السورة: Suratun Najm

الآية : 1

وَٱلنَّجۡمِ إِذَا هَوَىٰ

Na rantse da tauraro yayin da ya faxi



السورة: Suratun Najm

الآية : 2

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمۡ وَمَا غَوَىٰ

Mutumin naku[1] bai vata ba, kuma bai kauce hanya ba


1- Watau Annabi Muhammadu ().


السورة: Suratun Najm

الآية : 3

وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلۡهَوَىٰٓ

Kuma ba ya yin magana bisa son rai



السورة: Suratun Najm

الآية : 4

إِنۡ هُوَ إِلَّا وَحۡيٞ يُوحَىٰ

Shi (Alqur’ani) ba wani abu ne ba in ban da wahayi da ake yiwo (masa)



السورة: Suratun Najm

الآية : 5

عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلۡقُوَىٰ

Mai tsananin qarfi ne (watau Jibrilu) ya koyar da shi



السورة: Suratun Najm

الآية : 6

ذُو مِرَّةٖ فَٱسۡتَوَىٰ

Mai kyawawan halitta ne, sai ya daidaita



السورة: Suratun Najm

الآية : 7

وَهُوَ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Alhali kuwa shi yana a sassa na can sama



السورة: Suratun Najm

الآية : 8

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ

Sannan sai ya kusanto, sai ya qara matsawa[1]


1- Watau Jibrilu () ya kusanto Annabi () ya matso kusa don yi masa wahayi.


السورة: Suratun Najm

الآية : 9

فَكَانَ قَابَ قَوۡسَيۡنِ أَوۡ أَدۡنَىٰ

Sai ya kasance kamar kusancin kamu biyu ko qasa da haka



السورة: Suratun Najm

الآية : 10

فَأَوۡحَىٰٓ إِلَىٰ عَبۡدِهِۦ مَآ أَوۡحَىٰ

Sannan (Allah) Ya yiyo wahayin abin da Ya yi wahayi zuwa ga Bawansa (Ma’aiki)



السورة: Suratun Najm

الآية : 11

مَا كَذَبَ ٱلۡفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ

Zuciyar (ta Ma’aiki) ba ta yi qaryar abin da ta gani ba



السورة: Suratun Najm

الآية : 12

أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ

Yanzu kwa riqa jayayya da shi kan abin da yake gani?



السورة: Suratun Najm

الآية : 13

وَلَقَدۡ رَءَاهُ نَزۡلَةً أُخۡرَىٰ

Haqiqa ya gan shi (Jibrilu) a wani karon ma[1]


1- Watau lokacin Isra’i da Mi’iraji, inda ya gan shi a halittarsa ta asali.


السورة: Suratun Najm

الآية : 14

عِندَ سِدۡرَةِ ٱلۡمُنتَهَىٰ

A wurin Magaryar tuqewa



السورة: Suratun Najm

الآية : 15

عِندَهَا جَنَّةُ ٱلۡمَأۡوَىٰٓ

A wurinta ne Aljannar makoma take



السورة: Suratun Najm

الآية : 16

إِذۡ يَغۡشَى ٱلسِّدۡرَةَ مَا يَغۡشَىٰ

A yayin da abin da ya lulluve Magaryar (na ban mamaki) ya lulluve ta



السورة: Suratun Najm

الآية : 17

مَا زَاغَ ٱلۡبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ

Ganin (nasa) bai karkace ba, kuma bai zarme ba



السورة: Suratun Najm

الآية : 18

لَقَدۡ رَأَىٰ مِنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ

Haqiqa ya ga wasu ayoyin Ubangijinsa manya-manya



السورة: Suratun Najm

الآية : 19

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱللَّـٰتَ وَٱلۡعُزَّىٰ

Ku ba ni labarin (gumakan) Lata da Uzza



السورة: Suratun Najm

الآية : 20

وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰٓ

Da Manata cikon ta ukunsu



السورة: Suratun Najm

الآية : 21

أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلۡأُنثَىٰ

Yanzu xa namiji zai zama naku, Shi kuma Ya tashi da ‘ya mace?



السورة: Suratun Najm

الآية : 22

تِلۡكَ إِذٗا قِسۡمَةٞ ضِيزَىٰٓ

Idan haka ne wannan rabon na zalunci ne[1]


1- Domin ya qunshi Fifita mahaluki a kan Mahalicci.


السورة: Suratun Najm

الآية : 23

إِنۡ هِيَ إِلَّآ أَسۡمَآءٞ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٍۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهۡوَى ٱلۡأَنفُسُۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلۡهُدَىٰٓ

Su ba komai ba ne face sunaye da kuka sa musu, ku da iyayenku, Allah bai saukar muku da wata hujja ba game da su. Ba abin da suke bi sai zato da son zuciya. Haqiqa kuwa shiriya ta zo musu daga Ubangijinsu



السورة: Suratun Najm

الآية : 24

أَمۡ لِلۡإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ

Ko kuwa sai mutum ya sami abin da yake buri ne?



السورة: Suratun Najm

الآية : 25

فَلِلَّهِ ٱلۡأٓخِرَةُ وَٱلۡأُولَىٰ

To lahira da duniya duka na Allah ne



السورة: Suratun Najm

الآية : 26

۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ

Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?



السورة: Suratun Najm

الآية : 27

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ تَسۡمِيَةَ ٱلۡأُنثَىٰ

Lalle waxanda ba sa yin imani da ranar lahira suna kiran mala’iku da sunan mata



السورة: Suratun Najm

الآية : 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا

Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya



السورة: Suratun Najm

الآية : 29

فَأَعۡرِضۡ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكۡرِنَا وَلَمۡ يُرِدۡ إِلَّا ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Sai ka kau da kai daga duk wanda ya ba da baya daga ambatonmu, bai kuma yi nufin komai ba sai rayuwar duniya



السورة: Suratun Najm

الآية : 30

ذَٰلِكَ مَبۡلَغُهُم مِّنَ ٱلۡعِلۡمِۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱهۡتَدَىٰ

Wannan ne maqurar iliminsu. Lalle Ubangijinka Shi ne Ya fi sanin wanda ya vace daga hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin wanda ya shiriya