السورة: Suratul Ankabut

الآية : 31

وَلَمَّا جَآءَتۡ رُسُلُنَآ إِبۡرَٰهِيمَ بِٱلۡبُشۡرَىٰ قَالُوٓاْ إِنَّا مُهۡلِكُوٓاْ أَهۡلِ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِۖ إِنَّ أَهۡلَهَا كَانُواْ ظَٰلِمِينَ

Lokacin kuwa da manzanninmu suka zo wa Ibrahimu da albishir[1], sai suka ce: “Lalle mu masu hallaka mutanen wannan alqaryar ne, lalle mutanenta sun kasance azzalumai.”


1- Albishir na samun haihuwar xansa Ishaq () da kuma jikansa Ya’aqub ().


السورة: Suratul Ankabut

الآية : 32

قَالَ إِنَّ فِيهَا لُوطٗاۚ قَالُواْ نَحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَن فِيهَاۖ لَنُنَجِّيَنَّهُۥ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai (Ibrahimu) ya ce: “Lalle Luxu yana cikinta”. Sai suka ce: “Mu muka fi sanin waxanda suke cikinta; tabbas za mu tserar da shi tare da iyalinsa, sai matarsa kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 33

وَلَمَّآ أَن جَآءَتۡ رُسُلُنَا لُوطٗا سِيٓءَ بِهِمۡ وَضَاقَ بِهِمۡ ذَرۡعٗاۖ وَقَالُواْ لَا تَخَفۡ وَلَا تَحۡزَنۡ إِنَّا مُنَجُّوكَ وَأَهۡلَكَ إِلَّا ٱمۡرَأَتَكَ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Lokacin kuma da manzanninmu suka zo wa Luxu, sai ya yi baqin ciki da zuwansu, zuciyarsa kuma ta quntata saboda su[1], sai suka ce da shi: “Kada ka ji tsoro, kuma kada ka damu; lalle mu masu tserar da kai ne tare da iyalinka, sai matarka kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)


1- Domin jiye musu tsoron mugun halin mutanensa musamman saboda mala’ikun sun zo a cikin kamanni na mutane maza.


السورة: Suratul Ankabut

الآية : 34

إِنَّا مُنزِلُونَ عَلَىٰٓ أَهۡلِ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

“Lalle mu masu saukar da azaba ce daga sama a kan mutanen wannan alqaryar saboda abin da suka kasance suna aikatawa na fasiqanci.”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 35

وَلَقَد تَّرَكۡنَا مِنۡهَآ ءَايَةَۢ بَيِّنَةٗ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Kuma haqiqa Mu mun bar aya bayyananniya game da ita (alqaryar) ga mutanen da suke hankalta



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 36

وَإِلَىٰ مَدۡيَنَ أَخَاهُمۡ شُعَيۡبٗا فَقَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَٱرۡجُواْ ٱلۡيَوۡمَ ٱلۡأٓخِرَ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

Mun kuma (aika wa mutanen) Madyana xan’uwansu Shu’aibu, sai ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, kuma ku yi fatan (kyakkyawan samakon) ranar lahira, kada kuma ku riqa yaxa varna a bayan qasa.”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 37

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دَارِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Sai suka qaryata shi, sai girgizar qasa ta kama su, suka wayi gari duddurqushe (matattu) cikin gidajensu



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 38

وَعَادٗا وَثَمُودَاْ وَقَد تَّبَيَّنَ لَكُم مِّن مَّسَٰكِنِهِمۡۖ وَزَيَّنَ لَهُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُ أَعۡمَٰلَهُمۡ فَصَدَّهُمۡ عَنِ ٱلسَّبِيلِ وَكَانُواْ مُسۡتَبۡصِرِينَ

Kuma (Mun hallaka) Adawa da Samudawa, haqiqa (abin da ya faru a gare su) ya bayyana gare ku a fili a gidajensu; kuma Shaixan ya qawata musu ayyukansu, sai ya kange su daga hanya (madaidaiciya), sun kuma kasance masu gani da basirarsu (amma suka zavi vata)



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 39

وَقَٰرُونَ وَفِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مُّوسَىٰ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَٱسۡتَكۡبَرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا كَانُواْ سَٰبِقِينَ

Kuma (Mun hallaka) Qaruna da Fir’auna da Hamana; haqiqa kuma Musa ya zo musu da hujjoji bayyanannu, sai suka yi girman kai a bayan qasa, kuma ba su kasance masu guje wa (azaba) ba



