السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 1

حمٓ

HA MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 2

وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Na rantse da Littafi mabayyani (Alqur’ani)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 3

إِنَّا جَعَلۡنَٰهُ قُرۡءَٰنًا عَرَبِيّٗا لَّعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Lalle Mu Mun sanya shi ya zamo abin karantawa cikin harshen Larabci domin ku hankalta



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 4

وَإِنَّهُۥ فِيٓ أُمِّ ٱلۡكِتَٰبِ لَدَيۡنَا لَعَلِيٌّ حَكِيمٌ

Lalle kuma shi (Alqur’ani) a cikin Littafi Lauhul-Mahafuzu a wurinmu tabbas maxaukaki ne, mai hikima



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 5

أَفَنَضۡرِبُ عَنكُمُ ٱلذِّكۡرَ صَفۡحًا أَن كُنتُمۡ قَوۡمٗا مُّسۡرِفِينَ

Yanzu Ma fasa saukar muku da Alqur’ani Mu watsar da ku, don kun kasance mutane masu yawan varna?



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 6

وَكَمۡ أَرۡسَلۡنَا مِن نَّبِيّٖ فِي ٱلۡأَوَّلِينَ

Annabi nawa Muka aika wa mutanen farko



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 7

وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن نَّبِيٍّ إِلَّا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ

Ba kuma wani annabi da yakan zo musu sai sun kasance suna yi masa izgili



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 8

فَأَهۡلَكۡنَآ أَشَدَّ مِنۡهُم بَطۡشٗا وَمَضَىٰ مَثَلُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Sai Muka hallakar da waxanda suka fi su tsananin qarfi[1], kuma bayanin yadda aka hallakar da mutanen farko ya riga ya shuxe


1- Watau kamar qabilun Adawa da Samudawa da mutanen Annabi Luxu ().


السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 9

وَلَئِن سَأَلۡتَهُم مَّنۡ خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ لَيَقُولُنَّ خَلَقَهُنَّ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡعَلِيمُ

Lalle kuma idan ka tambaye su wane ne ya halicci sammai da qasa, to tabbas za su ce: “(Allah) ne Mabuwayi, Masani Ya halicce su.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 10

ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ مَهۡدٗا وَجَعَلَ لَكُمۡ فِيهَا سُبُلٗا لَّعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Wanda Ya sanya muku qasa ta zama shimfixa, Ya kuma sanya muku hanyoyi a cikinta don ku gane (inda za ku dosa)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 11

وَٱلَّذِي نَزَّلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءَۢ بِقَدَرٖ فَأَنشَرۡنَا بِهِۦ بَلۡدَةٗ مَّيۡتٗاۚ كَذَٰلِكَ تُخۡرَجُونَ

Wanda kuma Ya saukar da ruwa daidai gwargwado daga sama sannan Muka raya mataccen gari da shi. Kamar haka ne za a fito da ku (daga qabarurruka)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 12

وَٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡأَزۡوَٰجَ كُلَّهَا وَجَعَلَ لَكُم مِّنَ ٱلۡفُلۡكِ وَٱلۡأَنۡعَٰمِ مَا تَرۡكَبُونَ

Kuma wanda Ya halicci dukkan dangogin abubuwa bibbiyu, Ya kuma sanya muku daga jiragen ruwa da kuma dabbobin ni’ima, abubuwan da kuke hawa



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 13

لِتَسۡتَوُۥاْ عَلَىٰ ظُهُورِهِۦ ثُمَّ تَذۡكُرُواْ نِعۡمَةَ رَبِّكُمۡ إِذَا ٱسۡتَوَيۡتُمۡ عَلَيۡهِ وَتَقُولُواْ سُبۡحَٰنَ ٱلَّذِي سَخَّرَ لَنَا هَٰذَا وَمَا كُنَّا لَهُۥ مُقۡرِنِينَ

Don ku daidaita a kan bayansu, sannan ku tuna ni’imar Ubangijinku lokacin da kuka daidaita a kansu kuma ku ce: “Tsarki ya tabbata ga wanda Ya hore mana wannan, ba mu zamanto masu ikon sarrafa shi ba



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 14

وَإِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا لَمُنقَلِبُونَ

“Kuma lalle zuwa ga Ubangijinmu tabbas za mu koma.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 15

وَجَعَلُواْ لَهُۥ مِنۡ عِبَادِهِۦ جُزۡءًاۚ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَكَفُورٞ مُّبِينٌ

Kuma suka mai da wasu daga cikin bayinsa wani vangare nasa (wato `ya`yansa). Lalle mutum mai yawan butulci ne mai bayyana (butulcinsa)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 16

أَمِ ٱتَّخَذَ مِمَّا يَخۡلُقُ بَنَاتٖ وَأَصۡفَىٰكُم بِٱلۡبَنِينَ

Yanzu Ya xauki `ya`ya mata daga abubuwan da Yake halitta, ku kuma Ya zava muku `ya`ya maza?



