



السورة: Suratu Sad

الآية : 52

۞وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ أَتۡرَابٌ

Kuma a wurinsu akwai tsaraikun mata masu taqaita kallo (ga mazansu kawai)



السورة: Suratu Sad

الآية : 53

هَٰذَا مَا تُوعَدُونَ لِيَوۡمِ ٱلۡحِسَابِ

Wannan shi ne ake yi muku alqawari da shi a ranar hisabi



السورة: Suratu Sad

الآية : 54

إِنَّ هَٰذَا لَرِزۡقُنَا مَا لَهُۥ مِن نَّفَادٍ

Lalle wannan tabbas arzikinmu ne ba mai qarewa ba



السورة: Suratu Sad

الآية : 55

هَٰذَاۚ وَإِنَّ لِلطَّـٰغِينَ لَشَرَّ مَـَٔابٖ

Wannan (shi ne sakamakon masu taqawa). Kuma lalle masu xagawa tabbas suna da mummunar makoma



السورة: Suratu Sad

الآية : 56

جَهَنَّمَ يَصۡلَوۡنَهَا فَبِئۡسَ ٱلۡمِهَادُ

(Wato) Jahannama wadda za su shige ta, to wannan shimfixar zama ta munana



السورة: Suratu Sad

الآية : 57

هَٰذَا فَلۡيَذُوقُوهُ حَمِيمٞ وَغَسَّاقٞ

Wannan (sakamako ne), sai su xanxane shi na tafasasshen ruwa da mugunya



السورة: Suratu Sad

الآية : 58

وَءَاخَرُ مِن شَكۡلِهِۦٓ أَزۡوَٰجٌ

Da kuma wani mai kama da shi iri daban-daban



السورة: Suratu Sad

الآية : 59

هَٰذَا فَوۡجٞ مُّقۡتَحِمٞ مَّعَكُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِهِمۡۚ إِنَّهُمۡ صَالُواْ ٱلنَّارِ

(Za a ce da su): “Wannan ma wani gungun ne (na mabiya) mai afkawa tare da ku;” (sai shugabannin su ce): “Ba ma yin maraba da su.” Lalle (su duka) wuta za su shiga



السورة: Suratu Sad

الآية : 60

قَالُواْ بَلۡ أَنتُمۡ لَا مَرۡحَبَۢا بِكُمۡۖ أَنتُمۡ قَدَّمۡتُمُوهُ لَنَاۖ فَبِئۡسَ ٱلۡقَرَارُ

(Mabiyan kuma sai) su ce: “A’a, ku dai ne ba ma maraba da ku; ku ne kuka kawo mana shi (wannan mummunan sakamako);” to wannan matabbata ta munana