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 40

فَكُلًّا أَخَذۡنَا بِذَنۢبِهِۦۖ فَمِنۡهُم مَّنۡ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِ حَاصِبٗا وَمِنۡهُم مَّنۡ أَخَذَتۡهُ ٱلصَّيۡحَةُ وَمِنۡهُم مَّنۡ خَسَفۡنَا بِهِ ٱلۡأَرۡضَ وَمِنۡهُم مَّنۡ أَغۡرَقۡنَاۚ وَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيَظۡلِمَهُمۡ وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Kowanne (cikin al’ummun da suka gabata) Mun kama shi da laifinsa; daga cikinsu akwai waxanda Muka aiko wa da duwatsu, akwai kuma waxanda tsawa ta kama su, kuma daga cikinsu akwai waxanda Muka kifar da su cikin qasa, akwai kuma daga cikinsu waxanda Muka nutsar a ruwa. Allah kuma bai kasance Yana zaluntar su ba, sai dai kawai kawunansu suke zalunta



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 41

مَثَلُ ٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِ ٱللَّهِ أَوۡلِيَآءَ كَمَثَلِ ٱلۡعَنكَبُوتِ ٱتَّخَذَتۡ بَيۡتٗاۖ وَإِنَّ أَوۡهَنَ ٱلۡبُيُوتِ لَبَيۡتُ ٱلۡعَنكَبُوتِۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Misalin waxanda suka riqi wasu iyayen giji ba Allah ba, kamar misalin gizo-gizo ne da ya saqa gida; haqiqa kuwa lalle gidan gizo-gizo shi ya fi kowanne gida rauni, da sun kasance suna sanin (haka)



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 42

إِنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ مِن شَيۡءٖۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Lalle Allah Yana sane da kowane abu da suke bauta wa wanda ba Shi ba. Kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 43

وَتِلۡكَ ٱلۡأَمۡثَٰلُ نَضۡرِبُهَا لِلنَّاسِۖ وَمَا يَعۡقِلُهَآ إِلَّا ٱلۡعَٰلِمُونَ

Waxancan misalan Muna ba da su ne ga mutane; ba kuwa wanda yake hankaltar su sai malamai kawai



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 44

خَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Allah Ya halicci sammai da qasa da gaskiya. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga muminai



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 45

ٱتۡلُ مَآ أُوحِيَ إِلَيۡكَ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَۖ إِنَّ ٱلصَّلَوٰةَ تَنۡهَىٰ عَنِ ٱلۡفَحۡشَآءِ وَٱلۡمُنكَرِۗ وَلَذِكۡرُ ٱللَّهِ أَكۡبَرُۗ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تَصۡنَعُونَ

Ka karanta abin da ake yi maka wahayinsa na Alqur’ani, ka kuma tsai da salla; lalle salla tana hana alfasha da kuma abin qi. Kuma tabbas ambaton Allah shi ne mafi girma. Kuma Allah Yana sane da abin da kuke aikatawa



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 46

۞وَلَا تُجَٰدِلُوٓاْ أَهۡلَ ٱلۡكِتَٰبِ إِلَّا بِٱلَّتِي هِيَ أَحۡسَنُ إِلَّا ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡهُمۡۖ وَقُولُوٓاْ ءَامَنَّا بِٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡنَا وَأُنزِلَ إِلَيۡكُمۡ وَإِلَٰهُنَا وَإِلَٰهُكُمۡ وَٰحِدٞ وَنَحۡنُ لَهُۥ مُسۡلِمُونَ

Kuma kada ku yi jayayya da ma’abota littafi (Yahudu da Nasara) sai ta hanyar da ta fi kyau, sai dai waxanda suka yi zalunci daga cikinsu; kuma ku ce: “Mun yi imani da abin da aka saukar mana da kuma abin da aka saukar muku, kuma Abin bautarmu da Abin bautarku Xaya ne, kuma mu masu miqa wuya ne gare Shi.”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 47

وَكَذَٰلِكَ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَۚ فَٱلَّذِينَ ءَاتَيۡنَٰهُمُ ٱلۡكِتَٰبَ يُؤۡمِنُونَ بِهِۦۖ وَمِنۡ هَـٰٓؤُلَآءِ مَن يُؤۡمِنُ بِهِۦۚ وَمَا يَجۡحَدُ بِـَٔايَٰتِنَآ إِلَّا ٱلۡكَٰفِرُونَ

Kamar haka kuma Muka saukar maka da Alqur’ani. To waxanda Muka bai wa littafi (a gabaninka) suna imani da shi; daga waxannan kuma (wato mutanen Makka) akwai wanda yake imani da shi. Ba kuwa mai musun ayoyinmu sai kafirai



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 48

وَمَا كُنتَ تَتۡلُواْ مِن قَبۡلِهِۦ مِن كِتَٰبٖ وَلَا تَخُطُّهُۥ بِيَمِينِكَۖ إِذٗا لَّٱرۡتَابَ ٱلۡمُبۡطِلُونَ

Ba ka zamanto kuma kana karanta wani littafi kafinsa ba (wato Alkur’ani), kuma ba ka rubuta shi da hannun damanka; da kuwa haka ya faru, to da sai masu qaryatawa su shiga kokwanto



