السورة: Suratul Baqara

الآية : 31

وَعَلَّمَ ءَادَمَ ٱلۡأَسۡمَآءَ كُلَّهَا ثُمَّ عَرَضَهُمۡ عَلَى ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ فَقَالَ أَنۢبِـُٔونِي بِأَسۡمَآءِ هَـٰٓؤُلَآءِ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Kuma sai (Allah) Ya koya wa Adamu dukkan sunaye (na abubuwa) sannan Ya kawo su gaban mala’iku, sai Ya ce: “Ku faxa min sunayen waxannan abubuwan in kun zamanto masu gaskiya.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 32

قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ لَا عِلۡمَ لَنَآ إِلَّا مَا عَلَّمۡتَنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَلِيمُ ٱلۡحَكِيمُ

Sai suka ce: “Tsarki ya tabbata a gare Ka, ba mu da wani ilimi sai wanda Ka sanar da mu. Lalle Kai ne cikakken Masani, Mai hikima.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 33

قَالَ يَـٰٓـَٔادَمُ أَنۢبِئۡهُم بِأَسۡمَآئِهِمۡۖ فَلَمَّآ أَنۢبَأَهُم بِأَسۡمَآئِهِمۡ قَالَ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ غَيۡبَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَأَعۡلَمُ مَا تُبۡدُونَ وَمَا كُنتُمۡ تَكۡتُمُونَ

Ya ce: “Ya Adamu faxa musu sunayensu.” Yayin da ya faxa musu sunayensu, sai (Allah) Ya ce: “Ba Na faxa muku cewa, lalle Ni ne Nake sane da gaibin sammai da qasa ba, kuma Nake sane da abin da kuke bayyanawa da kuma abin da kuke voyewa ba?”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 34

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ وَٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce wa mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu.” Sai duk suka yi sujjada[1], in ban da Iblis, sai shi ya qi, ya kuma yi girman kai, kuma ya tabbata cikin kafirai


1- Mala’iku sun yi wa Adamu () sujjada ne don biyayya ga umarnin Allah. Ba ya halatta a Musulunci wani ya yi wa wani sujjada ba Allah ba.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 35

وَقُلۡنَا يَـٰٓـَٔادَمُ ٱسۡكُنۡ أَنتَ وَزَوۡجُكَ ٱلۡجَنَّةَ وَكُلَا مِنۡهَا رَغَدًا حَيۡثُ شِئۡتُمَا وَلَا تَقۡرَبَا هَٰذِهِ ٱلشَّجَرَةَ فَتَكُونَا مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma Muka ce: “Ya kai Adamu, ka zauna gidan Aljanna kai da matarka, kuma ku ci (kayan marmarinta) cikin yalwa a duk inda kuka ga dama, kada kuma ku kuskura ku kusanci wannan bishiyar, sai ku kasance daga cikin azzalumai.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 36

فَأَزَلَّهُمَا ٱلشَّيۡطَٰنُ عَنۡهَا فَأَخۡرَجَهُمَا مِمَّا كَانَا فِيهِۖ وَقُلۡنَا ٱهۡبِطُواْ بَعۡضُكُمۡ لِبَعۡضٍ عَدُوّٞۖ وَلَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُسۡتَقَرّٞ وَمَتَٰعٌ إِلَىٰ حِينٖ

Sai Shaixan ya zamar da su[1] game da ita (bishiyar), sai ya fitar da su daga ni’imar da suke ciki. Sai Muka ce: “Ku sauko qasa sashinku yana mai gaba da sashi; kuma kuna da mazauni a bayan qasa da wani jin daxi zuwa wani xan lokaci.”


1- Ta hanyar yi musu waswasi, kamar yadda ya zo a Suratul A’raf, aya ta 20, da Xaha, aya ta 120.


السورة: Suratul Baqara

الآية : 37

فَتَلَقَّىٰٓ ءَادَمُ مِن رَّبِّهِۦ كَلِمَٰتٖ فَتَابَ عَلَيۡهِۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Sai Adamu ya karvi wasu kalmomi daga Ubangijinsa (na neman gafara), sai Ya yafe masa; lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba kuma Mai yawan jin qai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 38

قُلۡنَا ٱهۡبِطُواْ مِنۡهَا جَمِيعٗاۖ فَإِمَّا يَأۡتِيَنَّكُم مِّنِّي هُدٗى فَمَن تَبِعَ هُدَايَ فَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Muka ce: “Dukkanku ku sauko daga cikinta, sannan idan wata shiriyata ta zo muku, to waxanda suka bi shiriyata, babu wani tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



السورة: Suratul Baqara

الآية : 39

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَكَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَآ أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Kuma waxanda suka kafirta suka kuma qaryata ayoyinmu, waxannan su ne ‘yan wuta, su masu dawwama ne a cikinta



السورة: Suratul Baqara

الآية : 40

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَوۡفُواْ بِعَهۡدِيٓ أُوفِ بِعَهۡدِكُمۡ وَإِيَّـٰيَ فَٱرۡهَبُونِ

Ya ku ‘ya’yan Isra’ila, ku tuna ni’imata da Na yi muku, kuma ku cika alqawarina zan cika muku alkawarinku, kuma ku tsorace Ni Ni kaxai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 41

وَءَامِنُواْ بِمَآ أَنزَلۡتُ مُصَدِّقٗا لِّمَا مَعَكُمۡ وَلَا تَكُونُوٓاْ أَوَّلَ كَافِرِۭ بِهِۦۖ وَلَا تَشۡتَرُواْ بِـَٔايَٰتِي ثَمَنٗا قَلِيلٗا وَإِيَّـٰيَ فَٱتَّقُونِ

Kuma ku yi imani da abin da Na saukar yana mai gaskata abin da yake tare da ku (na wahayi), kada kuma ku zama farkon (jinsinku) da zai kafirce masa, kuma kada ku sayar da ayoyina da xan kuxi kaxan, kuma ku kiyaye dokokina



السورة: Suratul Baqara

الآية : 42

وَلَا تَلۡبِسُواْ ٱلۡحَقَّ بِٱلۡبَٰطِلِ وَتَكۡتُمُواْ ٱلۡحَقَّ وَأَنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kada kuma ku gauraya gaskiya da qarya, kuma ku voye gaskiya, alhalin kuna sane



السورة: Suratul Baqara

الآية : 43

وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱرۡكَعُواْ مَعَ ٱلرَّـٰكِعِينَ

Kuma ku tsayar da salla, ku kuma ba da zakka, kuma ku yi ruku’i tare da masu ruku’i



السورة: Suratul Baqara

الآية : 44

۞أَتَأۡمُرُونَ ٱلنَّاسَ بِٱلۡبِرِّ وَتَنسَوۡنَ أَنفُسَكُمۡ وَأَنتُمۡ تَتۡلُونَ ٱلۡكِتَٰبَۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Shin yanzu kwa riqa umartar mutane da ayyukan alheri ku kuma kuna mantawa da kawunanku, alhalin kuna karanta Littafi? Ashe ba za ku hankalta ba?



السورة: Suratul Baqara

الآية : 45

وَٱسۡتَعِينُواْ بِٱلصَّبۡرِ وَٱلصَّلَوٰةِۚ وَإِنَّهَا لَكَبِيرَةٌ إِلَّا عَلَى ٱلۡخَٰشِعِينَ

Kuma ku nemi agaji ta hanyar haquri da kuma salla, kuma lalle ita (salla) babban abu ne sai dai ga masu qasqantar da kai



السورة: Suratul Baqara

الآية : 46

ٱلَّذِينَ يَظُنُّونَ أَنَّهُم مُّلَٰقُواْ رَبِّهِمۡ وَأَنَّهُمۡ إِلَيۡهِ رَٰجِعُونَ

Waxanda suka tabbatar da cewa, su masu haxuwa ne da Ubangijinsu, kuma su zuwa gare Shi suke komawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 47

يَٰبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱذۡكُرُواْ نِعۡمَتِيَ ٱلَّتِيٓ أَنۡعَمۡتُ عَلَيۡكُمۡ وَأَنِّي فَضَّلۡتُكُمۡ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ya ku ‘ya’yan Isra’ila ku tuna ni’imata da Na yi muku, kuma Ni Na fifita ku a kan sauran mutanen duniya (na zamaninku)



السورة: Suratul Baqara

الآية : 48

وَٱتَّقُواْ يَوۡمٗا لَّا تَجۡزِي نَفۡسٌ عَن نَّفۡسٖ شَيۡـٔٗا وَلَا يُقۡبَلُ مِنۡهَا شَفَٰعَةٞ وَلَا يُؤۡخَذُ مِنۡهَا عَدۡلٞ وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ

Kuma ku kiyayi wata rana da babu wani (mai) rai da zai isar wa da wani (mai) rai komai a cikinta; kuma ba za a karvi wani ceto daga gare shi ba, kuma ba za a karvi wata fansa daga gare shi ba, kuma ba za a taimaka musu ba



السورة: Suratul Baqara

الآية : 49

وَإِذۡ نَجَّيۡنَٰكُم مِّنۡ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ يَسُومُونَكُمۡ سُوٓءَ ٱلۡعَذَابِ يُذَبِّحُونَ أَبۡنَآءَكُمۡ وَيَسۡتَحۡيُونَ نِسَآءَكُمۡۚ وَفِي ذَٰلِكُم بَلَآءٞ مِّن رَّبِّكُمۡ عَظِيمٞ

Kuma ku tuna lokacin da Muka kuvutar da ku daga jama’ar Fir’auna waxanda suke xanxana muku mummunar azaba, suna yanka ‘ya’yanku maza, kuma suna qyale ‘ya’yanku mata. A cikin wannan lamari akwai babbar jarraba daga Ubangijinku



السورة: Suratul Baqara

الآية : 50

وَإِذۡ فَرَقۡنَا بِكُمُ ٱلۡبَحۡرَ فَأَنجَيۡنَٰكُمۡ وَأَغۡرَقۡنَآ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ وَأَنتُمۡ تَنظُرُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka raba muku kogi, sai Muka kuvutar da ku, kuma Muka nutsar da jama’ar Fir’auna, alhalin kuna kallo



السورة: Suratul Baqara

الآية : 51

وَإِذۡ وَٰعَدۡنَا مُوسَىٰٓ أَرۡبَعِينَ لَيۡلَةٗ ثُمَّ ٱتَّخَذۡتُمُ ٱلۡعِجۡلَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَنتُمۡ ظَٰلِمُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka yi wa Musa wa’adin (ganawa da shi) na kwana arba’in, sannan ku kuma kuka kama bautar xan maraqi a bayansa, alhalin kuna masu zaluntar kawunanku



السورة: Suratul Baqara

الآية : 52

ثُمَّ عَفَوۡنَا عَنكُم مِّنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Sannan sai Muka yi muku afuwa bayan haka, don ku yi godiya



السورة: Suratul Baqara

الآية : 53

وَإِذۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡفُرۡقَانَ لَعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka ba wa Musa Littafin (Attaura) da abin da yake rarrabewa (tsakanin gaskiya da qarya) don ku shiriya



السورة: Suratul Baqara

الآية : 54

وَإِذۡ قَالَ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ إِنَّكُمۡ ظَلَمۡتُمۡ أَنفُسَكُم بِٱتِّخَاذِكُمُ ٱلۡعِجۡلَ فَتُوبُوٓاْ إِلَىٰ بَارِئِكُمۡ فَٱقۡتُلُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ عِندَ بَارِئِكُمۡ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma ku tuna lokacin da Musa ya cewa mutanensa: “Ya ku mutanena, lalle ku kun zalunci kawunanku ta hanyar mayar da xan maraqi abin bauta, don haka ku tuba zuwa ga Mahaliccinku, kuma ku kashe kawunanku; wannan shi ne ya fi alheri a gare ku a wajen Mahaliccinku. Lalle shi Mai yawan karvar tuba ne, Mai yawan jin qai.”



