السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 1

الٓرۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

ALIF LAM RA[1]. Waxannan ayoyi ne na Littafi mabayyani


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 2

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ قُرۡءَٰنًا عَرَبِيّٗا لَّعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Lalle Mu Muka saukar da shi Alqur’ani da (harshen) Larabci don ku hankalta



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 3

نَحۡنُ نَقُصُّ عَلَيۡكَ أَحۡسَنَ ٱلۡقَصَصِ بِمَآ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ وَإِن كُنتَ مِن قَبۡلِهِۦ لَمِنَ ٱلۡغَٰفِلِينَ

Mu ne Muke labarta maka (labari) mafi kyan labartawa ta hanyar yi maka wahayin wannan Alqur’ani, ko da yake gabaninsa kana cikin marasa sanin(sa)



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 4

إِذۡ قَالَ يُوسُفُ لِأَبِيهِ يَـٰٓأَبَتِ إِنِّي رَأَيۡتُ أَحَدَ عَشَرَ كَوۡكَبٗا وَٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَ رَأَيۡتُهُمۡ لِي سَٰجِدِينَ

(Ka tuna) lokacin da Yusufu ya ce da babansa[1]: “Ya babana, lalle na yi mafarkin taurari goma sha xaya da rana da wata[2], na gan su suna yi min sujjada.”


1- Babansa shi ne Annabi Ya’aqub () xan Annabi Ishaq () xan Annabi Ibrahim ().


2- Taurari goma sha xaya su ne ‘yan’uwansa goma sha xaya; rana kuwa tana nufin mahaifiyarsa; wata kuwa yana nufin mahaifinsa Annabi Ya’aqub ().


السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 5

قَالَ يَٰبُنَيَّ لَا تَقۡصُصۡ رُءۡيَاكَ عَلَىٰٓ إِخۡوَتِكَ فَيَكِيدُواْ لَكَ كَيۡدًاۖ إِنَّ ٱلشَّيۡطَٰنَ لِلۡإِنسَٰنِ عَدُوّٞ مُّبِينٞ

Ya ce: “Ya xana, kada ka labarta mafarkinka ga ‘yan’uwanka, sai su shirya maka makirci; lalle Shaixan maqiyi ne mai bayyana qiyayya ga mutum



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 6

وَكَذَٰلِكَ يَجۡتَبِيكَ رَبُّكَ وَيُعَلِّمُكَ مِن تَأۡوِيلِ ٱلۡأَحَادِيثِ وَيُتِمُّ نِعۡمَتَهُۥ عَلَيۡكَ وَعَلَىٰٓ ءَالِ يَعۡقُوبَ كَمَآ أَتَمَّهَا عَلَىٰٓ أَبَوَيۡكَ مِن قَبۡلُ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡحَٰقَۚ إِنَّ رَبَّكَ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

“Kamar haka ne kuma Ubangijinka zai zave ka Ya kuma sanar da kai wani abu daga fassarar mafarkai, Ya kuma cika ni’imarsa a gare ka da kuma ga iyalin Ya’aqubu kamar yadda tun tuni Ya cika ta ga iyayenka Ibrahimu da Is’haqa. Lalle Ubangijinka Masani ne Mai hikima.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 7

۞لَّقَدۡ كَانَ فِي يُوسُفَ وَإِخۡوَتِهِۦٓ ءَايَٰتٞ لِّلسَّآئِلِينَ

Haqiqa akwai ayoyi ga matambaya dangane da (labarin) Yusufu shi da ‘yan’uwansa



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 8

إِذۡ قَالُواْ لَيُوسُفُ وَأَخُوهُ أَحَبُّ إِلَىٰٓ أَبِينَا مِنَّا وَنَحۡنُ عُصۡبَةٌ إِنَّ أَبَانَا لَفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ

(Ka tuna) lokacin da (‘yan’uwan) suka ce: “Lalle Yusufu da xan’uwansa[1] babanmu ya fi son su da mu, ga mu kuwa jama’a masu yawa. Lalle babanmu yana cikin kuskure mabayyani


1- Shi ne Binyaminu, xan’uwansa ne shaqiqi.


السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 9

ٱقۡتُلُواْ يُوسُفَ أَوِ ٱطۡرَحُوهُ أَرۡضٗا يَخۡلُ لَكُمۡ وَجۡهُ أَبِيكُمۡ وَتَكُونُواْ مِنۢ بَعۡدِهِۦ قَوۡمٗا صَٰلِحِينَ

“Ku kashe Yusufu ko kuma ku jefa shi wata qasa, (yin haka) zai juyo muku fuskar babanku, sai kuma ku kasance salihai bayansa[1].”


1- Watau su tuba su nemi yafiyar Allah ().


السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 10

قَالَ قَآئِلٞ مِّنۡهُمۡ لَا تَقۡتُلُواْ يُوسُفَ وَأَلۡقُوهُ فِي غَيَٰبَتِ ٱلۡجُبِّ يَلۡتَقِطۡهُ بَعۡضُ ٱلسَّيَّارَةِ إِن كُنتُمۡ فَٰعِلِينَ

Wani mai magana daga cikinsu ya ce: “Kada ku kashe Yusufu, ku jefa shi cikin duhun kururrumar rijiya, wasu ayarin matafiya za su tsince shi, in har haka za ku yi.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 11

قَالُواْ يَـٰٓأَبَانَا مَا لَكَ لَا تَأۡمَ۬نَّا عَلَىٰ يُوسُفَ وَإِنَّا لَهُۥ لَنَٰصِحُونَ

Suka ce: “Ya babanmu, me ya sa ne ba ka amince mana game da Yusufu, alhali kuwa lalle mu ba shakka masu kula da shi ne?



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 12

أَرۡسِلۡهُ مَعَنَا غَدٗا يَرۡتَعۡ وَيَلۡعَبۡ وَإِنَّا لَهُۥ لَحَٰفِظُونَ

“Ka tura shi gobe tare da mu ya yi kiwo, ya kuma yi wasa, lalle kuma mu tabbas za Mu kiyaye shi.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 13

قَالَ إِنِّي لَيَحۡزُنُنِيٓ أَن تَذۡهَبُواْ بِهِۦ وَأَخَافُ أَن يَأۡكُلَهُ ٱلذِّئۡبُ وَأَنتُمۡ عَنۡهُ غَٰفِلُونَ

Ya ce: “Lalle tabbas tafiyarku da shi za ta baqanta mini rai, ina kuma tsoron kyarkeci ya cinye shi ba da saninku ba.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 14

قَالُواْ لَئِنۡ أَكَلَهُ ٱلذِّئۡبُ وَنَحۡنُ عُصۡبَةٌ إِنَّآ إِذٗا لَّخَٰسِرُونَ

Suka ce: “Lalle idan kyarkeci ya cinye shi ga mu kuwa muna da yawa kuma majiya qarfi to ashe lalle mun tave.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 15

فَلَمَّا ذَهَبُواْ بِهِۦ وَأَجۡمَعُوٓاْ أَن يَجۡعَلُوهُ فِي غَيَٰبَتِ ٱلۡجُبِّۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡهِ لَتُنَبِّئَنَّهُم بِأَمۡرِهِمۡ هَٰذَا وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

To lokacin da suka tafi da shi suka kuma haxu a kan su saka shi cikin duhun kururrumar rijiya. Muka kuma yi masa wahayi (da cewa): “Wallahi (wata rana) za ka ba su labarin wannan al’amari nasu alhali su ba sa jin (haka zai faru).”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 16

وَجَآءُوٓ أَبَاهُمۡ عِشَآءٗ يَبۡكُونَ

Suka kuwa dawo wa babansu da lisha suna kuka



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 17

قَالُواْ يَـٰٓأَبَانَآ إِنَّا ذَهَبۡنَا نَسۡتَبِقُ وَتَرَكۡنَا يُوسُفَ عِندَ مَتَٰعِنَا فَأَكَلَهُ ٱلذِّئۡبُۖ وَمَآ أَنتَ بِمُؤۡمِنٖ لَّنَا وَلَوۡ كُنَّا صَٰدِقِينَ

Suka ce: “Ya babanmu, mun tafi muna wasan rige muka kuma bar Yusufu wurin kayanmu, sai kyarkeci ya cinye shi. Ba kuwa za ka gaskanta mu ba ko da muna da gaskiya.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 18

