السورة: Suratul A’araf

الآية : 54

إِنَّ رَبَّكُمُ ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ يُغۡشِي ٱلَّيۡلَ ٱلنَّهَارَ يَطۡلُبُهُۥ حَثِيثٗا وَٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَ وَٱلنُّجُومَ مُسَخَّرَٰتِۭ بِأَمۡرِهِۦٓۗ أَلَا لَهُ ٱلۡخَلۡقُ وَٱلۡأَمۡرُۗ تَبَارَكَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Lalle Ubangijinku shi ne Allah wanda Ya halicci sammai da qasa cikin kwanaki shida, sannan sai Ya daidaita a kan Al’arshi[1], Yana lulluve (duhun) dare da (hasken) yini, (kowannensu) yana neman sa (xan’uwansa) a gurguje, da rana da wata da taurari kuma abubuwan horewa ne da umarninsa. Haqiqa halitta da umarni nasa ne. Albarkatun Allah Ubangijin talikai sun yawaita


1- Allah mai girma da buwaya ya daidaita a kan Al’arshi daidaiton da ya dace da girmansa.


السورة: Suratu Hud

الآية : 7

وَهُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ وَكَانَ عَرۡشُهُۥ عَلَى ٱلۡمَآءِ لِيَبۡلُوَكُمۡ أَيُّكُمۡ أَحۡسَنُ عَمَلٗاۗ وَلَئِن قُلۡتَ إِنَّكُم مَّبۡعُوثُونَ مِنۢ بَعۡدِ ٱلۡمَوۡتِ لَيَقُولَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٞ

Shi ne kuma wanda Ya halicci sammai da qasa cikin kwana shida, Al’arshinsa kuwa ya kasance a kan ruwa, don Ya jarraba ku a cikinku wa ya fi kyakkyawan aiki. Kuma tabbas idan ka ce (da su): “Lalle za a tashe ku bayan mutuwa,” tabbas kafirai za su ce: “Ai wannan ba wani abu ba ne sai tsafi mabayyani.”



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 44

خَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Allah Ya halicci sammai da qasa da gaskiya. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga muminai



السورة: Suratuz Zumar

الآية : 5

خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۖ يُكَوِّرُ ٱلَّيۡلَ عَلَى ٱلنَّهَارِ وَيُكَوِّرُ ٱلنَّهَارَ عَلَى ٱلَّيۡلِۖ وَسَخَّرَ ٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَۖ كُلّٞ يَجۡرِي لِأَجَلٖ مُّسَمًّىۗ أَلَا هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفَّـٰرُ

Ya halicci sammai da qasa da gaskiya; Yana naxa dare a kan yini, Ya kuma naxa yini a kan dare; kuma Ya hore rana da wata; kowane yana tafiya zuwa wani lokaci qayyadajje. Ku saurara! Shi ne Mabuwayi, Mai yawan gafara



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 57

لَخَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ أَكۡبَرُ مِنۡ خَلۡقِ ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Tabbas halittar sammai da qasa ta fi girma a kan halittar mutane, sai dai kuma yawancin mutane ba sa sanin (haka)



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 9

۞قُلۡ أَئِنَّكُمۡ لَتَكۡفُرُونَ بِٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡأَرۡضَ فِي يَوۡمَيۡنِ وَتَجۡعَلُونَ لَهُۥٓ أَندَادٗاۚ ذَٰلِكَ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka ce: “Yanzu kwa riqa kafircewa da wanda Ya halicci qasa a cikin (gwargwadon) kwana biyu, kuna kuma sanya masa kishiyoyi? Wannan fa Shi ne Ubangijin talikai!



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 10

وَجَعَلَ فِيهَا رَوَٰسِيَ مِن فَوۡقِهَا وَبَٰرَكَ فِيهَا وَقَدَّرَ فِيهَآ أَقۡوَٰتَهَا فِيٓ أَرۡبَعَةِ أَيَّامٖ سَوَآءٗ لِّلسَّآئِلِينَ

“Ya kuma sanya kafaffun duwatsu a cikinta daga samanta, Ya kuma yi albarka a cikinta, Ya kuma qaddara dangogin abincinta a cikin kwana huxu (tare da kwanaki biyu na halittar qasa) daidai da daidai ga masu tambaya



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 11

ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰٓ إِلَى ٱلسَّمَآءِ وَهِيَ دُخَانٞ فَقَالَ لَهَا وَلِلۡأَرۡضِ ٱئۡتِيَا طَوۡعًا أَوۡ كَرۡهٗا قَالَتَآ أَتَيۡنَا طَآئِعِينَ

“Sannan Ya nufi zuwa sama, (a sannan) ita kuma hayaqi ce, sai Ya ce da ita da kuma qasa: “Ku zo cikin biyayya ko kuma bisa tilas.” Suka ce: ‘Mun zo muna masu biyayya’



السورة: Suratux Xalaq

الآية : 12

ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ وَمِنَ ٱلۡأَرۡضِ مِثۡلَهُنَّۖ يَتَنَزَّلُ ٱلۡأَمۡرُ بَيۡنَهُنَّ لِتَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ وَأَنَّ ٱللَّهَ قَدۡ أَحَاطَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عِلۡمَۢا

Allah ne Wanda Ya halicci sammai bakwai, qasa ma Ya halicci kwatankwacinsu (watau sammai), umarni yana sauka a tsakaninsu, don ku san cewa, Allah Mai iko ne a kan komai, kuma haqiqa Allah iliminsa ya kewaye kowane abu



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 31

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا

Ya fitar da ruwanta da makiyayarta daga gare ta



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 32

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا

Duwatsu kuma Ya kafa su



السورة: Suratun Nazi’at

الآية : 33

مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku