السورة: Suratul Qalam

الآية : 1

نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ

NUN[1]. (Allah ya ce): Na rantse da alqalami da abin da (mala’iku) suke rubutawa


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


السورة: Suratul Qalam

الآية : 2

مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ

Kai ba mahaukaci ba ne saboda ni’imar Ubangijinka



السورة: Suratul Qalam

الآية : 3

وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ

Kuma lalle tabbas kana da lada marar yankewa



السورة: Suratul Qalam

الآية : 4

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ

Lalle kuma kai kana kan halaye masu girma



السورة: Suratul Qalam

الآية : 5

فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ

To ba da daxewa ba za ka gani, su ma kuma su gani



السورة: Suratul Qalam

الآية : 6

بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ

Wane ne daga cikinku mahaukaci?



السورة: Suratul Qalam

الآية : 7

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle Ubangijinka Shi Ya fi sanin wanda ya kauce wa hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin shiryayyu



السورة: Suratul Qalam

الآية : 8

فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Saboda haka kada ka bi masu qaryatawa



السورة: Suratul Qalam

الآية : 9

وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ

Sun yi burin da za ka sassauto, sai su ma su sassauto[1]


1- Watau ya daina aibata gumakansu da bautarsu, sai su ma su daina sukan sa da addininsa.


السورة: Suratul Qalam

الآية : 10

وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ

Kada kuma ka bi duk wani mai yawan rantsuwa, wulaqantacce



السورة: Suratul Qalam

الآية : 11

هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ

Mai yawan yin zunxe, mai yawan yawo da annamimanci



السورة: Suratul Qalam

الآية : 12

مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ

Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai yawan savo



السورة: Suratul Qalam

الآية : 13

عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ

Mai busasshiyar zuciya, bayan wannan kuma marar asali ne



السورة: Suratul Qalam

الآية : 14

أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ

Don ya kasance mai dukiya da ‘ya’ya



السورة: Suratul Qalam

الآية : 15

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 16

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ

Ba da daxewa ba za Mu yi masa alama a kan hancinsa



السورة: Suratul Qalam

الآية : 17

إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ

Lalle Mu Mun jarrabe su (wato mutanen Makka) kamar yadda Muka jarrabi ma’abota gona, lokacin da suka rantse cewa, lalle tabbas za su girbe ta da asussuba



السورة: Suratul Qalam

الآية : 18

وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ

Ba sa kuma togaciya (da faxar insha Allah)



السورة: Suratul Qalam

الآية : 19

فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ

Sai wani bala’i daga Ubangijinka ya kewaye ta alhali su suna bacci



السورة: Suratul Qalam

الآية : 20

فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ

Sai ta wayi gari (baqi qirin) kamar duhun dare



السورة: Suratul Qalam

الآية : 21

فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ

Sai suka kirawo junansu da asussuba



السورة: Suratul Qalam

الآية : 22

أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ

Cewa: “Ku yi sammako ga amfanin gonarku idan kun kasance masu yin girbi.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 23

فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ

Sai suka tafi alhali suna yi wa junansu raxa



السورة: Suratul Qalam

الآية : 24

أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ

Cewa: “Lalle a yau kada wani miskini ya shigar muku cikinta.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 25

وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ

Suka kuwa yi sammako suna masu zaton su masu iko ne a kan hana (mabuqata)



السورة: Suratul Qalam

الآية : 26

فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ

To lokacin da suka gan ta sai suka ce: “Lalle mu tabbas mun yi vatan kai



السورة: Suratul Qalam

الآية : 27

بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ

“A’a, mu dai an hana mu ne kawai.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 28

قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ

Sai wanda ya fi su kirki ya ce: “Ban gaya muku ya kamata ku tsarkake Allah ba?”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 29

قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Suka ce, “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu, lalle mu mun kasance azzalumai.”



السورة: Suratul Qalam

الآية : 30

فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ

Sai sashinsu ya fuskanci sashi suna zargin juna