السورة: Suratul Hajji

الآية : 21

وَلَهُم مَّقَٰمِعُ مِنۡ حَدِيدٖ

Suna kuma (shan duka) da gudumomi na baqin qarfe



السورة: Suratul Hajji

الآية : 22

كُلَّمَآ أَرَادُوٓاْ أَن يَخۡرُجُواْ مِنۡهَا مِنۡ غَمٍّ أُعِيدُواْ فِيهَا وَذُوقُواْ عَذَابَ ٱلۡحَرِيقِ

Duk sanda suka yi nufin fita daga cikinta (wutar) saboda baqin ciki sai a sake mayar da su cikinta, (a ce da su): “Ku xanxani azabar gobara.”



السورة: Suratul Hajji

الآية : 72

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلۡمُنكَرَۖ يَكَادُونَ يَسۡطُونَ بِٱلَّذِينَ يَتۡلُونَ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِنَاۗ قُلۡ أَفَأُنَبِّئُكُم بِشَرّٖ مِّن ذَٰلِكُمُۚ ٱلنَّارُ وَعَدَهَا ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu bayyanannu, to za ka ga alamar musantawa a fuskokin waxanda suka kafirta, suna kamar za su auka wa waxanda suke karanta musu ayoyinmu. To ka ce: “Shin ba na ba ku labarin abin da ya fi wannan muni ba[1]? Wuta ce da Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka kafirta; makoma kuwa ta munana.”


1- Watau fiye da abin da suke ganin muninsa idan ana karanta musu shi, watau ayoyin Alqur’ani.


السورة: Suratun Nur

الآية : 57

لَا تَحۡسَبَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مُعۡجِزِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ وَمَأۡوَىٰهُمُ ٱلنَّارُۖ وَلَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Kada kuma ka tsammaci waxanda suka kafirta za su gagara a bayan qasa, kuma makomarsu wuta ce; makoma kuwa ta munana



السورة: Suratul Ankabut

الآية : 23

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَلِقَآئِهِۦٓ أُوْلَـٰٓئِكَ يَئِسُواْ مِن رَّحۡمَتِي وَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Waxanda kuma suka kafirce wa ayoyin Allah da kuma gamuwa da Shi, waxannan sun xebe qauna daga rahamata, kuma waxannan suna da azaba mai raxaxi



السورة: Suratu Faxir

الآية : 36

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَهُمۡ نَارُ جَهَنَّمَ لَا يُقۡضَىٰ عَلَيۡهِمۡ فَيَمُوتُواْ وَلَا يُخَفَّفُ عَنۡهُم مِّنۡ عَذَابِهَاۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي كُلَّ كَفُورٖ

Waxanda kuwa suka kafirta suna da (sakamakon) wutar Jahannama, ba za a karvi rayukansu ba balle su mutu, ba kuma za a sauqaqa musu wani abu daga azabarta ba. Kamar haka Muke saka wa kowanne kafiri



السورة: Suratu Faxir

الآية : 39

هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَكُمۡ خَلَـٰٓئِفَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ فَمَن كَفَرَ فَعَلَيۡهِ كُفۡرُهُۥۖ وَلَا يَزِيدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ كُفۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ إِلَّا مَقۡتٗاۖ وَلَا يَزِيدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ كُفۡرُهُمۡ إِلَّا خَسَارٗا

Shi ne wanda Ya sanya ku halifofi a bayan qasa. Saboda haka wanda ya kafirta sakamakon kafircinsa yana kansa, kuma kafircin kafirai ba zai qara musu komai ba a wurin Ubangijinsu sai qiyayya; kuma kafircin kafirai ba zai qara musu komai ba sai hasara



