السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 23

حُرِّمَتۡ عَلَيۡكُمۡ أُمَّهَٰتُكُمۡ وَبَنَاتُكُمۡ وَأَخَوَٰتُكُمۡ وَعَمَّـٰتُكُمۡ وَخَٰلَٰتُكُمۡ وَبَنَاتُ ٱلۡأَخِ وَبَنَاتُ ٱلۡأُخۡتِ وَأُمَّهَٰتُكُمُ ٱلَّـٰتِيٓ أَرۡضَعۡنَكُمۡ وَأَخَوَٰتُكُم مِّنَ ٱلرَّضَٰعَةِ وَأُمَّهَٰتُ نِسَآئِكُمۡ وَرَبَـٰٓئِبُكُمُ ٱلَّـٰتِي فِي حُجُورِكُم مِّن نِّسَآئِكُمُ ٱلَّـٰتِي دَخَلۡتُم بِهِنَّ فَإِن لَّمۡ تَكُونُواْ دَخَلۡتُم بِهِنَّ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ وَحَلَـٰٓئِلُ أَبۡنَآئِكُمُ ٱلَّذِينَ مِنۡ أَصۡلَٰبِكُمۡ وَأَن تَجۡمَعُواْ بَيۡنَ ٱلۡأُخۡتَيۡنِ إِلَّا مَا قَدۡ سَلَفَۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

An haramta muku auren iyayenku mata da ‘ya’yanku mata da ‘yan’uwanku mata da gwaggonninku da yagwalgwalanku da ‘ya’yan xan’uwa da ‘ya’yan ‘yar’uwa da iyayenku waxanda suka shayar da ku da ‘yan’uwanku mata ta wajen shayarwa, da iyayen matanku[1] da agololinku waxanda suke cikin gidajenku, waxanda matan da kuka tava saduwa da su suka haife su, in kuwa ba ku tava saduwa da su ba, to babu laifi a kanku, da matan ‘ya’yanku maza waxanda suke na tsatsonku; haramun ne kuma ku haxa ‘yan’uwa mata biyu, sai dai abin da ya wuce a baya[2]. Lalle Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai jin qai


1- Daga zarar an xaura auren mutum da mace, to uwarta ta haramta gare shi, ko ba su tare ba.


2- Haramun ne mutum ya auri ya da qanwa lokaci xaya. Hakanan haramun ne ya haxa mace da gwaggonta ko innarta lokaci xaya.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 24

۞وَٱلۡمُحۡصَنَٰتُ مِنَ ٱلنِّسَآءِ إِلَّا مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡۖ كِتَٰبَ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡۚ وَأُحِلَّ لَكُم مَّا وَرَآءَ ذَٰلِكُمۡ أَن تَبۡتَغُواْ بِأَمۡوَٰلِكُم مُّحۡصِنِينَ غَيۡرَ مُسَٰفِحِينَۚ فَمَا ٱسۡتَمۡتَعۡتُم بِهِۦ مِنۡهُنَّ فَـَٔاتُوهُنَّ أُجُورَهُنَّ فَرِيضَةٗۚ وَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ فِيمَا تَرَٰضَيۡتُم بِهِۦ مِنۢ بَعۡدِ ٱلۡفَرِيضَةِۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Haka ma da matan aure, sai dai qwaraqwaranku; wannan hukuncin Allah ke nan a kanku. Kuma an halatta muku (sauran) matan da ba waxannan ba, ku neme su da kuxinku, kuna masu kame kanku, ba ma su zina ba. To waxanda kuka sadu da su daga cikinsu ku ba su sadakinsu wanda kuka yanka musu. Kuma babu laifi a kanku game da abin da kuka yi yarjejeniya da shi bayan sadakin da kuka yanka. Lalle Allah Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 26

يُرِيدُ ٱللَّهُ لِيُبَيِّنَ لَكُمۡ وَيَهۡدِيَكُمۡ سُنَنَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكُمۡ وَيَتُوبَ عَلَيۡكُمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمٌ حَكِيمٞ

Allah Yana nufin yi muku bayani ne, kuma Ya shiryar da ku hanyoyin waxanda suka gabace ku, kuma Ya karvi tubanku. Kuma Allah Mai yawan sani ne, Mai hikima



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 27

وَٱللَّهُ يُرِيدُ أَن يَتُوبَ عَلَيۡكُمۡ وَيُرِيدُ ٱلَّذِينَ يَتَّبِعُونَ ٱلشَّهَوَٰتِ أَن تَمِيلُواْ مَيۡلًا عَظِيمٗا

Kuma Allah Yana nufin Ya karvi tubanku ne, amma waxanda suke bin sha’awace-sha’awace, su kuma suna nufin ku karkace karkacewa mai girma



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 28

يُرِيدُ ٱللَّهُ أَن يُخَفِّفَ عَنكُمۡۚ وَخُلِقَ ٱلۡإِنسَٰنُ ضَعِيفٗا

Allah Yana nufin Ya sassauta muku. Kuma an halicci xan’adam mai rauni ne



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 29

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَأۡكُلُوٓاْ أَمۡوَٰلَكُم بَيۡنَكُم بِٱلۡبَٰطِلِ إِلَّآ أَن تَكُونَ تِجَٰرَةً عَن تَرَاضٖ مِّنكُمۡۚ وَلَا تَقۡتُلُوٓاْ أَنفُسَكُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِكُمۡ رَحِيمٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku ci dukiyoyinku a tsakaninku ta hanyar rashin gaskiya, sai dai in ya kasance kasuwanci ne bisa yarjejeniya a tsakaninku. Kuma kada ku kashe kawunanku. Lalle Allah Ya kasance Mai tausaya muku ne



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 32

وَلَا تَتَمَنَّوۡاْ مَا فَضَّلَ ٱللَّهُ بِهِۦ بَعۡضَكُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖۚ لِّلرِّجَالِ نَصِيبٞ مِّمَّا ٱكۡتَسَبُواْۖ وَلِلنِّسَآءِ نَصِيبٞ مِّمَّا ٱكۡتَسَبۡنَۚ وَسۡـَٔلُواْ ٱللَّهَ مِن فَضۡلِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٗا

Kuma kada ku yi burin abin da Allah Ya fifita wasunku a kan wasu da shi, maza suna da kaso na abin da suka tsuwurwurta, haka mata ma suna da kaso na abin da suka tsuwurwurta. Kuma ku roqi Allah daga falalarsa. Lalle Allah Ya kasance Masanin komai ne



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 45

وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِأَعۡدَآئِكُمۡۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَلِيّٗا وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ نَصِيرٗا

Allah kuma Shi ne mafi sanin maqiyanku. Kuma Allah Ya isa Ya zama majivinci (gare ku), kuma Ya isa Ya zama Mai taimako (gare ku)



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 48

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَغۡفِرُ أَن يُشۡرَكَ بِهِۦ وَيَغۡفِرُ مَا دُونَ ذَٰلِكَ لِمَن يَشَآءُۚ وَمَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدِ ٱفۡتَرَىٰٓ إِثۡمًا عَظِيمًا

Lalle Allah ba Ya gafarta a yi shirka da Shi, amma Yana gafarta abin da bai kai shirka ba ga wanda Ya ga dama. Kuma duk wanda ya yi shirka da Allah, to haqiqa ya qirqiri wani gagarumin laifi



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 58

۞إِنَّ ٱللَّهَ يَأۡمُرُكُمۡ أَن تُؤَدُّواْ ٱلۡأَمَٰنَٰتِ إِلَىٰٓ أَهۡلِهَا وَإِذَا حَكَمۡتُم بَيۡنَ ٱلنَّاسِ أَن تَحۡكُمُواْ بِٱلۡعَدۡلِۚ إِنَّ ٱللَّهَ نِعِمَّا يَعِظُكُم بِهِۦٓۗ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ سَمِيعَۢا بَصِيرٗا

Lalle Allah Yana umartar ku da ku mayar da amanoni ga masu su, kuma idan za ku yi hukunci a tsakanin mutane, to ku yi hukunci da adalci. Lalle kam madalla da abin da Allah Yake muku wa’azi da shi. Lalle Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai gani



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 59

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُواْ ٱلرَّسُولَ وَأُوْلِي ٱلۡأَمۡرِ مِنكُمۡۖ فَإِن تَنَٰزَعۡتُمۡ فِي شَيۡءٖ فَرُدُّوهُ إِلَى ٱللَّهِ وَٱلرَّسُولِ إِن كُنتُمۡ تُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۚ ذَٰلِكَ خَيۡرٞ وَأَحۡسَنُ تَأۡوِيلًا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi xa’a ga Allah, kuma ku yi xa’a ga Manzo da kuma majivinta lamarinku. Idan kun yi jayayya a kan wani abu, to ku mayar da shi zuwa ga Allah da Manzonsa in kun kasance kun yi imani da Allah da ranar qarshe. Wannan shi ne mafi alheri, kuma mafi kyan makoma