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 17

وَإِذَا بُشِّرَ أَحَدُهُم بِمَا ضَرَبَ لِلرَّحۡمَٰنِ مَثَلٗا ظَلَّ وَجۡهُهُۥ مُسۡوَدّٗا وَهُوَ كَظِيمٌ

Idan kuma aka yi wa xayansu albishir da abin da ya buga misali cewa na (Allah) Arrahmanu ne, sai fuskarsa ta yini a murtuke yana cike da baqin ciki



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 18

أَوَمَن يُنَشَّؤُاْ فِي ٱلۡحِلۡيَةِ وَهُوَ فِي ٱلۡخِصَامِ غَيۡرُ مُبِينٖ

Yanzu (sa danganta wa Allah) wanda da ake renon sa cikin kwalliya, alhali kuma idan an zo wajen husuma ba zai iya bayyana kansa (wajan ba da hujja) ba?



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 19

وَجَعَلُواْ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ ٱلَّذِينَ هُمۡ عِبَٰدُ ٱلرَّحۡمَٰنِ إِنَٰثًاۚ أَشَهِدُواْ خَلۡقَهُمۡۚ سَتُكۡتَبُ شَهَٰدَتُهُمۡ وَيُسۡـَٔلُونَ

Suka kuma mai da mala’iku waxanda suke bayin (Allah) Arrahmanu ne `ya`ya mata. Shin sun halarci sanda aka halicce su ne? To za a rubuta shaidarsu, za kuma a tambaye su (a lahira)



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 20

وَقَالُواْ لَوۡ شَآءَ ٱلرَّحۡمَٰنُ مَا عَبَدۡنَٰهُمۗ مَّا لَهُم بِذَٰلِكَ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِنۡ هُمۡ إِلَّا يَخۡرُصُونَ

Suka kuma ce: “Da (Allah) Arrahmanu Ya ga dama, da ba mu bauta musu ba (wato mala’ikun).” Ba su da wani takamaiman ilimi a kan hakan; ba abin da suke yi sai shaci-faxi



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 21

أَمۡ ءَاتَيۡنَٰهُمۡ كِتَٰبٗا مِّن قَبۡلِهِۦ فَهُم بِهِۦ مُسۡتَمۡسِكُونَ

Ko kuma Mun ba su wani littafi ne gabaninsa (Alqur’ani), saboda haka suke riqe da shi qam-qam?



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 22

بَلۡ قَالُوٓاْ إِنَّا وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا عَلَىٰٓ أُمَّةٖ وَإِنَّا عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِم مُّهۡتَدُونَ

A’a, cewa dai suka yi: “Lalle mu mun sami iyayenmu a kan wani addini ne, mu kuma lalle sawunsu muke bi.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 23

وَكَذَٰلِكَ مَآ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ فِي قَرۡيَةٖ مِّن نَّذِيرٍ إِلَّا قَالَ مُتۡرَفُوهَآ إِنَّا وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا عَلَىٰٓ أُمَّةٖ وَإِنَّا عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِم مُّقۡتَدُونَ

Kuma kamar haka ne, ba Mu tava aiko wani mai gargaxi ba a wata alqarya a gabaninka sai ‘yan ta-moren cikinsu sun ce: “Lalle mu mun sami iyayenmu a kan wani addini, kuma lalle mu hanyarsu muke kwaikwayo.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 24

۞قَٰلَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكُم بِأَهۡدَىٰ مِمَّا وَجَدتُّمۡ عَلَيۡهِ ءَابَآءَكُمۡۖ قَالُوٓاْ إِنَّا بِمَآ أُرۡسِلۡتُم بِهِۦ كَٰفِرُونَ

Ya ce (da su: “Yanzu za ku yi koyi da su) ko da na zo muku da abin da ya fi zama shiriya a kan abin da kuka sami iyayenku a kansa?” Suka ce: “Lalle mu masu kafirce wa abin da aka aiko ku da shi ne.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 25

فَٱنتَقَمۡنَا مِنۡهُمۡۖ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Sai Muka saka musu da azaba; to duba ka ga yadda qarshen masu qaryatawa ya kasance



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 26

وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِيمُ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦٓ إِنَّنِي بَرَآءٞ مِّمَّا تَعۡبُدُونَ

Kuma ka tuna lokacin da Ibrahimu ya ce da Babansa da mutanensa: “Lalle ni ba ruwana da abin da kuke bautawa



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 27

إِلَّا ٱلَّذِي فَطَرَنِي فَإِنَّهُۥ سَيَهۡدِينِ

“Sai dai wanda Ya halicce ni, to lalle Shi ne Zai shirye ni.”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 28

وَجَعَلَهَا كَلِمَةَۢ بَاقِيَةٗ فِي عَقِبِهِۦ لَعَلَّهُمۡ يَرۡجِعُونَ

Ya kuma sanya ta (kalmar Tauhidi ta zama) kalma ce mai wanzuwa a cikin zuri’arsa don (mutanen Makka) su komo (kan hanya).”



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 29

بَلۡ مَتَّعۡتُ هَـٰٓؤُلَآءِ وَءَابَآءَهُمۡ حَتَّىٰ جَآءَهُمُ ٱلۡحَقُّ وَرَسُولٞ مُّبِينٞ

A’a, Na jiyar da waxannan daxi tare da iyayensu ne har gaskiya ta zo musu da wani manzo mai bayyanawa



السورة: Suratuz Zukhruf 

الآية : 30

وَلَمَّا جَآءَهُمُ ٱلۡحَقُّ قَالُواْ هَٰذَا سِحۡرٞ وَإِنَّا بِهِۦ كَٰفِرُونَ

Yayin da gaskiyar ta zo musu sai suka ce: “Wannan sihiri ne, kuma lalle mu masu kafirce masa ne.”