إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ
Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi
إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ
Sai abin da Allah Ya ga dama, Lalle Shi Yana sane da bayyanannen (abu) da kuma abin da yake vuya
وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ
Amma kuma game da ni’imar Ubangijinka sai ka ba da labari
أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ
Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?
وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ
Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya
فَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ وَٱسۡتَغۡفِرۡهُۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابَۢا
To ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka, ka kuma nemi gafararsa. Lalle Shi Ya kasance Mai karvar tuba ne
قُلۡ هُوَ ٱللَّهُ أَحَدٌ
Ka ce: “Shi Allah Xaya ne[1]
1- Watau a Zatinsa da siffofinsa da ayyukansa, kuma shi kaxai ya cancanci a bauta masa.
ٱللَّهُ ٱلصَّمَدُ
“Allah Abin nufa da buqatu[1]
1- Watau wanda shugabanci ya tuqe zuwa gare shi, domin ya tattara dukkan siffofin kamala da xaukaka.
لَمۡ يَلِدۡ وَلَمۡ يُولَدۡ
“Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba
وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ كُفُوًا أَحَدُۢ
“Kuma babu wani da ya kasance kini a gare Shi[1].”
1- Domin babu mai kama da shi a sunayensa da siffofinsa da ayyukansa.
مَلِكِ ٱلنَّاسِ
“Sarkin mutane