السورة: Suratu Muhammad

الآية : 1

ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَصَدُّواْ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ أَضَلَّ أَعۡمَٰلَهُمۡ

Waxanda suka kafirta suka kuma toshe hanyar Allah, to (Allah) Ya lalata ayyukansu[1]


1- Watau ba za su sami lada ba a kan ayyuka na qwarai da suka yi. Hakanan ayyukansu da suke yi na qoqarin rushe Musulunci haqansu ba zai cimma ruwa ba.


السورة: Suratu Muhammad

الآية : 2

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَءَامَنُواْ بِمَا نُزِّلَ عَلَىٰ مُحَمَّدٖ وَهُوَ ٱلۡحَقُّ مِن رَّبِّهِمۡ كَفَّرَ عَنۡهُمۡ سَيِّـَٔاتِهِمۡ وَأَصۡلَحَ بَالَهُمۡ

Waxanda kuwa suka yi imani suka kuma yi aiki nagari, kuma suka gaskata abin da aka saukar wa Muhammadu alhali kuwa shi ne gaskiya daga Ubangijinsu, sai (Allah) Ya kankare musu munanan ayyukansu, Ya kuma gyara musu halayensu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 3

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱتَّبَعُواْ ٱلۡبَٰطِلَ وَأَنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّبَعُواْ ٱلۡحَقَّ مِن رَّبِّهِمۡۚ كَذَٰلِكَ يَضۡرِبُ ٱللَّهُ لِلنَّاسِ أَمۡثَٰلَهُمۡ

Wannan (sakamako) kuwa saboda waxanda suka kafirta sun bi varna, waxanda kuwa suka yi imani sun bi shiriya daga Ubangijinsu. Kamar haka ne Allah Yake buga wa mutane misalansu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 4

فَإِذَا لَقِيتُمُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَضَرۡبَ ٱلرِّقَابِ حَتَّىٰٓ إِذَآ أَثۡخَنتُمُوهُمۡ فَشُدُّواْ ٱلۡوَثَاقَ فَإِمَّا مَنَّۢا بَعۡدُ وَإِمَّا فِدَآءً حَتَّىٰ تَضَعَ ٱلۡحَرۡبُ أَوۡزَارَهَاۚ ذَٰلِكَۖ وَلَوۡ يَشَآءُ ٱللَّهُ لَٱنتَصَرَ مِنۡهُمۡ وَلَٰكِن لِّيَبۡلُوَاْ بَعۡضَكُم بِبَعۡضٖۗ وَٱلَّذِينَ قُتِلُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ فَلَن يُضِلَّ أَعۡمَٰلَهُمۡ

To idan kuka haxu da waxanda suka kafirta sai ku sare wuyoyinsu har lokacin da kuka yi musu jina-jina, sai ku tsananta xauri[1]; to bayan nan ko dai yafewa su tafi bayan (kun ribace su), ko kuma karvar fansa har sai yaqi ya lafa. Wannan abu haka yake, da kuma Allah Ya ga dama da Ya yi nasara a kansu (ko da ba yaqi), sai dai kuma (Ya yi haka ne) don Ya jarrabi shashinku da shashi. Waxanda kuwa aka kashe su a hanyar Allah, to ba zai tava lalata ayyukansa ba


1- Watau Musulmi su kama su a matsayin ribatattun yaqi.


السورة: Suratu Muhammad

الآية : 5

سَيَهۡدِيهِمۡ وَيُصۡلِحُ بَالَهُمۡ

Zai shirye su Ya kuma kyautata halinsu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 6

وَيُدۡخِلُهُمُ ٱلۡجَنَّةَ عَرَّفَهَا لَهُمۡ

Ya kuma shigar da su Aljannar da Ya sanar da ita gare su



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 7

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تَنصُرُواْ ٱللَّهَ يَنصُرۡكُمۡ وَيُثَبِّتۡ أَقۡدَامَكُمۡ

Ya ku waxanda suka yi imani idan kuka taimaki Allah, to zai taimake ku, Ya kuma tabbatar da dugaduganku



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 8

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَتَعۡسٗا لَّهُمۡ وَأَضَلَّ أَعۡمَٰلَهُمۡ

Waxanda kuwa suka kafirce to kaiconsu, (Allah) kuma Ya lalata ayyukansu[1]


1- Watau ba za su sami ladan wani aiki nasu na qwarai ba, kuma ayyukansu na qoqarin rushe Musulunci ba za su yi nasara ba.