السورة: Suratuz Zumar

الآية : 71

وَسِيقَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِلَىٰ جَهَنَّمَ زُمَرًاۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءُوهَا فُتِحَتۡ أَبۡوَٰبُهَا وَقَالَ لَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ رُسُلٞ مِّنكُمۡ يَتۡلُونَ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتِ رَبِّكُمۡ وَيُنذِرُونَكُمۡ لِقَآءَ يَوۡمِكُمۡ هَٰذَاۚ قَالُواْ بَلَىٰ وَلَٰكِنۡ حَقَّتۡ كَلِمَةُ ٱلۡعَذَابِ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Aka kuma ingiza qeyar waxanda suka kafirta zuwa (wutar) Jahannama qungiya-qungiya; har yayin da suka zo wurinta sai aka buxe qofofinta, masu tsaronta suka ce (da su): “Yanzu manzanni daga cikinku ba su zo muku ba ne suna karanta muku ayoyin Ubangijinku, suna kuma gargaxin ku game da haxuwa da wannan ranar taku?” Sai suka ce: “Haka ne, (sun zo mana),” sai dai kuma kalmar azaba ta tabbata a kan kafirai.”



السورة: Suratuz Zumar

الآية : 72

قِيلَ ٱدۡخُلُوٓاْ أَبۡوَٰبَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَاۖ فَبِئۡسَ مَثۡوَى ٱلۡمُتَكَبِّرِينَ

Aka ce: “Ku shiga qofofin Jahannama, kuna masu dawwama a cikinta;” to makomar masu girman kai ta munana



السورة: Suratu Ghafir

الآية : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُنَادَوۡنَ لَمَقۡتُ ٱللَّهِ أَكۡبَرُ مِن مَّقۡتِكُمۡ أَنفُسَكُمۡ إِذۡ تُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلۡإِيمَٰنِ فَتَكۡفُرُونَ

Lalle waxanda suka kafirta ana kiran su cewa: “Tabbas fushin Allah da ku ya fi girman fushinku ga kawunanku, lokacin da ake kiran ku zuwa imani (a duniya) sai kuke kafircewa.”



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 27

فَلَنُذِيقَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ عَذَابٗا شَدِيدٗا وَلَنَجۡزِيَنَّهُمۡ أَسۡوَأَ ٱلَّذِي كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

To tabbas za Mu xanxana wa waxanda suka kafirta azaba mai tsanani, kuma tabbas za mu saka musu da mafi munin abin da suka kasance suna aikatawa



السورة: Suratu Fussilat

الآية : 28

ذَٰلِكَ جَزَآءُ أَعۡدَآءِ ٱللَّهِ ٱلنَّارُۖ لَهُمۡ فِيهَا دَارُ ٱلۡخُلۡدِ جَزَآءَۢ بِمَا كَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَجۡحَدُونَ

Wannan fa shi ne sakamakon maqiya Allah (watau) wuta; suna da gidan dawwama a cikinta; sakamako ne saboda abin da suka kasance suna musuntawa na ayoyinmu



السورة: Suratus Shura

الآية : 26

وَيَسۡتَجِيبُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَيَزِيدُهُم مِّن فَضۡلِهِۦۚ وَٱلۡكَٰفِرُونَ لَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدٞ

Kuma Yana amsa wa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, Yana kuma qara musu daga falalarsa. Kafirai kuwa suna da azaba mai tsanani



السورة: Suratu Muhammad

الآية : 34

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَصَدُّواْ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ ثُمَّ مَاتُواْ وَهُمۡ كُفَّارٞ فَلَن يَغۡفِرَ ٱللَّهُ لَهُمۡ

Lalle waxanda suka kafirta suka kuma toshe hanyar Allah, sannan suka mutu a halin suna kafirai, to Allah ba zai tava gafarta musu ba



السورة: Suratul Mujadila

الآية : 5

إِنَّ ٱلَّذِينَ يُحَآدُّونَ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥ كُبِتُواْ كَمَا كُبِتَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ وَقَدۡ أَنزَلۡنَآ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖۚ وَلِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابٞ مُّهِينٞ

Lalle waxanda suke sava wa Allah da Manzonsa an qasqantar da su kamar yadda aka qasqantar da waxanda suke gabaninsu. Kuma haqiqa Mun saukar da ayoyi bayyanannu. Kafirai kuma suna da azaba mai wulaqantarwa



السورة: Suratul Mulk

الآية : 6

وَلِلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Waxanda kuma suka kafirce wa Ubangijinsu suna da azabar Jahannama; makoma kuwa ta munana