وَجَآءُو عَلَىٰ قَمِيصِهِۦ بِدَمٖ كَذِبٖۚ قَالَ بَلۡ سَوَّلَتۡ لَكُمۡ أَنفُسُكُمۡ أَمۡرٗاۖ فَصَبۡرٞ جَمِيلٞۖ وَٱللَّهُ ٱلۡمُسۡتَعَانُ عَلَىٰ مَا تَصِفُونَ

Suka kuma zo da jinin qarya a rigarsa[1]. (Babansu) ya ce: “Ba haka ba ne, zuciyarku dai ta shirya muku wani abu. Saboda haka (ba ni da wani abin yi) sai haquri nagari; Allah kuma Shi ne wanda ake neman taimakonsa a kan abin da kuke sifantawa.”


1- Watau suka zo da rigar Yusufu cava-cava da jini don su tabbatar da gaskiyarsu, amma sun manta dabba ba za ta cinye mutum ba ba tare da yayyaga tufafin jikinsa ba.


السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 19

وَجَآءَتۡ سَيَّارَةٞ فَأَرۡسَلُواْ وَارِدَهُمۡ فَأَدۡلَىٰ دَلۡوَهُۥۖ قَالَ يَٰبُشۡرَىٰ هَٰذَا غُلَٰمٞۚ وَأَسَرُّوهُ بِضَٰعَةٗۚ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِمَا يَعۡمَلُونَ

Da wasu ayarin matafiya suka zo sai suka tura mai nemo musu ruwa, sai ya zura gugansa (a rijiyar); sai ya ce: “Abin farin ciki ya same ni, wannan yaro ne;” suka kuma voye shi a matsayin kayan kiri. Allah kuwa Masanin abin da suke aikatawa ne



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 20

وَشَرَوۡهُ بِثَمَنِۭ بَخۡسٖ دَرَٰهِمَ مَعۡدُودَةٖ وَكَانُواْ فِيهِ مِنَ ٱلزَّـٰهِدِينَ

Suka kuma sayar da shi araha da ‘yan dirhamai qirgaggu, suka zamanto kuma suna masu tsantsami game da shi



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 21

وَقَالَ ٱلَّذِي ٱشۡتَرَىٰهُ مِن مِّصۡرَ لِٱمۡرَأَتِهِۦٓ أَكۡرِمِي مَثۡوَىٰهُ عَسَىٰٓ أَن يَنفَعَنَآ أَوۡ نَتَّخِذَهُۥ وَلَدٗاۚ وَكَذَٰلِكَ مَكَّنَّا لِيُوسُفَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلِنُعَلِّمَهُۥ مِن تَأۡوِيلِ ٱلۡأَحَادِيثِۚ وَٱللَّهُ غَالِبٌ عَلَىٰٓ أَمۡرِهِۦ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Wanda ya saye shi kuma daga Masar[1] ya ce da matarsa: “Ki kyautata mazauninsa, muna fatan ya amfane mu, ko kuwa mu riqe shi a matsayin xa.” (Allah Ya ci gaba da cewa): Kamar haka Muka tabbatar da Yusufu a bayan qasa don kuma Mu sanar da shi fassarar mafarkai. Allah kuwa Mai rinjaye ne a bisa al’amarinsa, sai dai yawancin mutane ba sa ganewa


1- Shi ne babban minista mai kula da tattalin arziki na qasar Masar, ana masa laqabi da Azizu.


السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 22

وَلَمَّا بَلَغَ أَشُدَّهُۥٓ ءَاتَيۡنَٰهُ حُكۡمٗا وَعِلۡمٗاۚ وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lokacin kuma da qarfinsa ya kawo sai Muka ba shi hikima da ilimi. Kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 23

وَرَٰوَدَتۡهُ ٱلَّتِي هُوَ فِي بَيۡتِهَا عَن نَّفۡسِهِۦ وَغَلَّقَتِ ٱلۡأَبۡوَٰبَ وَقَالَتۡ هَيۡتَ لَكَۚ قَالَ مَعَاذَ ٱللَّهِۖ إِنَّهُۥ رَبِّيٓ أَحۡسَنَ مَثۡوَايَۖ إِنَّهُۥ لَا يُفۡلِحُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Wadda kuma yake xakinta ta yi qoqarin ya yi lalata da ita, ta kuwa kukkulle qofofi, ta kuma ce: “To ka zo mana!” Ya ce: “Allah Ya kiyashe ni! Lalle shi mai gidana ne, ya kyautata mazaunina. Lalle yadda al’amarin yake su azzalumai ba sa rabauta.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 24