السورة: Suratu Muhammad

الآية : 9

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ كَرِهُواْ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ فَأَحۡبَطَ أَعۡمَٰلَهُمۡ

Wannan kuwa saboda cewa sun qi abin da Allah Ya saukar, sai Ya lalata ayyukansu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 10

۞أَفَلَمۡ يَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَيَنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۖ دَمَّرَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِمۡۖ وَلِلۡكَٰفِرِينَ أَمۡثَٰلُهَا

Yanzu ba za su yi tafiya a bayan qasa ba sai su duba yaya qarshen waxanda suka gabace su ya kasance? Allah Ya hallaka su; kafirai kuma suna da (sakamako) kwatankwacinsa



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 11

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ مَوۡلَى ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَأَنَّ ٱلۡكَٰفِرِينَ لَا مَوۡلَىٰ لَهُمۡ

Wannan kuwa saboda lalle Allah ne Majivincin al’amuran waxanda suka yi imani, lalle kuma su kafirai ba su da wani majivinci



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 12

إِنَّ ٱللَّهَ يُدۡخِلُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يَتَمَتَّعُونَ وَيَأۡكُلُونَ كَمَا تَأۡكُلُ ٱلۡأَنۡعَٰمُ وَٱلنَّارُ مَثۡوٗى لَّهُمۡ

Lalle Allah Yana shigar da waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari gidajen Aljanna (waxanda) qoramu suke gudana ta qarqashinsu; waxanda kuwa suka kafirta suna jin daxi (a duniya), suna kuma ta ciye-ciye kamar yadda dabbobi suke yi, wuta ce kuma makomarsu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 13

وَكَأَيِّن مِّن قَرۡيَةٍ هِيَ أَشَدُّ قُوَّةٗ مِّن قَرۡيَتِكَ ٱلَّتِيٓ أَخۡرَجَتۡكَ أَهۡلَكۡنَٰهُمۡ فَلَا نَاصِرَ لَهُمۡ

Alqaryu nawa ne waxanda suka fi alqaryarka wadda ta fitar da kai qarfi, Mun hallakar da su, don haka ba su da wani mai taimakon su



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 14

أَفَمَن كَانَ عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّهِۦ كَمَن زُيِّنَ لَهُۥ سُوٓءُ عَمَلِهِۦ وَٱتَّبَعُوٓاْ أَهۡوَآءَهُم

Yanzu waxanda suka kasance a kan hujja daga Ubangijinsu, sa yi daidai da waxanda aka qawata musu mummuna aikinsu, suka kuma bi son zuciyarsu?



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 15

مَّثَلُ ٱلۡجَنَّةِ ٱلَّتِي وُعِدَ ٱلۡمُتَّقُونَۖ فِيهَآ أَنۡهَٰرٞ مِّن مَّآءٍ غَيۡرِ ءَاسِنٖ وَأَنۡهَٰرٞ مِّن لَّبَنٖ لَّمۡ يَتَغَيَّرۡ طَعۡمُهُۥ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ خَمۡرٖ لَّذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ عَسَلٖ مُّصَفّٗىۖ وَلَهُمۡ فِيهَا مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ وَمَغۡفِرَةٞ مِّن رَّبِّهِمۡۖ كَمَنۡ هُوَ خَٰلِدٞ فِي ٱلنَّارِ وَسُقُواْ مَآءً حَمِيمٗا فَقَطَّعَ أَمۡعَآءَهُمۡ

Kwatankwacin Aljannar da aka yi wa masu taqawa alqawari da ita shi ne, a cikinta akwai qoramu na ruwa ba gurvatacce ba, da kuma qoramu na nono da xanxanonsa bai canja ba, da qoramu na giya masu daxi ga mashaya, da qoramu na tatacciyar zuma, kuma suna da kowane irin nau’i na ‘ya’yan itace da kuma gafara daga Ubangijinsu. Yanzu (masu waxannan sa yi) daidai da waxanda za su dawwama a cikin wuta a kuma shayar da su ruwa tafasasshe, sai ya yayyanke kayan cikinsu?