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 63

أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ يَعۡلَمُ ٱللَّهُ مَا فِي قُلُوبِهِمۡ فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ وَعِظۡهُمۡ وَقُل لَّهُمۡ فِيٓ أَنفُسِهِمۡ قَوۡلَۢا بَلِيغٗا

Waxannan su ne waxanda Allah Yake sane da abin da ke cikin zukatansu, don haka ka kawar da kai daga kansu kuma ka yi musu wa’azi kuma ka faxa musu magana a karan-kawunansu magana mai shiga zukata



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 81

وَيَقُولُونَ طَاعَةٞ فَإِذَا بَرَزُواْ مِنۡ عِندِكَ بَيَّتَ طَآئِفَةٞ مِّنۡهُمۡ غَيۡرَ ٱلَّذِي تَقُولُۖ وَٱللَّهُ يَكۡتُبُ مَا يُبَيِّتُونَۖ فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ وَكَفَىٰ بِٱللَّهِ وَكِيلًا

Kuma sukan ce: “Ai ba mu da wani abu sai biyayya.” To idan suka fita daga wajenka, sai wata qungiya daga cikinsu, su riqa qulla wani abu daban cikin dare, savanin abin da suke faxa; Allah kuwa Yana rubuta duk wani abu da suke qullawa da daddare; to ka kawar da kai daga kansu, kuma ka dogara ga Allah. Allah kuwa Ya isa abin dogaro



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 83

وَإِذَا جَآءَهُمۡ أَمۡرٞ مِّنَ ٱلۡأَمۡنِ أَوِ ٱلۡخَوۡفِ أَذَاعُواْ بِهِۦۖ وَلَوۡ رَدُّوهُ إِلَى ٱلرَّسُولِ وَإِلَىٰٓ أُوْلِي ٱلۡأَمۡرِ مِنۡهُمۡ لَعَلِمَهُ ٱلَّذِينَ يَسۡتَنۢبِطُونَهُۥ مِنۡهُمۡۗ وَلَوۡلَا فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكُمۡ وَرَحۡمَتُهُۥ لَٱتَّبَعۡتُمُ ٱلشَّيۡطَٰنَ إِلَّا قَلِيلٗا

Kuma idan wani lamari ya zo musu wanda ya shafi zaman lafiya ko tsoro, sai su yaxa shi. Da a ce sun mayar da shi zuwa ga wannan Manzo da shugabanni daga cikinsu, da lalle wanxanda suke bin qwaqqwafin al’amarin sun san (dacewar a yaxa shi ko a’a). Kuma ba don falalar Allah da rahamarsa a gare ku ba, tabbas da kun bi Shaixan, in ban da ‘yan kaxan (daga cikinku)



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 87

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ لَيَجۡمَعَنَّكُمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَا رَيۡبَ فِيهِۗ وَمَنۡ أَصۡدَقُ مِنَ ٱللَّهِ حَدِيثٗا

Allah, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Lalle zai tattara ku a ranar alqiyama, wadda babu kokwanto a cikinsa. Kuma wane ne ya fi Allah gaskiyar zance?



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 93

وَمَن يَقۡتُلۡ مُؤۡمِنٗا مُّتَعَمِّدٗا فَجَزَآؤُهُۥ جَهَنَّمُ خَٰلِدٗا فِيهَا وَغَضِبَ ٱللَّهُ عَلَيۡهِ وَلَعَنَهُۥ وَأَعَدَّ لَهُۥ عَذَابًا عَظِيمٗا

Duk kuwa wanda ya kashe mumini da gangan, to sakamakonsa wutar Jahannama ce, yana mai dawwama a cikinta, kuma Allah Ya yi fushi da shi, kuma Ya la’ance shi, kuma Ya yi masa tanadin azaba mai girma



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 96

دَرَجَٰتٖ مِّنۡهُ وَمَغۡفِرَةٗ وَرَحۡمَةٗۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمًا

Wasu darajoji masu yawa daga gare Shi da gafara da kuma jin qai. Kuma Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 99

فَأُوْلَـٰٓئِكَ عَسَى ٱللَّهُ أَن يَعۡفُوَ عَنۡهُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَفُوًّا غَفُورٗا

To waxannan mai yiwuwa ne Allah Ya yi musu afuwa, Allah kuma Ya kasance Mai afuwa ne, Mai yawan gafara



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 103

فَإِذَا قَضَيۡتُمُ ٱلصَّلَوٰةَ فَٱذۡكُرُواْ ٱللَّهَ قِيَٰمٗا وَقُعُودٗا وَعَلَىٰ جُنُوبِكُمۡۚ فَإِذَا ٱطۡمَأۡنَنتُمۡ فَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَۚ إِنَّ ٱلصَّلَوٰةَ كَانَتۡ عَلَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ كِتَٰبٗا مَّوۡقُوتٗا

To idan kun kammala salla, to sai ku ambaci Allah a tsaye ko a zaune ko kuma a kwance. To idan kuka samu nutsuwa sai ku tsayar da salla (a yadda take). Lalle salla ta kasance wata farilla ce mai qayyadajjen lokaci a kan muminai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 110

وَمَن يَعۡمَلۡ سُوٓءًا أَوۡ يَظۡلِمۡ نَفۡسَهُۥ ثُمَّ يَسۡتَغۡفِرِ ٱللَّهَ يَجِدِ ٱللَّهَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma duk wanda ya aikata mummunan aiki ko ya zalunci kansa, sannan ya nemi gafarar Allah, to zai sami Allah Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 113

وَلَوۡلَا فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكَ وَرَحۡمَتُهُۥ لَهَمَّت طَّآئِفَةٞ مِّنۡهُمۡ أَن يُضِلُّوكَ وَمَا يُضِلُّونَ إِلَّآ أَنفُسَهُمۡۖ وَمَا يَضُرُّونَكَ مِن شَيۡءٖۚ وَأَنزَلَ ٱللَّهُ عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَعَلَّمَكَ مَا لَمۡ تَكُن تَعۡلَمُۚ وَكَانَ فَضۡلُ ٱللَّهِ عَلَيۡكَ عَظِيمٗا

Ba don falalar Allah da rahamarsa a kanka ba kuwa, lalle da waxansu jama’a daga cikinsu sun yi niyyar su vatar da kai, ba kuwa kowa za su iya vatarwa ba sai dai kawunansu; kuma ba za su cuce ka da komai ba. Kuma Allah Ya saukar maka da Littafi da hikima, kuma Ya sanar da kai abin da a da ba ka sani ba. Kuma falalar Allah mai girma ce gare ka



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 116

إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَغۡفِرُ أَن يُشۡرَكَ بِهِۦ وَيَغۡفِرُ مَا دُونَ ذَٰلِكَ لِمَن يَشَآءُۚ وَمَن يُشۡرِكۡ بِٱللَّهِ فَقَدۡ ضَلَّ ضَلَٰلَۢا بَعِيدًا

Lalle Allah ba Ya gafartawa a yi masa shirka, Yana kuwa gafarta abin da bai kai shirka ba ga wanda Ya ga dama. Duk wanda ya yi wa Allah shirka, to haqiqa ya vata manisanciyar vata



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 127

وَيَسۡتَفۡتُونَكَ فِي ٱلنِّسَآءِۖ قُلِ ٱللَّهُ يُفۡتِيكُمۡ فِيهِنَّ وَمَا يُتۡلَىٰ عَلَيۡكُمۡ فِي ٱلۡكِتَٰبِ فِي يَتَٰمَى ٱلنِّسَآءِ ٱلَّـٰتِي لَا تُؤۡتُونَهُنَّ مَا كُتِبَ لَهُنَّ وَتَرۡغَبُونَ أَن تَنكِحُوهُنَّ وَٱلۡمُسۡتَضۡعَفِينَ مِنَ ٱلۡوِلۡدَٰنِ وَأَن تَقُومُواْ لِلۡيَتَٰمَىٰ بِٱلۡقِسۡطِۚ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ بِهِۦ عَلِيمٗا

Kuma suna neman fatawarka game da lamarin mata. Ka ce: “Allah ne Yake ba ku fatawa game da lamarinsu da kuma abin da ake karanta muku a cikin Littafi dangane da marayu mata waxanda ba kwa iya ba su sadakinsu cikakke, ga shi kuma kuna kwaxayin ku aure su; hakanan da kuma (dukiyar) yara masu rauni. Kuma ku tsaya wajen kula da (dukiyar) marayu ta hanyar adalci. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, to lalle Allah Yana sane da shi.”