وَلَقَدۡ هَمَّتۡ بِهِۦۖ وَهَمَّ بِهَا لَوۡلَآ أَن رَّءَا بُرۡهَٰنَ رَبِّهِۦۚ كَذَٰلِكَ لِنَصۡرِفَ عَنۡهُ ٱلسُّوٓءَ وَٱلۡفَحۡشَآءَۚ إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Lalle kuma ta yi niyyar ta rarumo shi, shi kuma ya yi niyyar karkata gare ta, ba don ya ga wata hujja ta Ubangijinsa ba. Kamar haka (Muka nuna masa hujjar) don Mu kawar da mummunan aiki da varna daga gare shi. Lalle shi yana daga bayinmu zavavvu



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 25

وَٱسۡتَبَقَا ٱلۡبَابَ وَقَدَّتۡ قَمِيصَهُۥ مِن دُبُرٖ وَأَلۡفَيَا سَيِّدَهَا لَدَا ٱلۡبَابِۚ قَالَتۡ مَا جَزَآءُ مَنۡ أَرَادَ بِأَهۡلِكَ سُوٓءًا إِلَّآ أَن يُسۡجَنَ أَوۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Suka kuma yiwo rige wajen qofa, sai kuwa ta yaga rigarsa daga baya, kuma suka ci karo da mijinta daf da qofar, ta ce: “Ba wani sakamakon da ya cancanta ga wanda ya yi nufin mummunan abu da iyalinka in ban da kawai a xaure shi, ko kuwa a yi masa azaba mai raxaxi.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 26

قَالَ هِيَ رَٰوَدَتۡنِي عَن نَّفۡسِيۚ وَشَهِدَ شَاهِدٞ مِّنۡ أَهۡلِهَآ إِن كَانَ قَمِيصُهُۥ قُدَّ مِن قُبُلٖ فَصَدَقَتۡ وَهُوَ مِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ

(Annabi Yusufu) ya ce: “Ita ce ta neme ni”. Wani shaida kuwa daga danginta ya shaida (cewa): “Idan an yaga rigarsa ta gaba, to ta yi gaskiya shi kuwa yana cikin masu qarya



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 27

وَإِن كَانَ قَمِيصُهُۥ قُدَّ مِن دُبُرٖ فَكَذَبَتۡ وَهُوَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Idan kuwa an yaga rigarsa ta baya, to ta yi qarya shi kuwa yana daga masu gaskiya.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 28

فَلَمَّا رَءَا قَمِيصَهُۥ قُدَّ مِن دُبُرٖ قَالَ إِنَّهُۥ مِن كَيۡدِكُنَّۖ إِنَّ كَيۡدَكُنَّ عَظِيمٞ

To yayin da (mijin nata) ya ga an yaga rigarsa ta baya ne, sai ya ce: “Lalle wannan yana daga irin makircinku; lalle makircinku kuwa yana da girma.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 29

يُوسُفُ أَعۡرِضۡ عَنۡ هَٰذَاۚ وَٱسۡتَغۡفِرِي لِذَنۢبِكِۖ إِنَّكِ كُنتِ مِنَ ٱلۡخَاطِـِٔينَ

“Kai Yusufu, ka kau da kai daga wannan (magana). Ke kuma ki nemi gafarar laifinki, lalle ke kin zamanto daga masu laifi.”



السورة: Suratu Yusuf 

الآية : 30

۞وَقَالَ نِسۡوَةٞ فِي ٱلۡمَدِينَةِ ٱمۡرَأَتُ ٱلۡعَزِيزِ تُرَٰوِدُ فَتَىٰهَا عَن نَّفۡسِهِۦۖ قَدۡ شَغَفَهَا حُبًّاۖ إِنَّا لَنَرَىٰهَا فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Waxansu mata kuma a cikin garin suka ce: “Matar Azizu tana neman yaron gidanta; tsananin son sa ya rufe mata zuciya; lalle mu dai muna ganin ta a kan kuskure mabayyani.”