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 16

وَمِنۡهُم مَّن يَسۡتَمِعُ إِلَيۡكَ حَتَّىٰٓ إِذَا خَرَجُواْ مِنۡ عِندِكَ قَالُواْ لِلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ مَاذَا قَالَ ءَانِفًاۚ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ طَبَعَ ٱللَّهُ عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ وَٱتَّبَعُوٓاْ أَهۡوَآءَهُمۡ

Daga cikinsu kuma akwai waxanda suke sauraron ka, har lokacin da suka fita daga wurinka sai su ce da waxanda aka bai wa ilimi: “Shin me ma ya ce xazu?” Waxannan su ne waxanda Allah Ya toshe zukatansu suka kuma bi son ransu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 17

وَٱلَّذِينَ ٱهۡتَدَوۡاْ زَادَهُمۡ هُدٗى وَءَاتَىٰهُمۡ تَقۡوَىٰهُمۡ

Waxanda kuwa suka shiryu Ya qara musu shiriya, Ya kuma kimsa musu taqawarsu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 18

فَهَلۡ يَنظُرُونَ إِلَّا ٱلسَّاعَةَ أَن تَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗۖ فَقَدۡ جَآءَ أَشۡرَاطُهَاۚ فَأَنَّىٰ لَهُمۡ إِذَا جَآءَتۡهُمۡ ذِكۡرَىٰهُمۡ

Ai ba wani abu da suke sauraro sai alqiyama ta zo musu farat xaya; to haqiqa alamominta sun zo[1]. To qaqa tunawar tasu za ta zame musu idan abin (alqiyamar) ta zo musu ne?


1- Daga cikinsu akwai aiko da Manzon Allah () da tsagewar wata gida biyu da ya faru a Makka.


السورة: Suratu Muhammad

الآية : 19

فَٱعۡلَمۡ أَنَّهُۥ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ وَٱسۡتَغۡفِرۡ لِذَنۢبِكَ وَلِلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِۗ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مُتَقَلَّبَكُمۡ وَمَثۡوَىٰكُمۡ

To ka sani cewa, babu wani abin bauta da gaskiya sai Allah, kuma ka nemi gafarar zunubanka da na muminai maza da mata, Allah kuma Yana sane da kai-kawonku (na rana) da kuma wurin kwanciyarku (da daddare)



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 20

وَيَقُولُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَوۡلَا نُزِّلَتۡ سُورَةٞۖ فَإِذَآ أُنزِلَتۡ سُورَةٞ مُّحۡكَمَةٞ وَذُكِرَ فِيهَا ٱلۡقِتَالُ رَأَيۡتَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ يَنظُرُونَ إِلَيۡكَ نَظَرَ ٱلۡمَغۡشِيِّ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡمَوۡتِۖ فَأَوۡلَىٰ لَهُمۡ

Waxanda kuma suka yi imani suna cewa: “Me ya hana a saukar da wata sura (wadda za ta ba mu damar yin yaqi)?” Sannan lokacin da aka saukar da wata sura mai xauke da hukunci aka kuma ambaci yaqi a cikinta, sai ka ga waxanda suke da raunin imani a zukatansu (watau munafukai), suna kallon ka kamar kallon wanda yake cikin magagin mutuwa. To abin da ya fiye musu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 21

طَاعَةٞ وَقَوۡلٞ مَّعۡرُوفٞۚ فَإِذَا عَزَمَ ٱلۡأَمۡرُ فَلَوۡ صَدَقُواْ ٱللَّهَ لَكَانَ خَيۡرٗا لَّهُمۡ