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 129

وَلَن تَسۡتَطِيعُوٓاْ أَن تَعۡدِلُواْ بَيۡنَ ٱلنِّسَآءِ وَلَوۡ حَرَصۡتُمۡۖ فَلَا تَمِيلُواْ كُلَّ ٱلۡمَيۡلِ فَتَذَرُوهَا كَٱلۡمُعَلَّقَةِۚ وَإِن تُصۡلِحُواْ وَتَتَّقُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ كَانَ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Kuma ba za ku iya yin adalci (na soyayya) a tsakankanin mata ba, ko da kuna matuqar son yin hakan. To kada ku karkata, karkata ta gaba xaya, ta yadda za ku qyale xayar kamar ratayayya[1]. Amma idan za ku kyautata kuma ku yi taqawa, to lalle Allah Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai


1- Watau su karkata ga xaya su qyale xayar a rataye, ita ba a sake ta ba ita kuma ba mai jin daxin aure ba.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 133

إِن يَشَأۡ يُذۡهِبۡكُمۡ أَيُّهَا ٱلنَّاسُ وَيَأۡتِ بِـَٔاخَرِينَۚ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلَىٰ ذَٰلِكَ قَدِيرٗا

Idan Ya ga dama sai Ya tafiyar da ku, ya ku mutane, kuma Ya kawo waxansu daban. Allah kuwa Ya kasance Mai iko ne a kan hakan



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 136

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ ءَامِنُواْ بِٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦ وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلَّذِي نَزَّلَ عَلَىٰ رَسُولِهِۦ وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ مِن قَبۡلُۚ وَمَن يَكۡفُرۡ بِٱللَّهِ وَمَلَـٰٓئِكَتِهِۦ وَكُتُبِهِۦ وَرُسُلِهِۦ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ فَقَدۡ ضَلَّ ضَلَٰلَۢا بَعِيدًا

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yi imani[1] da Allah da Manzonsa da Littafin da Ya saukar ga Manzonsa da Littafin da Ya saukar gabaninsa. Duk wanda kuwa ya kafirce wa Allah da mala’ikunsa da littattafansa da manzanninsa da ranar qarshe, to haqiqa ya vace vata mai nisa


1- Watau ku tsaya qyam a kan imaninsu da Allah da Annabinsa (), su riqe addininsu da kyau.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 139

ٱلَّذِينَ يَتَّخِذُونَ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَۚ أَيَبۡتَغُونَ عِندَهُمُ ٱلۡعِزَّةَ فَإِنَّ ٱلۡعِزَّةَ لِلَّهِ جَمِيعٗا

Su ne waxanda suke riqar kafirai a matsayin masoya, su qyale muminai. Shin suna neman wata xaukaka ce a wurinsu? To lalle xaukaka gaba xaya ta Allah ce[1]


1- Watau shi ne yake bayar da girma, kuma ga muminai kaxai yake ba da shi, don haka munafukai ba za su same shi ba.


السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 148

۞لَّا يُحِبُّ ٱللَّهُ ٱلۡجَهۡرَ بِٱلسُّوٓءِ مِنَ ٱلۡقَوۡلِ إِلَّا مَن ظُلِمَۚ وَكَانَ ٱللَّهُ سَمِيعًا عَلِيمًا

Allah ba Ya son bayyana mummunan zance, sai dai wanda aka zalunce shi. Kuma Allah Ya kasance Mai ji ne, Mai yawan sani



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 152

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦ وَلَمۡ يُفَرِّقُواْ بَيۡنَ أَحَدٖ مِّنۡهُمۡ أُوْلَـٰٓئِكَ سَوۡفَ يُؤۡتِيهِمۡ أُجُورَهُمۡۚ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Waxanda suka yi imani da Allah da manzanninsa, kuma ba su nuna bambanci tsakanin xaya daga cikinsu ba, waxannan (Allah) zai ba su ladansu. Allah kuma Ya kasance Mai yawan gafara ne, Mai yawan rahama



السورة: Suratun Nisa’i

الآية : 162

لَّـٰكِنِ ٱلرَّـٰسِخُونَ فِي ٱلۡعِلۡمِ مِنۡهُمۡ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ يُؤۡمِنُونَ بِمَآ أُنزِلَ إِلَيۡكَ وَمَآ أُنزِلَ مِن قَبۡلِكَۚ وَٱلۡمُقِيمِينَ ٱلصَّلَوٰةَۚ وَٱلۡمُؤۡتُونَ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ أُوْلَـٰٓئِكَ سَنُؤۡتِيهِمۡ أَجۡرًا عَظِيمًا

Amma masu zurfin ilimi daga cikinsu da muminai, suna imani da abin da aka saukar maka da abin da aka saukar gabaninka; musamman ma masu tsayar da salla, da kuma masu bayar da zakka, kuma masu imani da Allah da ranar qarshe. Waxannan ba da jimawa ba za Mu ba su lada mai girma