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 49

بَلۡ هُوَ ءَايَٰتُۢ بَيِّنَٰتٞ فِي صُدُورِ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَۚ وَمَا يَجۡحَدُ بِـَٔايَٰتِنَآ إِلَّا ٱلظَّـٰلِمُونَ

A’a, shi dai (Alqur’ani) ayoyi ne bayyanannu (da suke) cikin zukatan waxanda aka bai wa ilimi. Ba kuwa mai yin musun ayoyinmu sai azzalumai



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 50

وَقَالُواْ لَوۡلَآ أُنزِلَ عَلَيۡهِ ءَايَٰتٞ مِّن رَّبِّهِۦۚ قُلۡ إِنَّمَا ٱلۡأٓيَٰتُ عِندَ ٱللَّهِ وَإِنَّمَآ أَنَا۠ نَذِيرٞ مُّبِينٌ

Suka kuma ce: “Me ya hana a saukar masa da wasu ayoyi daga Ubangijinsa?” Ka ce (da su): “Ayoyi suna wurin Allah ne kawai, ni kuma ba kowa ba ne face mai gargaxi, mai bayyana (gargaxin).”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 51

أَوَلَمۡ يَكۡفِهِمۡ أَنَّآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ يُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَرَحۡمَةٗ وَذِكۡرَىٰ لِقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Yanzu bai ishe su ba cewa, Mun saukar maka da Littafi da ake karanta musu shi? Lalle a game da wannan tabbas akwai rahama da kuma tunatarwa ga mutanen da suke yin imani



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 52

قُلۡ كَفَىٰ بِٱللَّهِ بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡ شَهِيدٗاۖ يَعۡلَمُ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱلۡبَٰطِلِ وَكَفَرُواْ بِٱللَّهِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Ka ce (da su): “Allah Ya isa shaida tsakanina da ku; Yana sane da abin da yake cikin sammai da qasa. Waxanda kuwa suka yi imani da qarya suka kuma kafirce wa Allah, waxannan su ne asararru.”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 53

وَيَسۡتَعۡجِلُونَكَ بِٱلۡعَذَابِ وَلَوۡلَآ أَجَلٞ مُّسَمّٗى لَّجَآءَهُمُ ٱلۡعَذَابُۚ وَلَيَأۡتِيَنَّهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Suna kuma neman ka da ka gaggauto musu da azaba. Ba don kuwa akwai lokaci na musamman (da aka tanada) ba, tabbas da azabar ta zo musu, kuma tabbas da za ta zo musu ne ba zato ba tsammani, alhali ba su sani ba



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 54

يَسۡتَعۡجِلُونَكَ بِٱلۡعَذَابِ وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمُحِيطَةُۢ بِٱلۡكَٰفِرِينَ

Suna (kuma) neman ka da ka gaggauto musu da azaba, alhali kuwa Jahannama tabbas mai kewaye kafirai ce



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 55

يَوۡمَ يَغۡشَىٰهُمُ ٱلۡعَذَابُ مِن فَوۡقِهِمۡ وَمِن تَحۡتِ أَرۡجُلِهِمۡ وَيَقُولُ ذُوقُواْ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

A ranar da azaba za ta lulluve su ta samansu da ta qarqashin qafafuwansu, kuma (Allah) Ya ce (da su): “Ku xanxani abin da kuka kasance kuna aikatawa.”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 56

يَٰعِبَادِيَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِنَّ أَرۡضِي وَٰسِعَةٞ فَإِيَّـٰيَ فَٱعۡبُدُونِ

Ya ku bayina waxanda suka yi imani, lalle qasata yalwatacciya ce, to Ni kaxai sai ku bauta Mini



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 57

كُلُّ نَفۡسٖ ذَآئِقَةُ ٱلۡمَوۡتِۖ ثُمَّ إِلَيۡنَا تُرۡجَعُونَ

Kowanne rai zai xanxani mutuwa; sannan wurinmu za a mayar da ku



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 58

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَنُبَوِّئَنَّهُم مِّنَ ٱلۡجَنَّةِ غُرَفٗا تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ نِعۡمَ أَجۡرُ ٱلۡعَٰمِلِينَ

Waxanda kuma suka yi imani suka kuma yi aiki nagari, lallai za Mu zaunar da su cikin manya-manyan gidaje a Aljanna (waxanda) qoramu za su riqa gudana ta qarqashinsu suna madawwama a cikinsu. Madalla da ladan masu aiki (nagari)



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 59

ٱلَّذِينَ صَبَرُواْ وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

(Su ne) waxanda suka yi haquri, kuma ga Ubangijinsu kawai suke dogara



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 60

وَكَأَيِّن مِّن دَآبَّةٖ لَّا تَحۡمِلُ رِزۡقَهَا ٱللَّهُ يَرۡزُقُهَا وَإِيَّاكُمۡۚ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Sau tari ga dabba nan da ba za ta iya xaukar arzikinta ba, Allah ne Yake arzuta ta har da ku. Shi ne Mai ji, Masani