السورة: Suratul Baqara

الآية : 55

وَإِذۡ قُلۡتُمۡ يَٰمُوسَىٰ لَن نُّؤۡمِنَ لَكَ حَتَّىٰ نَرَى ٱللَّهَ جَهۡرَةٗ فَأَخَذَتۡكُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَأَنتُمۡ تَنظُرُونَ

Kuma ku tuna lokacin da kuka ce: “Ya Musa ba za mu yi imani da kai ba har sai mun ga Allah a sarari”, sai tsawa ta halaka ku, alhali kuma kuna kallo



السورة: Suratul Baqara

الآية : 56

ثُمَّ بَعَثۡنَٰكُم مِّنۢ بَعۡدِ مَوۡتِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Sannan sai Muka tashe ku bayan mutuwarku, don ku yi godiya



السورة: Suratul Baqara

الآية : 57

وَظَلَّلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡغَمَامَ وَأَنزَلۡنَا عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَنَّ وَٱلسَّلۡوَىٰۖ كُلُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا رَزَقۡنَٰكُمۡۚ وَمَا ظَلَمُونَا وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Kuma Muka yi muku inuwa da girgije, kuma Muka saukar muku da mannu da (soyayyun) tsuntsayen salwa, ku ci daga daxaxan abin da Muka arzuta ku da shi; kuma ba su zalince Mu ba, sai dai kawunansu kaxai suke zalunta



السورة: Suratul Baqara

الآية : 58

وَإِذۡ قُلۡنَا ٱدۡخُلُواْ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةَ فَكُلُواْ مِنۡهَا حَيۡثُ شِئۡتُمۡ رَغَدٗا وَٱدۡخُلُواْ ٱلۡبَابَ سُجَّدٗا وَقُولُواْ حِطَّةٞ نَّغۡفِرۡ لَكُمۡ خَطَٰيَٰكُمۡۚ وَسَنَزِيدُ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma ku tuna lokacin da Muka ce: “Ku shiga wannan alqaryar ku ci daga (kayan marmarinta ta) inda kuka ga dama cikin yalwa, kuma ku shiga qofar garin a duqe, kuma ku ce: “(Allah Ka) kankare mana laifuffukanmu”, za Mu gafarta muku laifuffukanku. Kuma za Mu qara wa masu kyautatawa



السورة: Suratul Baqara

الآية : 59

فَبَدَّلَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ قَوۡلًا غَيۡرَ ٱلَّذِي قِيلَ لَهُمۡ فَأَنزَلۡنَا عَلَى ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

Sai waxanda suka yi zalunci suka canza maganar da aka faxa musu, sai Muka saukar da wata azaba daga sama a kan waxanda suka yi zalunci saboda abin da suke aikatawa na fasiqanci



السورة: Suratul Baqara

الآية : 60

۞وَإِذِ ٱسۡتَسۡقَىٰ مُوسَىٰ لِقَوۡمِهِۦ فَقُلۡنَا ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡحَجَرَۖ فَٱنفَجَرَتۡ مِنۡهُ ٱثۡنَتَا عَشۡرَةَ عَيۡنٗاۖ قَدۡ عَلِمَ كُلُّ أُنَاسٖ مَّشۡرَبَهُمۡۖ كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ مِن رِّزۡقِ ٱللَّهِ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Musa ya roqa wa mutanensa ruwan sha, sai Muka ce: “Ka bugi dutse da sandarka”, sai idanuwan marmaron ruwa goma sha biyu suka vuvvugo daga cikinsa. Haqiqa kowaxanne mutane sun san mashayarsu. (Muka ce): “Ku ci kuma ku sha daga arzikin Allah, kuma kada ku yaxa varna a bayan qasa