(Shi ne) yin biyayya da magana mai kyau. To idan al’amarin yaqi ya tabbata, to da za su nuna wa Allah gaskiyarsu, da ya fi musu alhairi



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 22

فَهَلۡ عَسَيۡتُمۡ إِن تَوَلَّيۡتُمۡ أَن تُفۡسِدُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَتُقَطِّعُوٓاْ أَرۡحَامَكُمۡ

Shin ba kwa ganin idan kuka ba da baya (daga bin Allah) sai ku yi varna a bayan qasa, ku kuma yanke zumuntarku?



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 23

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ لَعَنَهُمُ ٱللَّهُ فَأَصَمَّهُمۡ وَأَعۡمَىٰٓ أَبۡصَٰرَهُمۡ

Waxannan su ne waxanda Allah Ya la’ance su, sai Ya kurumtar da su, Ya kuma makantar da ganinsu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 24

أَفَلَا يَتَدَبَّرُونَ ٱلۡقُرۡءَانَ أَمۡ عَلَىٰ قُلُوبٍ أَقۡفَالُهَآ

Yanzu ba za su yi tunani na basira ba (game da) Alqur’ani ba, ko kuwa akwai wani rufi ne a kan zukatansu?



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 25

إِنَّ ٱلَّذِينَ ٱرۡتَدُّواْ عَلَىٰٓ أَدۡبَٰرِهِم مِّنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمُ ٱلۡهُدَى ٱلشَّيۡطَٰنُ سَوَّلَ لَهُمۡ وَأَمۡلَىٰ لَهُمۡ

Lalle waxanda suka yi ridda suka koma baya, bayan kuwa shiriya ta bayyana a gare su, to Shaixan ne ya qawata musu ya kuma yi musu shifta



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 26

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ قَالُواْ لِلَّذِينَ كَرِهُواْ مَا نَزَّلَ ٱللَّهُ سَنُطِيعُكُمۡ فِي بَعۡضِ ٱلۡأَمۡرِۖ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ إِسۡرَارَهُمۡ

Wannan kuwa saboda lalle su, sun ce wa waxanda suka qi bin abin da Allah Ya saukar: “Za mu bi ku a wasu al’amura.” Allah kuwa Yana sane da asiransu



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 27

فَكَيۡفَ إِذَا تَوَفَّتۡهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يَضۡرِبُونَ وُجُوهَهُمۡ وَأَدۡبَٰرَهُمۡ

To yaya za su zama lokacin da mala’iku za su karvi rayukansu suna dukan fuskokinsu da bayansu?



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 28

ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمُ ٱتَّبَعُواْ مَآ أَسۡخَطَ ٱللَّهَ وَكَرِهُواْ رِضۡوَٰنَهُۥ فَأَحۡبَطَ أَعۡمَٰلَهُمۡ

Wannan kuwa saboda lalle su, sun bi abin da yake fusata Allah suka kuma qi bin yardarsa, sai ya rusa ayyukansa



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 29

أَمۡ حَسِبَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٌ أَن لَّن يُخۡرِجَ ٱللَّهُ أَضۡغَٰنَهُمۡ

Ko kuwa waxanda suke da cuta a cikin zukatansu suna tsammanin cewa Allah ba zai fito da qulle-qullen zukatansu ba ne?



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 30

وَلَوۡ نَشَآءُ لَأَرَيۡنَٰكَهُمۡ فَلَعَرَفۡتَهُم بِسِيمَٰهُمۡۚ وَلَتَعۡرِفَنَّهُمۡ فِي لَحۡنِ ٱلۡقَوۡلِۚ وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ أَعۡمَٰلَكُمۡ

Kuma da Mun ga dama da tabbas Mun nuna maka su (watau munafukai), to tabbas da ka gane su da alamominsu. Kuma tabbas za ka iya gane su ta hanyar salon maganarsu. Allah kuma Yana sane da ayyukanku